< Yahuda 1 >

1 Yahuza, bawan Yesu Almasihu kuma dan'uwan Yakubu, zuwa ga kirayayyu, kaunatattu a cikin Allah Uba, kebabbu domin Yesu Kristi:
IVde a seruaunt of Iesus Christ, and brother of Iames, to them which are called and sanctified of God the Father, and returned to Iesus Christ:
2 bari jinkai da salama da kauna su ribabanya a gare ku.
Mercie vnto you, and peace and loue be multiplied.
3 Kaunatattu, ina iyakar kokari in rubuta maku game da ceton mu duka, ya zama dole in gargade ku sosai game da bangaskiya wadda aka mika wa masu bi sau daya tak ba kari.
Beloued, when I gaue al diligece to write vnto you of the common saluation, it was needful for me to write vnto you to exhort you, that yee should earnestly contend for the maintenace of ye faith, which was once giuen vnto the Saintes.
4 Don wasu mutane sun sadado sun shigo da sanda a asirce wadanda an rubuta game da hukuncin su tun da dadewa-mutane marasa imani, wanda suka canza alherin Allah zuwa lalata, kuma sun karyata makadaicin Shugaba da Ubangijinmu, Yesu Almasihu.
For there are certaine men crept in, which were before of olde ordeined to this condemnation: vngodly men they are which turne the grace of our God into wantonnesse, and denie God the onely Lord, and our Lord Iesus Christ.
5 Ina so in tunashe ku-ko da shike kun rigaya kun san abin, da cewa Allah ya ceci wasu mutane daga kasar masar, amma daga baya ya hallaka wadanda basu ba da gaskiya ba.
I wil therfore put you in remebrance, forasmuch as ye once knew this, how that the Lord, after that he had deliuered the people out of Egypt, destroied them afterward which beleeued not.
6 Kuma mala'iku wadanda ba su rike matsayin ikon su ba, amma suka bar wurin zaman su na ainihi-Allah ya tsare su a sarka na har'abada a cikin bakin duhu domin babban ranar shari'a. (aïdios g126)
The Angels also which kept not their first estate, but left their owne habitation, hee hath reserued in euerlasting chaines vnder darkenesse vnto the iudgement of the great day. (aïdios g126)
7 Suna nan kamar Saduma da Gwamrata da kuma biranen da ke kewaye da su, wadanda suka ba da kansu ga fasikanci suna bin sha'awoyi wanda ba na dabi'a ba. Aka mai da su abin misalin wadanda suka sha wuta mara matuka. (aiōnios g166)
As Sodom and Gomorrhe, and the cities about them, which in like maner as they did, committed fornication, and followed strange flesh, are set foorth for an ensample, and suffer the vengeance of eternall fire. (aiōnios g166)
8 Haka kuma, wadannan masu mafarkan suna lalatar da jikinsu. Suna raina masu mulki, kuma suna fadar miyagun abubuwa a kan masu daukaka.
Likewise notwithstanding these sleepers also defile the flesh, and despise gouernment, and speake euill of them that are in authoritie.
9 Amma ko Mika'ilu babban mala'ika, a lokacin da yake jayyaya da muhawara da shaidan a kan gawar Musa, bai kuskura ya fadi wata kalmar hukunci a kansa ba. Maimakon haka ya ce, “Bari Ubangiji ya tsauta maka!''
Yet Michael the Archangell, when hee stroue against the deuill, and disputed about the body of Moses, durst not blame him with cursed speaking, but sayd, The Lord rebuke thee.
10 Amma waddannan mutane suna kawo batanci game da dukan abin da ba su gane ba. Wadannan mutane masu halin dabbobi ne, suna kwa jawo wa kansu hallaka kenan.
But these speake euill of those thinges, which they know not: and whatsoeuer things they know naturally, as beasts, which are without reason, in those things they corrupt them selues.
11 Kaiton su! Domin sun bi hanyar Kayinu, kuma sun tsunduma cikin kuskuren Bal'amu domin samun riba. Suka hallaka cikin husuma irin ta Kora.
Wo be vnto them: for they haue followed the way of Cain, and are cast away by the deceit of Balaams wages, and perish in the gainsaying of Core.
