< Yahuda 1 >
1 Yahuza, bawan Yesu Almasihu kuma dan'uwan Yakubu, zuwa ga kirayayyu, kaunatattu a cikin Allah Uba, kebabbu domin Yesu Kristi:
Jude, slave of Jesus Christ, and brother of James, to the called, those who have been sanctified by God the Father and preserved through Jesus Christ:
2 bari jinkai da salama da kauna su ribabanya a gare ku.
May mercy and peace and love be multiplied to you.
3 Kaunatattu, ina iyakar kokari in rubuta maku game da ceton mu duka, ya zama dole in gargade ku sosai game da bangaskiya wadda aka mika wa masu bi sau daya tak ba kari.
Dear ones, while I was really intent on writing to you about the salvation we share, I had a compulsion to write exhorting you to contend earnestly for the Faith once for all committed to the saints.
4 Don wasu mutane sun sadado sun shigo da sanda a asirce wadanda an rubuta game da hukuncin su tun da dadewa-mutane marasa imani, wanda suka canza alherin Allah zuwa lalata, kuma sun karyata makadaicin Shugaba da Ubangijinmu, Yesu Almasihu.
Because certain men, who were marked out for this condemnation long ago, have sneaked in; they are godless, perverting the grace of our God into licentiousness and denying the only Sovereign God, even our Lord Jesus Christ.
5 Ina so in tunashe ku-ko da shike kun rigaya kun san abin, da cewa Allah ya ceci wasu mutane daga kasar masar, amma daga baya ya hallaka wadanda basu ba da gaskiya ba.
So I want to remind you, though you already know this, that the Lord delivered a people out of the land of Egypt yet later destroyed those who did not believe.
6 Kuma mala'iku wadanda ba su rike matsayin ikon su ba, amma suka bar wurin zaman su na ainihi-Allah ya tsare su a sarka na har'abada a cikin bakin duhu domin babban ranar shari'a. (aïdios )
And the angels who did not keep their proper domain but deserted their own dwelling He has kept bound in everlasting chains under darkness for the judgment of the great day. (aïdios )
7 Suna nan kamar Saduma da Gwamrata da kuma biranen da ke kewaye da su, wadanda suka ba da kansu ga fasikanci suna bin sha'awoyi wanda ba na dabi'a ba. Aka mai da su abin misalin wadanda suka sha wuta mara matuka. (aiōnios )
So also Sodom and Gomorrah and the surrounding towns—who gave themselves up to fornication and went after a different kind of flesh in a manner similar to those angels—stand as an example, undergoing a punishment of eternal fire. (aiōnios )
8 Haka kuma, wadannan masu mafarkan suna lalatar da jikinsu. Suna raina masu mulki, kuma suna fadar miyagun abubuwa a kan masu daukaka.
Likewise these dreamers in their turn both defile flesh and reject authority and slander celestial beings.
9 Amma ko Mika'ilu babban mala'ika, a lokacin da yake jayyaya da muhawara da shaidan a kan gawar Musa, bai kuskura ya fadi wata kalmar hukunci a kansa ba. Maimakon haka ya ce, “Bari Ubangiji ya tsauta maka!''
Yet even Michael the archangel, when taking issue with the devil—he was arguing about Moses' corpse—did not dare to pronounce a reviling judgment, but said, “May the Lord rebuke you!”
10 Amma waddannan mutane suna kawo batanci game da dukan abin da ba su gane ba. Wadannan mutane masu halin dabbobi ne, suna kwa jawo wa kansu hallaka kenan.
But these speak abusively against whatever they do not understand, while whatever they know by instinct, like unreasoning animals—by these things they are ruined.
11 Kaiton su! Domin sun bi hanyar Kayinu, kuma sun tsunduma cikin kuskuren Bal'amu domin samun riba. Suka hallaka cikin husuma irin ta Kora.
Woe to them, because they have taken the way of Cain, have rushed into Balaam's error for profit, and have destroyed themselves in Korah's rebellion!
