< Luka 1 >

1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
Efterdi mange have taget sig for at forfatte en Beretning om de Ting, som ere fuldbyrdede iblandt os,
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
således som de, der fra Begyndelsen bleve Øjenvidner og Ordets Tjenere, have overleveret os:
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
så har også jeg besluttet, efter nøje at have gennemgået alt forfra, at nedskrive det for dig i Orden, mægtigste Theofilus!
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
for at du kan erkende Pålideligheden af de Ting, hvorom du er bleven mundtligt undervist.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
I de Dage, da Herodes var Konge i Judæa, var der en Præst af Abias Skifte, ved Navn Sakarias; og han havde en Hustru af Arons Døtre, og hendes Navn var Elisabeth.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
Men de vare begge retfærdige for Gud og vandrede udadlelige i alle Herrens Bud og Forskrifter.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
Og de havde intet Barn, efterdi Elisabeth var ufrugtbar, og de vare begge fremrykkede i Alder.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
Men det skete, medens han efter sit Skiftes Orden gjorde Præstetjeneste for Gud,
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
tilfaldt det ham efter Præstetjenestens Sædvane at gå ind i Herrens Tempel og bringe Røgelseofferet.
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
Og hele Folkets Mængde holdt Bøn udenfor i Røgelseofferets Time.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
Men en Herrens Engel viste sig for ham, stående ved den højre Side af Røgelsesalteret.
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
Og da Sakarias så ham, forfærdedes han, og Frygt faldt over ham.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
Men Engelen sagde til ham: "Frygt ikke, Sakarias! thi din Bøn er hørt, og din Hustru Elisabeth skal føde dig en Søn, og du skal kalde hans Navn Johannes.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
Og han skal blive dig til Glæde og Fryd, og mange skulle glædes over hans Fødsel;
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
thi han skal være stor for Herren. Og Vin og stærk Drik skal han ej drikke, og han skal fyldes med den Helligånd alt fra Moders Liv,
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
og mange af Israels Børn skal han omvende til Herren deres Gud.
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
Og han skal gå foran for ham i Elias's Ånd og Kraft for at vende Fædres Hjerter til Børn og genstridige til retfærdiges Sind for at berede Herren et velskikket folk."
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
Og Sakarias sagde til Engelen: "Hvorpå skal jeg kende dette? thi jeg er gammel, og min Hustru er fremrykket i Alder."
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
Og Engelen svarede og sagde til ham: "Jeg er Gabriel, som står for Guds Åsyn, og jeg er udsendt for at tale til dig og for at forkynde dig dette Glædesbudskab.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
Og se, du skal blive stum og ikke kunne tale indtil den Dag, da dette sker, fordi du ikke troede mine Ord, som dog skulle fuldbyrdes i deres Tid,"
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
Og folket biede efter Sakarias, og de undrede sig over, at han tøvede i Templet.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
Og da han kom ud, kunde han ikke tale til dem, og de forstode, at han havde set et Syn i Templet; og han gjorde Tegn til dem og forblev stum.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
Og det skete, da hans Tjenestes Dage vare fuldendte, gik han hjem til sit Hus.
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
Men efter disse Dage blev hans Hustru Elisabeth frugtsommelig, og hun skjulte sig fem Måneder og sagde:
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
"Således har Herren gjort imod mig i de Dage, da han så til mig for at borttage min Skam iblandt Mennesker:"
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
Men i den sjette Måned blev Engelen Gabriel sendt fra Gud til en By i Galilæa, som hedder Nazareth,
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
til en Jomfru, som var trolovet med en Mand ved Navn Josef, af Davids Hus; og Jomfruens Navn var Maria.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
Og Engelen kom ind til hende og sagde: "Hil være dig, du benådede, Herren er med dig, du velsignede iblandt Kvinder!"
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
Men hun blev forfærdet over den Tale, og hun tænkte, hvad dette skulde være for en Hilsen.
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
Og Engelen sagde til hende: "Frygt ikke, Maria! thi du har fundet Nåde hos Gud.
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
Og se, du skal undfange og føde en Søn, og du skal kalde hans Navn Jesus.
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
Han skal være stor og kaldes den Højestes Søn; og Gud Herren skal give ham Davids, hans Faders Trone.
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
Og han skal være Konge over Jakobs Hus evindelig, og der skal ikke være Ende på hans Kongedømme." (aiōn g165)
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
Men Maria sagde til Engelen: "Hvorledes skal dette gå til, efterdi jeg ikke ved af nogen Mand?"
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
Og Engelen svarede og sagde til hende: Den Helligånd skal komme over dig, og den Højestes Kraft skal overskygge dig; derfor skal også det hellige, som fødes, kaldes Guds Søn.