12 Wadannan hatsari ne a boye cikin bukukuwan ku na kauna. Suna shagali ba kunya ba tsoro, suna ciyar da kansu kadai. Su holokon hadari ne marar ruwa, wanda iska ke korar sa. Su itatuwa ne shirim ba yaya, mattatu ribi biyu, tumbukakku tun daga saiwa.
These are rockes in your feasts of charitie when they feast with you, without al feare, feeding themselues: cloudes they are without water, caried about of windes, corrupt trees and without fruit, twise dead, and plucked vp by ye rootes.
13 Su rakuman teku ne masu hauka, suna fahariya cikin kumfar kunyar su. Su kamar taurari ne masu tartsatsi. Wadanda aka tanada wa duhu baki kirin na har abada. (aiōn g165)
They are the raging waues of the sea, foming out their owne shame: they are wandring starres, to whome is reserued the blackenesse of darkenesse for euer. (aiōn g165)
14 Ahnuhu, mutum na bakwai daga Adamu, ya yi anabci game da su cewa, “Duba, Ubangiji zai zo da tsarkakan sa dubun dubbai.
And Enoch also the seuenth from Adam, prophecied of such, saying, Beholde, the Lord commeth with thousands of his Saints,
15 Domin ya zartar da hukunci a kan dukan kowa, ya kuma cakune dukan marasa da'a a cikin dukan ayyukan su na rashin da'a wanda suka aikata a hanyar da bata cancanta ba, da kuma kalmomi masu kaifi da masu zunubi suka fada game da shi.”
To giue iudgement against al men, and to rebuke all the vngodly among them of all their wicked deeds, which they haue vngodly committed, and of all their cruel speakings, which wicked sinners haue spoken against him.
16 Wadannan masu cecekuce ne, masu gunaguni, wadanda ke bin sha'awar su ta mugunta, masu tinkaho da fahariya, masu bambadanci domin ribar kansu.
These are murmurers, complainers, walking after their owne lustes: Whose mouthes speake proud things, hauing mens persons in admiration, because of aduantage.
17 Amma ku, kaunatattu, ku tuna da kalmomin da manzannin Yesu Almasihunmu suka gaya maku tun da.
But, yee beloued, remember the wordes which were spoken before of the Apostles of our Lord Iesus Christ,
18 Sun ce maku, “A cikin kwanaki na karshe, za a samu masu ba'a, wadanda ke bin sha'awoyin su na rashin ibada,”
How that they told you that there should be mockers in ye last time, which should walke after their owne vngodly lustes.
19 Wadannan mutane masu haddasa tsatsaguwa ne, kuma su yan duniya ne, ba su kuma da Ruhu.
These are they that separate them selues from other, naturall, hauing not the Spirit.
20 Amma ku, kaunatattu, ku gina kanku a cikin mafificiyar bangaskiyar ku mai daraja, kuma kuna addu'a a cikin Ruhu Mai Tsarki.
But, yee beloued, edifie your selues in your most holy faith, praying in the holy Ghost,
21 Ku rike kanku a cikin kaunar Allah, kuna kuma jiran jinkan Ubangijinmu Yesu Almasihu wanda ke kawo rai na har abada. (aiōnios g166)
And keepe your selues in the loue of God, looking for the mercie of our Lord Iesus Christ, vnto eternall life. (aiōnios g166)
22 Ku nuna jinkai ga masu shakku. Ceci wadansu ta wurin fizge su daga wuta.
And haue compassion of some, in putting difference:
23 Ga wadansu kuma ku nuna jinkai da rawar jiki, kuyi kyamar koda tufafin jikinsu ma.
And other saue with feare, pulling them out of the fire, and hate euen that garment which is spotted by the flesh.
24 Yanzu, zuwa ga wanda yake da iko ya hana ku tuntube, ya kuma sa ku tsaya a gaban madaukakiyar kasancewarsa, marasa abin zargi da kuma murna mai yawa,
Nowe vnto him that is able to keepe you, that ye fall not, and to present you faultlesse before the presence of his glorie with ioy,
25 zuwa ga Allah makadaici mai ceton mu ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu, daukaka, da girma, da mulki, da iko su kasance, kamin dukan lokuta, yanzu, da har abada. Amin. (aiōn g165)
That is, to God only wise, our Sauiour, be glorie, and maiestie, and dominion, and power, both nowe and for euer, Amen. (aiōn g165)

< Yahuda 1 >