< Yohanna 7 >
1 Bayan wadannan abubuwa Yesu ya zagaya cikin Gallili, saboda baya so ya shiga cikin Yahudiya domin Yahudawa suna shirin su kashe shi.
Derefter vandrede Jesus omkring i Galilæa; thi han vilde ikke vandre i Judæa, fordi Jøderne søgte at slaa ham ihjel.
2 To Idin Bukkoki na Yahudawa ya kusa.
Men Jødernes Højtid, Løvsalsfesten, var nær.
3 Sai 'yan'uwansa suka ce da shi, “ka tashi ka tafi Yahudiya, domin almajiranka su ga ayyukan da kake yi su ma.
Da sagde hans Brødre til ham: „Drag bort herfra og gaa til Judæa, for at ogsaa dine Disciple kunne se dine Gerninger, som du gør.
4 Ba wanda ya ke yin wani abu a boye idan dai yana so kowa da kowa ya san shi. Da yake ka na yin wadannan abubuwa sai ka nuna kan ka a fili ga duniya.
Thi ingen gør noget i Løndom, naar han selv ønsker at være aabenbar; dersom du gør dette, da vis dig for Verden!”
5 Domin ko 'yan'uwansa ma basu bada gaskiya gare shi ba.
Thi heller ikke hans Brødre troede paa ham.
6 Yesu ya ce dasu, “lokaci na bai yi ba tukuna, amma ku koyaushe lokacin ku ne.
Da siger Jesus til dem: „Min Tid er endnu ikke kommen; men eders Tid er stedse for Haanden.
7 Duniya baza ta iya kin ku ba, amma ta ki ni saboda ina fadin cewa ayyukanta ba su da kyau.
Verden kan ikke hade eder; men mig hader den, fordi jeg vidner om den, at dens Gerninger ere onde.
8 Ku ku je wurin idin, ni ba zan je wurin idin ba domin lokacina bai yi ba tukuna.
Drager I op til Højtiden; jeg drager endnu ikke op til denne Højtid, thi min Tid er endnu ikke fuldkommet.”
9 Bayan da ya gaya masu wadannan abubuwa, ya tsaya a cikin Gallili.
Da han havde sagt dette til dem, blev han i Galilæa.
10 Amma bayan da 'yan'uwansa su ka tafi wurin idin shi ma ya tafi, amma a asirce ba a fili ba.
Men da hans Brødre vare dragne op til Højtiden, da drog han ogsaa selv op, ikke aabenlyst, men lønligt.
11 Saboda Yahudawa suna neman sa a wurin idin, su na cewa “Ina yake?”
Da ledte Jøderne efter ham paa Højtiden og sagde: „Hvor er han?”
12 Akwai maganganu dayawa a kansa cikin taron. Wadansu suna cewa, “shi mutumin kirki ne.” Wadansu kuma suna cewa,”A'a yana karkatar da hankalin jama'a.”
Og der blev mumlet meget om ham iblandt Skarerne; nogle sagde: „Han er en god Mand;” men andre sagde: „Nej, han forfører Mængden.”
13 Amma duk da haka ba wanda ya yi magana a fili a kansa saboda suna jin tsoron Yahudawa.
Dog talte ingen frit om ham af Frygt for Jøderne.
14 Sa'anda aka kai rabin idin, sai Yesu ya shiga cikin haikali ya fara koyarwa.
Men da det allerede var midt i Højtiden, gik Jesus op i Helligdommen og lærte.
15 Yahudawa suna mamaki suna cewa,”Yaya aka yi wannan mutum ya sami ilimi dayawa haka? Shi kuwa bai je makaranta ba.”
Jøderne undrede sig nu og sagde: „Hvorledes kan denne have Lærdom, da han ikke er oplært?”
16 Yesu ya ba su amsa ya ce,”Koyarwata ba tawa ba ce, amma ta wanda ya aiko ni ce.”
Da svarede Jesus dem og sagde: „Min Lære er ikke min, men hans, som sendte mig.
17 Idan wani yana so ya yi nufinsa, za ya gane koyarwannan ko daga wurin Allah ta zo, ko ko tawa ce ta kaina.
Dersom nogen vil gøre hans Villie, skal han erkende, om Læren er fra Gud, eller jeg taler af mig selv.
18 Ko wanene yake maganar kansa, yana neman darajar kansa kenan, amma ko wanene ya nemi darajar wanda ya aiko ni, wannan mutum mai gaskiya ne, babu rashin adalci a cikin sa.
Den, som taler af sig selv, søger sin egen Ære; men den, som søger hans Ære, der sendte ham, han er sanddru, og der er ikke Uret i ham.
19 Ba Musa ya baku dokoki ba? Amma duk da haka ba mai aikata dokokin. Me yasa ku ke so ku kashe ni?
Har ikke Moses givet eder Loven? Og ingen af eder holder Loven. Hvorfor søge I at slaa mig ihjel?”
20 Taron suka ba shi amsa, “Ka na da aljani. Wanene yake so ya kashe ka?”
Mængden svarede: „Du er besat; hvem søger at slaa dig ihjel?”