12 Wadannan hatsari ne a boye cikin bukukuwan ku na kauna. Suna shagali ba kunya ba tsoro, suna ciyar da kansu kadai. Su holokon hadari ne marar ruwa, wanda iska ke korar sa. Su itatuwa ne shirim ba yaya, mattatu ribi biyu, tumbukakku tun daga saiwa.
These men are hidden reefs at your love feasts, joining the feast without fear, caring only for themselves; they are clouds without rain, carried along by winds; they are late autumn trees without fruit, twice dead (having been uprooted);
13 Su rakuman teku ne masu hauka, suna fahariya cikin kumfar kunyar su. Su kamar taurari ne masu tartsatsi. Wadanda aka tanada wa duhu baki kirin na har abada. (aiōn )
they are wild waves of the sea, foaming up their own shameful acts; they are wandering stars, for whom the black of the darkness has been reserved forever. (aiōn )
14 Ahnuhu, mutum na bakwai daga Adamu, ya yi anabci game da su cewa, “Duba, Ubangiji zai zo da tsarkakan sa dubun dubbai.
Now even Enoch, the seventh from Adam, prophesied about these men saying: “Look, the Lord is coming with ten thousands of His holy ones
15 Domin ya zartar da hukunci a kan dukan kowa, ya kuma cakune dukan marasa da'a a cikin dukan ayyukan su na rashin da'a wanda suka aikata a hanyar da bata cancanta ba, da kuma kalmomi masu kaifi da masu zunubi suka fada game da shi.”
to execute judgment on everyone and to convict all the godless among them of all their godless deeds that they have godlessly perpetrated, also of all the harsh things they have spoken against Him—the godless sinners!”
16 Wadannan masu cecekuce ne, masu gunaguni, wadanda ke bin sha'awar su ta mugunta, masu tinkaho da fahariya, masu bambadanci domin ribar kansu.
These men are grumblers and complainers, living according to their own evil desires; they talk big, flattering people to gain advantage.
17 Amma ku, kaunatattu, ku tuna da kalmomin da manzannin Yesu Almasihunmu suka gaya maku tun da.
But you, dear ones, remember the words that were spoken before by the Apostles of our Lord Jesus Christ:
18 Sun ce maku, “A cikin kwanaki na karshe, za a samu masu ba'a, wadanda ke bin sha'awoyin su na rashin ibada,”
how they told you that in the last time there will be scoffers who live according to their own godless desires.
19 Wadannan mutane masu haddasa tsatsaguwa ne, kuma su yan duniya ne, ba su kuma da Ruhu.
These are the ones who cause division; they are ‘soulish’, not having a spirit.
20 Amma ku, kaunatattu, ku gina kanku a cikin mafificiyar bangaskiyar ku mai daraja, kuma kuna addu'a a cikin Ruhu Mai Tsarki.
But you, dear ones, building yourselves up in your most holy faith, praying in the Holy Spirit,
21 Ku rike kanku a cikin kaunar Allah, kuna kuma jiran jinkan Ubangijinmu Yesu Almasihu wanda ke kawo rai na har abada. (aiōnios )
keep yourselves in God's love, looking forward to the mercy of our Lord Jesus Christ into eternal life. (aiōnios )
22 Ku nuna jinkai ga masu shakku. Ceci wadansu ta wurin fizge su daga wuta.
Now be merciful to some, making a distinction;
23 Ga wadansu kuma ku nuna jinkai da rawar jiki, kuyi kyamar koda tufafin jikinsu ma.
but others save with fear, snatching them out of the fire, hating even the garment stained by the flesh.
24 Yanzu, zuwa ga wanda yake da iko ya hana ku tuntube, ya kuma sa ku tsaya a gaban madaukakiyar kasancewarsa, marasa abin zargi da kuma murna mai yawa,
Now to Him who is able to keep them from stumbling and to present them before His glorious presence without fault and with exultation—
25 zuwa ga Allah makadaici mai ceton mu ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu, daukaka, da girma, da mulki, da iko su kasance, kamin dukan lokuta, yanzu, da har abada. Amin. (aiōn )
to God our Savior, who alone is wise, be glory and majesty, power and authority, both now and throughout all the ages! Amen. (aiōn )