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
Og se, Elisabeth din Frænke, også hun har undfanget en Søn i sin Alderdom, og denne Måned er den sjette for hende, som kaldes ufrugtbar.
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
Thi intet vil være umuligt for Gud."
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
Men Maria sagde: "Se, jeg er Herrens Tjenerinde; mig ske efter dit Ord!" Og Engelen skiltes fra hende.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
Men Maria stod op i de samme Dage og drog skyndsomt til Bjergegnen til en By i Juda.
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
Og hun kom ind i Sakarias's Hus og hilste Elisabeth.
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
Og det skete, da Elisabeth hørte Marias Hilsen, sprang Fosteret i hendes Liv. Og Elisabeth blev fyldt med den Helligånd
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
og råbte med høj Røst og sagde: "Velsignet er du iblandt Kvinder! og velsignet er dit Livs Frugt!
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
Og hvorledes times dette mig, at min Herres Moder kommer til mig?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
Thi se, da din Hilsens Røst nåede mine Øren, sprang Fosteret i mit Liv med Fryd.
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
Og salig er hun, som troede; thi det skal fuldkommes, hvad der er sagt hende af Herren,"
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
Og Maria sagde: "Min Sjæl ophøjer Herren;
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
og min Ånd fryder sig over Gud, min Frelser;
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
thi han har set til sin Tjenerindes Ringhed. Thi se, nu herefter skulle alle Slægter prise mig salig,
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
fordi den mægtige har gjort store Ting imod mig. Og hans Navn er helligt;
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
og hans Barmhjertighed varer fra Slægt til Slægt over dem, som frygte ham.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
Han har øvet Vælde med sin Arm; han har adspredt dem, som ere hovmodige i deres Hjertes Tanke.
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
Han har nedstødt mægtige fra Troner og ophøjet ringe.
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
Hungrige har han mættet med gode Gaver, og rige har han sendt tomhændede bort.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
Han har taget sig af sin Tjener Israel for at ihukomme Barmhjertighed
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
imod Abraham og hans Sæd til evig Tid, således som han talte til vore Fædre." (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
Og Maria blev hos hende omtrent tre Måneder, og hun drog til sit Hjem igen.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
Men for Elisabeth fuldkommedes Tiden til, at hun skulde føde, og hun fødte en Søn.
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
Og hendes Naboer og Slægtninge hørte, at Herren havde gjort sin Barmhjertighed stor imod hende, og de glædede sig med hende.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
Og det skete på den ottende Dag, da kom de for at omskære Barnet; og de vilde kalde det Sakarias efter Faderens Navn.
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
Og hans Moder svarede og sagde: "Nej, han skal kaldes Johannes."
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
Og de sagde til hende: "Der er ingen i din Slægt, som kaldes med dette Navn."
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
Men de gjorde Tegn til hans Fader om, hvad han vilde, det skulde kaldes.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
Og han forlangte en Tavle og skrev disse Ord: "Johannes er hans Navn." Og de undrede sig alle.
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
Men straks oplodes hans Mund og hans Tunge, og han talte og priste Gud.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
Og der kom en Frygt over alle, som boede omkring dem, og alt dette rygtedes over hele Judæas Bjergegn.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
Og alle, som hørte det, lagde sig det på Hjerte og sagde: "Hvad mon der skal blive af dette Barn?" Thi Herrens Hånd var med ham.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
Og Sakarias, hans Fader, blev fyldt med den Helligånd, og han profeterede og sagde:
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
"Lovet være Herren, Israels Gud! thi han har besøgt og forløst sit Folk
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
og har oprejst os et Frelsens Horn" i sin Tjener Davids Hus,
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
således som han talte ved sine hellige Profeters Mund fra fordums Tid, (aiōn g165)
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
en Frelse fra vore Fjender og fra alle deres Hånd, som hade os,
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
for at gøre Barmhjertighed imod vore Fædre og ihukomme sin hellige Pagt,
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
den Ed, som han svor vor Fader Abraham, at han vilde give os,
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
at vi, friede fra vore Fjenders Hånd, skulde tjene ham uden Frygt,
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
i Hellighed og Retfærdighed for hans Åsyn, alle vore Dage.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
Men også du, Barnlille! skal kaldes den Højestes Profet; thi du skal gå foran for Herrens Åsyn for at berede hans Veje,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
for at give hans Folk Erkendelse af Frelse ved deres Synders Forladelse,
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
for vor Guds inderlige Barmhjertigheds Skyld, ved hvilken Lyset fra det høje har besøgt os
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
for at skinne for dem, som sidde i Mørke og i Dødens Skygge, for at lede vore Fødder ind på Fredens Vej,"
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
Men Barnet voksede og blev styrket i Ånden; og han var i Ørkenerne indtil den Dag, da han trådte frem for Israel.

< Luka 1 >