< Yohanna 9 >
1 Da Yesu yana wucewa, sai ya ga wani mutum makaho tun daga haihuwa.
Og da han gik forbi, saa han et Menneske, som var blindt fra Fødselen.
2 Sai almajiransa suka tambaye shi, “Mallam, wa yayi zunubi, mutumin ne ko iyayensa, har aka haife shi makaho?”
Og hans Disciple spurgte ham og sagde: „Rabbi, hvem har syndet, denne eller hans Forældre, saa han skulde fødes blind?”
3 Yesu ya amsa, Ba mutumin ne ko iyayensa suka yi zunubi ba, amma domin aikin Allah ya bayyana a cikinsa.
Jesus svarede: „Hverken han eller hans Forældre have syndet; men det er sket, for at Guds Gerninger skulle aabenbares paa ham.
4 Dole mu yi aikin wanda ya aiko ni tunda rana. Dare na zuwa inda ba mai iya yin aiki.
Jeg maa gøre hans Gerninger, som sendte mig, saa længe det er Dag; der kommer en Nat, da ingen kan arbejde.
5 Yayinda ina duniya, ni ne hasken duniya.”
Medens jeg er i Verden, er jeg Verdens Lys.”
6 Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar.
Da han havde sagt dette, spyttede han paa Jorden og gjorde Dynd af Spyttet og smurte Dyndet paa hans Øjne.
7 Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike).” Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.
Og han sagde til ham: „Gaa hen, to dig i Dammen Siloam” (hvilket er udlagt: udsendt). Da gik han bort og toede sig, og han kom seende tilbage.
8 Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, “Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?”
Da sagde Naboerne og de, som før vare vante til at se ham som Tigger: „Er det ikke ham, som sad og tiggede?”
9 Wadansu suka ce, “shi ne.” Wadansu suka ce, “A'a, amma yana kama da shi.” Amma shi ya ce, “Ni ne wannan mutum.”
Nogle sagde: „Det er ham;” men andre sagde: „Nej, han ligner ham.” Han selv sagde: „Det er mig.”
10 Suka ce masa, “To yaya aka bude maka idanu?”
Da sagde de til ham: „Hvorledes bleve dine Øjne aabnede?”
11 Sai ya amsa, “Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani.”
Han svarede: „En Mand, som kaldes Jesus, gjorde Dynd og smurte det paa mine Øjne og sagde til mig: Gaa hen til Siloam og to dig! Da jeg saa gik hen og toede mig, blev jeg seende.”
12 Suka ce masa, “Ina yake?” Ya amsa, “Ban sani ba.”
Da sagde de til ham: „Hvor er han?” Han siger: „Det ved jeg ikke.”
13 Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa.
De føre ham, som før var blind, til Farisæerne.
14 A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu.
Men det var Sabbat den Dag, da Jesus gjorde Dyndet og aabnede hans Øjne.
15 Har yanzu farisawan suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Ya ce masu, “Ya sa mani kasa a idanuna, na wanke, kuma yanzu ina gani.”
Atter spurgte nu ogsaa Farisæerne ham, hvorledes han var bleven seende. Men han sagde til dem: „Han lagde Dynd paa mine Øjne, og jeg toede mig, og nu ser jeg.”
16 Wadansu daga cikin farisawa suka ce, “Wannan mutum ba daga Allah yake ba domin ba ya kiyaye ranar Asabar. “Wadansu suka ce, “Yaya mai zunubi zai yi irin wadannan alamu?” Sai rabuwa ta shiga tsakanin su.
Nogle af Farisæerne sagde da: „Dette Menneske er ikke fra Gud, efterdi han ikke holder Sabbaten.” Andre sagde: „Hvorledes kan et syndigt Menneske gøre saadanne Tegn?” Og der var Splid imellem dem.
17 Sai suka tambayi makahon kuma, “Me kake cewa game da shi dashike ya bude maka idanu?” Makahon ya ce, “shi annabi ne.”
De sige da atter til den blinde: „Hvad siger du om ham, efterdi han aabnede dine Øjne?” Men han sagde: „Han er en Profet.”
18 Har yanzu kam Yahudawan basu yarda da makantarsa ba da ganin gari da ya samu, sai da suka kirayo iyayen shi wanda ya sami ganin garin.
Saa troede Jøderne ikke om ham, at han havde været blind og var bleven seende, førend de fik kaldt paa Forældrene til ham, som havde faaet sit Syn.
19 Su ka tambayi iyayen, “Wannan shine yaronku da kuka ce an haife shi makaho? Yaya yanzu ya ke iya gani?”
Og de spurgte dem og sagde: „Er denne eders Søn, om hvem I sige, at han var født blind? Hvorledes er han da nu seende?”
20 Sai iyayen suka amsa masu, “Mun san wannan yaronmu ne kuma a makaho aka haife shi.
Hans Forældre svarede dem og sagde: „Vi vide, at denne er vor Søn, og at han var født blind.
21 Yadda ya ke gani yanzu, bamu sani ba, kuma wanda ya bude masa idanu, bamu sani ba. Ku tambaye shi, ba yaro ba ne. Zai iya magana don kansa.”
