< Yohanna 1 >
1 A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
Kubhwandelu kwa jhela ni Lilobhi, ni Lilobhi ajhela pamonga ni K'yara, ni lilobhi ajhele K'yara.
2 Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
E'le lilobhi, kubhwandelu ajhele pamonga ni K'yara.
3 Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
Fenu fyoha fyabhombiki kup'etela muene, ni bila muene kujhelepi khenu kimonga kya kikajhele kimalikubhombibhwa.
4 A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
Mugati mwa muene kwajhele ni bhusima, ni bhusima obhu bhwajhele nuru jha bhanadamu bhoha.
5 Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
Nuru jing'ara mu ngisi, wala ngisi jhajhisimisi lepi.
6 Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
Pajhe ni munu jha atumibhu kuh'omela kwa K'yara, ambajhe lihina lya muene akutibhweghe Yohana.
7 Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
Ahidili kama shahidi kushuhudila kuhusu nuru jhela, ili kwamba bhoha bhabhwesiajhi kuamini kup'etela muene.
8 Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
Yohana ajhelepi nuru jhela, bali ahidili kushuhudila kuhusu nuru jhela.
9 Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
Ejhu jhajhele nuru jha bhukweli ambajho jhajhele jhihida ku dunia najhu jhikampela nuru kila mmonga
10 Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
Ajhele ku dunia ni dunia jhabhombiki kup'etela muene, ni dunia jhammanyi lepi.
11 Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
Ahidili kwa fenu fya muene, nibharui bha muene bhabelikumpokela.
12 Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
Bali kwa bhala bhingi bhabhampokili, ambabho bhaliamini lihina lya muene, kwa abhu abhapelili haki jha kujha bhana bha K'yara,
13 Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
Ambabho bhahogoliki, sio kwa damu, wala kwa mapenzi gha mb'ele, wala kwa mapenzi gha munu, bali kwa K'yara muene.
14 Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
Nu muene Lilobhi abhombiki mb'ele ni kutama miongoni mwa tete, tubhubhwene bhutukufu bhwa muene, bhutukufu kama bhwamunu muene ghwa pasima ahidili kuh'omela kwa dadi, amemili neema ni kweli.
15 Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
Yohana ashuhudili kuhusu muene, na akwesili sauti ajobhili, “Ojho ndo jha najobhili habari sya muene najobhili, “Jhola jhaibetakuhida badala jha nene ndo mbaha kuliko nene, kwa ndabha ajhele kabla jha nene.”
16 Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
Kwa kujha kuh'omela mu bhutimilifu bhwa muene, tete twebhoha tupokili mebhu kipawa baada jha kipawa.
17 Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
Kwa kujha sheria jhaletibhu kup'etela Musa. Neema ni kweli fyahidili kup'etela Yesu kristu.
18 Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
Ajhelepi mwanadamu jhaambwene K'yara wakati bhuoha. Munu muene ambajhe ndo K'yara, jhaajhele pa kifua kya dadi, ambombili muene amanyikanayi.
19 Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
Na obhu ndo bhushuhuda bhwa Yohana wakati makuhani ni walawi bhabhatumibhu kwa muene ni bhayahudi kun'kota, “Bhebhe wa niani?”
20 Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
Bila kusitasita na abelilepi, bali ajibili, “Nene na Kristu lepi.”
21 Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
Hivyo bhakan'kota, “henu bhebhe ghweniani?” Bhebhe ndo Eliya? Akajobha, “Nene lepi.” Bhakajobha bhebhe wa niani wa nabii? Ajibili,” Lepi.”
22 Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
Kisha bhakan'jobhela, “Bhebhe wa niani, ili tubhapelayi lijibu bhabhatutumili”? Ukishuhudilayi wajhobhi?”
23 Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
Akajobha, “Nene na sauti jha muene jha ajhe nyikani: 'Mujhinyosiajhi njela jha Bwana,' kama nabii Isaya kyaajobhili.”
24 Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
Basi kwajhele ni bhanu bha bhatumibhu pala kuhoma kwa Mafarisayo. Bhakan'kota ni kujobha,
25 “To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
“Kwa ndabha jha kiki wibatisya basi kama bhebhe sio Kristu wala Eliya wala nabii?”
26 Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
Yohana abhajibili akajobha, “Nibatisya kwa masi. Hata efyo, miongoni mwa muenga ijhema munu jhamummanyilepi.
27 shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
Ojho ndo jha ihida baada jha nene. Nene nilondeka lepi ata kuhobhosya mighojhi jha filatu fya muene.”
