< Yohanna 8 >
1 Yesu ya je Dutsen Zaitun.
But Jesus went to the mount of Olives.
2 Da sassafe ya dawo Haikali, dukan mutane kuma suka zo wurin sa; yazauna koya masu.
And in the morning he again entered the temple, and all the people came to him, and he sat down and taught them.
3 Sai marubuta da Farisawa suka kawo mace wadda aka kama ta tana zina. Su ka sa ta a tsakiya.
And the scribes and Pharisees brought to him a woman who had been detected in adultery; and they made her stand in the midst,
4 Sai su ka ce da shi, “Malam, wannan mace an kama ta tana cikin yin zina.
and said to him: Teacher, this woman was detected in adultery; in the very act.
5 A cikin shari'a, Musa ya bamu umurni mu jejjefe irin wandannan mutume, kai me ka ce game da ita?”
Now Moses, in his law, commanded us, that such should be stoned; but what say you?
6 Sun fadi haka ne domin su gwada shi su sami abinda za su zarge shi da shi, amma Yesu ya sunkuya yayi rubutu da yatsansa a kasa.
This they said to tempt him, that they might bring an accusation against him. But Jesus stooped down, and with his finger wrote on the ground.
7 Sa'adda suka cigaba da tambayar sa, ya mike tsaye yace masu, “shi wanda ba shi da zunubi a cikin ku, ya fara jifar ta da dutse.”
But as they continued to ask him, he stood up, and said to them: Let him among you who is without sin, first throw a stone at her.
8 Ya sake sunkuyawa, ya yi rubutu da yatsansa a kasa.
And again he stooped down and wrote on the ground.
9 Da suka ji haka, sai suka fita dai-dai da dai-dai, kama daga babbansu. A karshe dai aka bar Yesu shi kadai, tare da matar wadda ta ke a tsakiyar su.
But having heard him, and being convicted by their conscience, they went out, one by one, beginning from the oldest, even to the last. And Jesus was left alone, and the woman standing in the midst.
10 Yesu ya tashi tsaye ya ce da ita, “mace, ina masu zargin ki? Ba wanda ya kashe ki?
And when Jesus stood up, and saw no one but the woman, he said to her: Woman, where are those who accused you? Has no one condemned you?
11 Ta ce, “Ba kowa, Ubangiji” Yesu ya ce, “Ni ma ban kashe ki ba. Ki yi tafiyar ki, daga yanzu kada ki kara yin zunubi.”
She said: No one, sir. Jesus said to her: Neither do I condemn you; go, and sin no more.
12 Yesu ya kara yin magana da mutanen cewa, “Ni ne hasken duniya, shi wanda ya biyo ni, ba zai yi tafiya cikin duhu ba, amma za ya sami hasken rai.
Then Jesus spoke to them again, saying: I am the light of the world; he that follows me shall not walk in darkness, but shall have the light of life.
13 Farisawa suka ce masa, “Kana bada shaida a kan ka, shaidarka ba gaskiya ba ce.”
Then the Pharisees said to him: You testify concerning yourself; your testimony is not worthy of credit.
14 Yesu ya amsa ya ce masu, “Ko ma na bada shaida a kai na, shaidata gaskiya ce, na san daga inda na fito da inda zan tafi, amma ku baku san daga inda na fito ba, baku kuma san inda zan tafi ba.
Jesus answered and said to them: Though I testify concerning myself, my testimony is worthy of credit; for I know whence I came, and whither I go. But you know not whence I came, and whither I go.
15 Kuna shari'a ta son kai, ni ko ban yi wa kowa shari'a ba.
You judge according to the flesh; I judge no man.
16 Ko ma da na yi shari'a, shari'ata gaskiya ce domin ba ni kadai ba ne, amma ina tare da Uba wanda ya aiko ni.
And yet if I judge, my judgment is true, because I am not alone, but I and the Father who sent me.
17 I, a cikin dokarku an rubuta cewa shaidar mutum biyu gaskiya ce.
It is also written in your law, The testimony of two is worthy of credit.
18 Ni ne ni ke shaidar kaina, kuma Uba wanda ya aiko ni ya na shaida ta.
I am one that testify concerning myself, and the Father who sent me, testifies of me.
19 Su ka ce da shi, “Ina ubanka?” Yesu ya amsa ma su ya ce, “baku san ni ba balle Ubana, in da kun san ni da kun san Uba na kuma. “
Then they said to him: Where is your Father? Jesus answered: You know neither me, nor my Father. If you had known me, you would have known my Father also.
20 Ya fadi wadannan kalmomi a kusa da wurin ajiya sa'adda ya ke koyarwa a cikin haikali, kuma ba wanda ya kama shi saboda sa'arsa bata yi ba tukuna.
These words Jesus spoke in the treasury, as he taught in the temple; and no one laid hands on him, because his hour had not yet come.