Men hvorledes han nu er bleven seende, vide vi ikke, og hvem der har aabnet hans Øjne, vide vi ikke heller; spørger ham; han er gammel nok; han maa selv tale for sig.”
22 Iyayensa sun fadi wadannan abubuwan, domin suna ji tsoron Yahudawan. Gama Yahudiyawan sun rigaya sun yarda duk wanda yace Yesu Almasihu ne, za a fitar dashi daga majami'a.
Dette sagde hans Forældre, fordi de frygtede for Jøderne; thi Jøderne vare allerede komne overens om, at dersom nogen bekendte ham som Kristus, skulde han udelukkes af Synagogen.
23 Domin wannan ne, iyayensa suka ce, “Ai shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
Derfor sagde hans Forældre: „Han er gammel nok, spørger ham selv!”
24 Suka sake kiran mutumin dake makaho karo na biyu, suka ce masa, “Ka girmama Allah. Mu kam mun sani wannan mutum mai zunubi ne.”
Da hidkaldte de anden Gang Manden, som havde været blind, og sagde til ham: „Giv Gud Æren; vi vide, at dette Menneske er en Synder.”
25 Sai wannan mutum ya amsa, “Ban sani ba ko shi mai zunubi ne. Abu guda daya na sani: da Ni makaho ne, amma yanzu ina gani.”
Da svarede han: „Om han er en Synder, ved jeg ikke; een Ting ved jeg, at jeg, som var blind, nu ser.”
26 Sai su ka ce masa, “Me ya yi maka? Ta yaya ya bude idanunka?”
De sagde da til ham igen: „Hvad gjorde han ved dig? Hvorledes aabnede han dine Øjne?”
27 Ya amsa, “Na rigaya na gaya maku, amma ba ku ji ba! Don me kuke so ku sake ji? Ko kuma kuna so ku zama almajiransa, haka ne?
Han svarede dem: „Jeg har allerede sagt eder det, og I hørte ikke efter. Hvorfor ville I høre det igen? Ville ogsaa I blive hans Disciple?”
28 Sai suka kwabe shi suka ce, “kai ne almajirinsa, amma mu almajiran Musa ne.
Da udskældte de ham og sagde: „Du er hans Discipel; men vi ere Mose Disciple.
29 Mun sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum, bamu san ko daga ina ne ya zo ba.”
Vi vide, at Gud har talt til Moses; men om denne vide vi ikke, hvorfra han er.”
30 Mutumin ya amsa masu ya ce, “Tirkashi, baku san inda ya fito ba, duk da haka shi ya bude mani idanu.
Manden svarede og sagde til dem: „Det er dog underligt, at I ikke vide, hvorfra han er, og han har aabnet mine Øjne.
31 Mun san da cewa Allah baya jin masu zunubi, amma idan wani mai ibada ne yana kuma yin nufinsa, to yana jin sa.
Vi vide, at Syndere bønhører Gud ikke; men dersom nogen er gudfrygtig og gør hans Villie, ham hører han.
32 Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba. (aiōn )
Aldrig er det hørt, at nogen har aabnet Øjnene paa en blindfødt. (aiōn )
33 In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba.”
Var denne ikke fra Gud, da kunde han intet gøre.”
34 Suka amsa suka ce masa, “an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?” Sai suka fitar da shi.
De svarede og sagde til ham: „Du er hel og holden født i Synder, og du vil lære os?” Og de stødte ham ud.
35 Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, “Kana bada gaskiya ga Dan Allah?”
Jesus hørte, at de havde udstødt ham; og da han traf ham, sagde han til ham: „Tror du paa Guds Søn?”
36 Sai ya amsa masa yace, “Wanene shi, Ubangiji, da zan bada gaskiya gare shi?”
Han svarede og sagde: „Hvem er han, Herre? for at jeg kan tro paa ham.”
37 Yesu yace masa, “Ai ka gan shi, shine wanda yake magana da kai.”
Jesus sagde til ham: „Baade har du set ham, og den, som taler med dig, ham er det.”
38 Mutumin ya ce, “Ubangiji, Na bada gaskiya.” Sai ya yi masa sujada.
Men han sagde: „Jeg tror, Herre!” og han kastede sig ned for ham.
39 Yesu ya ce, “Don hukunci na zo wannan duniya domin wadanda ba su gani su gani, saboda kuma wadanda suke gani su zama makafi.”
Og Jesus sagde: „Til Dom er jeg kommen til denne Verden, for at de, som ikke se, skulle blive seende, og de, som se, skulle blive blinde.”
40 Wadansu Farisawa wadanda suke tare da shi suka ji wadannan abubuwan, suka tambaye shi, “Muma makafi ne?”
Nogle af Farisæerne, som vare hos ham, hørte dette, og de sagde til ham: „Mon ogsaa vi ere blinde?”
41 Yesu ya ce masu, “Inda ku makafi ne, da ba ku da zunubi, amma yanzu kun ce, 'Muna gani', don haka zunubinku ya tabbata.
Jesus sagde til dem: „Vare I blinde, da havde I ikke Synd; men nu sige I: Vi se; eders Synd forbliver.”