28 Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
Mambo agha ghabhombiki okhu Bethania, kwiselya ku Yordani, mahali ambapo Yohana ajhele ibatisya.
29 Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
Ligono lyalafwatili Yohana ambwene Yesu ihida kwa muene akajobha, “Langayi mwanakondoo ghwa K'yara jhaibetakujhitola dhambi jha bhulimwengu!
30 Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
ojho ndo jhanijobheghe habari sya muene, nikajobhili, “Muene jhaibetakuhida kunyuma jha nene ndo mbaha kuliko nene, kwa kujha ajhele kabla jha nene.'
31 Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
Nikammanyilepi muene, lakini jhabhombiki naha ili kwamba afumulibhwayi ku Israeli, kujha nahidili kubatisya kwa masi.”
32 Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
Yohana ashuhudili, “Nabhwene Roho iselela kuh'oma kumbinguni mfuano ghwa hua, najhabakili kunani kwa muene.
33 Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
Nene nammanyilepi lakini muene jhaanitumili ili nibatisiajhi kwa masi anijobhili, 'jhola ambajhe ibetakubhona Roho iselela ni kutama panani pa muene, Ojho ndo ibetakubatisya kwa Roho Mtakatifu.'
34 Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
Nibhuene na nishuhudili kujha ojho ndo Mwana ghwa K'yara.”
35 Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
Kabhele ligono lya lafwatili Yohana ajhemili pamonga ni bhanafunzi bhamuene bhabhele,
36 suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
bhambwene Yesu igenda ni Yohana akajobha, “Langayi, Mwana kondoo ghwa K'yara!”
37 Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
Bhanafunzi bhabhele bhampeliki Yohana ijobha haya bhakan'kesya Yesu.
38 Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
Kabhele Yesu ageuki ni kubhabhona bhanafunzi bhala bhabhele bhakan'kesya, na akabhajobhela, “Mwilonda kiki?” Bhakajibu, “Rabbi, (maana jhiake 'mwalimu,' witama ndaku?”
39 Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
Akabhajobhela, “Muhidayi na mulotayi.”Kisha bhakalota ni kulola mahali pa atameghe; bhatamili pamonga naku ligono elu kwakujha jha jhele kama saa kumi ivi.
40 Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
Mmonga kati jha bhala bhabhele bhabhamp'eliki Yohana ilongela na kisha kun'kesya Yesu ajhele Andrea, ndongomunu Simoni Petro.
41 Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
Ambwene ndongomunu Simoni ni kun'jobhela, “Tun'kabhili masihi” (ambajho jhitafsiribhwa Kristu).
42 Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
Andetili kwa Yesu. Yesu akandanga ni kujobha, “Bhebhe ndo Simoni mwana ghwa Yohana” wibetakutibhwa kefa,” (maana jhiake 'Petro').
43 Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
Ligono lya lyafwatili wakati abhokili kulota Galilaya, an'kabhili Filipo ni kun'jobhela, “Nik'esiajhi nene.”
44 Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
Filipo ajhele mwenyeji wa Bethsaida, mji wa Andrea ni Petro.
45 Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
Filipo an'kabhili Nathanaeli ni kun'jobhela, Tun'kabhili jhola ambajhe Musa abhwesiti kulamba habari sya muene mun sheria sya manabii. Yesu mwana ghwa Yusufu, kuh'omela ku Nazareti.
46 Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
Nathanaeli akan'jobhela, “Je khenu kinofu kibhwesya kuh'omela Nazareti?” Filipo akan'jobhela, Hidayi na ulolayi.”
47 Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
Yesu akambona Nathanaeli ihida kwa muene ni kujobha, “Langayi, Mwisraeli kweli kweli jhaabelikujha ni udesi mugati mwa muene!”
48 Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
Nathanaeli akan'jobhela, “Unimanyibhuili nene?” Yesu akan'jibu ni kun'jobhela, “Kabla Filipo akukutilepi bho ujhele pasi pa mtini, nikakubhwene.”
49 Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
Nathanaeli akajibu, “Rabi bhebhe u Mwana ghwa K'yara! Bhebhe ndo Mfalme ghwa Israeli”!
50 Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
Yesu akan'jibu akan'jobhela, Kwa ndabha nikujobhili nikakubhwene pasi pa libehe lya mtini' je ghwiamini? wibetakulola matendo mabhaha kuliko agha.”
51 Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”
Yesu akajobha, “Muaminiajhi muaminiajhi nikabhajobhela mwibetakusibhona malaika bhikwela ni kuselela panani pa Mwana ghwa Adamu.”