21 Ya kara cewa da su,”Zan tafi, za ku neme ni ba za ku same ni ba, za ku mutu cikin zunubinku. Inda ni ke tafiya, ba za ku iya zuwa ba”.
Then spoke Jesus to them again; I go away, and you will seek me, and in your sin you shall die; whither I go, you can not come.
22 Yahudawa su ka ce,”Zai kashe kansa ne, da ya ce inda ni ke tafiya ba za ku iya zuwa ba?”
Then said the Jews: Will he kill himself, because he says, Whither I go, you can not come?
23 Yesu ya ce masu ku daga kasa kuke, Ni kuwa daga bisa ni ke. Ku na wannan duniya ne, Ni kuwa ba na wannan duniya ba ne.
And he said to them: You are from beneath, I am from above; you are of this world, I am not of this world.
24 Shiyasa na ce maku za ku mutu cikin zunubanku. In ba kun bada gaskiya NI NE ba, za ku mutu cikin zunubanku.
Therefore said I to you, that you shall die in your sins. For if you believe not that I am, He, you shall die in your sins.
25 Sai kuma suka ce da shi,”Wanene kai?” Yesu ya ce masu, “Abin da na gaya maku tun daga farko.
Then they said to him: Who are you? And Jesus said to them: The same that I said to you at the beginning.
26 Ina da a bubuwa da yawa da zan gaya maku, in kuma hukunta ku a kai. Duk da haka, wanda ya aiko ni, mai gaskiya ne, abubuwan da naji daga wurin sa, wadannan abubuwan su ni ke gaya wa duniya.”
I have many things to say, and to judge with respect to you; but he that sent me is true; and what things I have heard from him, these I speak to the world.
27 Ba su gane ba yana yi masu magana a kan Uban.
They knew not that he was speaking to them of the Father.
28 Yesu ya ce, “Sa'adda kuka tada Dan Mutum sama sa'annan za ku gane NI NE, kuma ban yi komi domin kaina ba. Kamar yadda Uba ya koya mani, haka nike fadin wadannan abubuwa.
Then said Jesus to them: When you have lifted up the Son of man, then you will know that I am He, and that I do nothing of myself, but as the Father has taught me I speak these things.
29 Shi wanda ya aiko ni, yana tare da ni kuma bai bar ni ni kadai ba, domin kullum ina yin abubuwan da suke faranta masa rai.”
And he that sent me is with me. The Father has not left me alone, because I always do what is pleasing to him.
30 Sa'adda Yesu ya ke fadin wadannan abubuwa, dayawa suka bada gaskiya gare shi.
While he was speaking these words, many believed on him.
31 Yesu ya gayawa wadancan Yahudawa da suka bada gaskiya gare shi, “Idan kun tsaya a cikin magana ta ku almajiraina ne na gaskiya,
Then said Jesus to those Jews that believed on him: If you continue in my word, you are my disciples indeed,
32 Kuma za ku san gaskiya, gaskiya kuwa zata 'yantar da ku.”
and you shall know the truth, and the truth shall make you free.
33 Suka amsa masa, “Mu zuriyar Ibrahim ne kuma bamu taba yin bauta wurin kowa ba, yaya za ka ce, 'Za a 'yantar da ku'?”
They answered him: We are the posterity of Abraham, and have never been in bondage to any one. How say you, You shall be made free?
34 Yesu ya ce masu, “Hakika, hakika, ina ce maku, dukan wanda ya ke aika zunubi bawan zunubi ne.
Jesus answered them: Verily, verily I say to you, whoever works sin is the servant of sin.
35 Bawa kuwa, ba ya zama a gida dindindin, da yana zama dindindin. (aiōn )
The servant continues not in the house forever; but the Son continues forever. (aiōn )
36 Saboda haka, idan Dan ya 'yantar da ku zaku zama 'yantattu sosai.
Therefore, if the Son make you free, you shall be free indeed.
37 Na san ku zuriyar Ibrahim ne, kuna so ku kashe ni saboda kalma ta bata da wurin zama a cikin ku.
I know that you are the posterity of Abraham; yet you seek to kill me, because my word has no place in you.
38 Na fadi abubuwan da na gani a wurin Ubana, ku kuma kuna yin abubuwan da kuka ji daga wurin ubanku.”
I speak what I have seen with my Father, and you do what you have seen with your father.
39 Suka amsa suka ce masa, “Ibrahim ne ubanmu” Yesu ya ce masu, “Da ku 'yayan Ibrahim ne da kun yi ayukan da Ibrahim ya yi.
They answered and said to him: Abra ham is our father. Jesus said to them: If you were the children of Abraham, you would do the works of Abraham.
40 Amma, yanzu kuna so ku kashe ni, mutumin da ya gaya maku gaskiyar da ya ji daga wurin Allah. Ibrahim bai yi haka ba.
But now you seek to kill me, a man that has spoken to you the truth, which I have heard from God; this Abraham did not.
41 Kuna yin ayyukan ubanku. Suka ce masa, “mu ba a haife mu cikin fasikanci ba, muna da Uba daya: Allah.”
You do the works of your father. They said to him: We were not born of lewdness; we have one father, God.
42 Yesu ya ce masu, “Inda Allah Ubanku ne, da kun kaunace ni, gama na zo daga wurin Allah kuma ga ni anan, gama ba domin kaina nazo ba, shine ya aiko ni.
Jesus said to them: If God were your father, you would love me; for I came forth from God and have come hither; nor, indeed, did I come of myself, but he sent me.
43 Meyasa baku gane magana ta ba? Ai saboda ba za ku iya jin maganata ba ne.
Why do you not know what I say? Because you can not understand my words.
44 Ku na ubanku, shaidan ne, kuma kuna so ku yi nufe-nufe na ubanku. Shi mai kisan kai ne tun daga farko kuma ba ya tsayawa gaskiya saboda da babu gaskiya a cikin sa. Sa'anda yake fadin karya, yana maganar halinsa ne domin shi dama makaryaci ne da uban karya kuma.
You are of your father, the devil; and the desires of your father you will do. He was a murderer from the beginning, and stood not in the truth, because there is no truth in him. When he speaks that which is false, he speaks from what is his own; for he is a liar, and the father of it.
45 Dayake ina fadin gaskiya baku bada gaskiya gare ni ba.
But because I speak the truth, you believe me not.
46 Wanene a cikin ku ya kama ni da zunubi? Idan na fadi gaskiya don me ba ku gaskanta ni ba?
Which of you convicts me of sin? If I speak the truth, why do you not believe me?
47 Shi wanda yake na Allah ya kan ji maganar Allah, ku ba kwa jin maganar Allah da yake ku ba na Allah bane,”
He that is of God, hears God’s words. For this reason you do not hear them, because you are not of God.
48 Yahudawa suka amsa suka ce masa, “Bamu fadi gaskiya ba da muka ce kai Basamariye ne kuma kana da aljan?”
The Jews answered, and said to him: Do we not well say that you are a Samaritan, and have a demon?
49 Yesu ya amsa, “Ni ba ni da aljan, ina girmama Ubana, ku kuma ba kwa girmama ni.”
Jesus answered: I have not a demon; but I honor my Father, and you dishonor me.
50 Ba na neman daraja domin kaina, akwai wanda ke nema yana kuma hukuntawa.
I seek not my own glory; there is one that seeks and judges.
51 Hakika, hakika, iIna ce maku, dukan wanda ya kiyaye maganata, ba za ya ga mutuwa ba.” (aiōn )
Verily, verily I say to you, if any one will keep my word, he shall never see death. (aiōn )
52 Sai Yahudawa su ka ce masa, Yanzu mun sani kana da aljan. Ibrahim da annabawa sun mutu, amma kai ka ce, 'dukan wanda ya yi biyayya da maganata ba zai dandana mutuwa ba'. (aiōn )
Then said the Jews to him: Now we know that you have a demon. Abraham is dead, and the prophets; and you say, If a man keep my word, he shall never taste of death. (aiōn )
53 Ai baka fi ubanmu Ibrahim girma ba wanda ya mutu, ko ka fi shi? Annabawa kuma sun mutu. Wa kake daukar kanka ne?”
Are you greater than our father Abraham, who is dead? And the prophets are dead; whom do you make yourself?
54 Yesu ya amsa, “Idan na daukaka kaina, daukaka ta banza ce, Ubana ne ya daukaka ni. Wanda kuka ce shi ne Allahnku.
Jesus answered: If I honor myself, my honor is nothing; it is my Father that honors me, of whom you say, that he is your God.
55 Ku kuwa ba ku san shi ba, amma ni na san shi. Idan na ce ban san shi ba, na zama kamar ku kenan, makaryaci. Sai dai, Ni na san shi ina kiyaye maganarsa.
And yet you have not known him. But I know him; and if I should say that I do not know him, I should be like yourselves, a liar. But I know him, and I keep his word.
56 Ubanku Ibrahim ya yi farinciki da ganin rana ta; ya gan ta kuma ya yi murna.”
Abraham, your father, rejoiced that he could see my day; and he saw it, and was glad.
57 Yahudawa su ka ce masa, “Baka kai shekara hamsin ba tukuna, ka taba ganin Ibrahim?”
Then the Jews said to him: You are not yet fifty years old, and have you seen Abraham?
58 Yesu ya ce masu, “Hakika, hakika, ina ce maku, kafin a haifi Ibrahim, NI NE.”
Jesus said to them: Verily, verily I say to you, before Abraham came into being, I was.
59 Suka dauki duwatsu za su jefe shi, amma Yesu ya boye kansa, ya fita daga haikali.
Then they took up stones to throw at him. But Jesus concealed himself, and went out of the temple, going through the midst of them; and so passed by.