21 Yesu ya amsa ya ce masu, “Nayi aiki daya, dukan ku kuna mamaki da shi.
Jesus svarede og sagde til dem: „Een Gerning gjorde jeg, og I undre eder alle derover.
22 Musa ya baku kaciya, (ba kuwa daga Musa take ba, amma daga kakannin kakanni ta ke), kuma a ranar Asabar kukan yi wa mutum kaciya.
Moses har givet eder Omskærelsen, (ikke at den er fra Moses, men fra Fædrene) og I omskære et Menneske paa en Sabbat.
23 Idan mutum ya karbi kaciya ranar Asabar, domin kada a karya dokar Musa, don me kuka ji haushi na saboda na mai da mutum lafiyayye sarai ranar Asabar?
Dersom et Menneske faar Omskærelse paa en Sabbat, for at Mose Lov ikke skal brydes, ere I da vrede paa mig, fordi jeg har gjort et helt Menneske rask paa en Sabbat?
24 Kada ku yi shari'a ta ganin ido, amma ku yi shari'a mai adalci.”
Dømmer ikke efter Skinnet, men dømmer en retfærdig Dom!”
25 Wadansun su daga Urushalima suka ce, “wannan ba shine wannan da suke nema su kashe ba?”
Da sagde nogle af dem fra Jerusalem: „Er det ikke ham, som de søge at slaa ihjel?
26 Kuma duba, yana magana a fili, sannan ba wanda ya ce da shi komai. Ba zai yiwu ba mahukunta su sani cewa wannan Kristi ne, ko ba haka ba?
Og se, han taler frit, og de sige intet til ham; mon Raadsherrerne virkelig skulde have erkendt, at han er Kristus?
27 da haka, mun san inda wannan mutum ya fito. Amma sa'anda Kristi za ya zo, ba wanda zai san inda ya fito.”
Dog — vi vide, hvorfra denne er; men naar Kristus kommer, kender ingen, hvorfra han er.”
28 Yesu yayi magana da karfi a haikali, yana koyarwa ya na cewa, “Kun san ni kuma kun san inda na fito. Ban zo domin kaina ba, amma wanda ya aiko ni mai gaskiya ne, ku kuwa baku san shi ba.
Derfor raabte Jesus, idet han lærte i Helligdommen, og sagde: „Baade kende I mig og vide, hvorfra jeg er! Og af mig selv er jeg ikke kommen, men han, som sendte mig, er sand, han, hvem I ikke kende.
29 Ni na san shi domin daga wurinsa na fito, kuma shine ya aiko ni.”
Jeg kender ham; thi jeg er fra ham, og han har udsendt mig.”
30 Suna kokari su kama shi, amma ba wanda ya iya sa masa hannu domin sa'arsa ba ta yi ba tukuna.
De søgte da at gribe ham; og ingen lagde Haand paa ham, thi hans Time var endnu ikke kommen.
31 Duk da haka wadansu dayawa a cikin taron suka bada gaskiya gare shi suka ce,”Sa'anda Kristi ya zo, zai yi alamu fiye da wadanda wannan mutum ya yi?”
Men mange af Folket troede paa ham, og de sagde: „Naar Kristus kommer, mon han da skal gøre flere Tegn, end denne har gjort?”
32 Farisawa suka ji tattarmukan suna yin rada a kan wadannan abubuwa game da Yesu, Sai manyan malamai da Farisawa su ka aika jami'ai su kama shi.
Farisæerne hørte, at Mængden mumlede dette om ham; og Ypperstepræsterne og Farisæerne sendte Tjenere ud for at gribe ham.
33 Sa'annan Yesu yace ma su,” jimawa kadan ina tare ku, sa'annan in tafi wurin wanda ya aiko ni.
Da sagde Jesus: „Endnu en liden Tid er jeg hos eder, saa gaar jeg bort til den, som sendte mig.
34 Za ku neme ni ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba.”
I skulle lede efter mig og ikke finde mig, og der, hvor jeg er, kunne I ikke komme.”
35 Yahudawa fa su ka cewa junan su, “Ina wannan mutum zai je inda ba za mu iya samun sa ba? Ko za ya tafi wurin Helinawa na warwatsuwa ya koyawa Helinawa?
Da sagde Jøderne til hverandre: „Hvor vil han gaa hen, siden vi ikke skulle finde ham? Mon han vil gaa til dem, som ere adspredte iblandt Grækerne, og lære Grækerne?
36 Wace kalma ya ke fadi haka, 'za ku neme ni amma ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba'?”
Hvad er det for et Ord, han siger: I skulle lede efter mig og ikke finde mig, og der, hvor jeg er, kunne I ikke komme?”
37 To a rana ta karshe, babbar rana ta idin, Yesu ya mike ya yi magana da karfi cewa, “Idan kowa yana jin kishi, ya zo wuri na ya sha.
Men paa den sidste, den store Højtidsdag stod Jesus og raabte og sagde: „Om nogen tørster, han komme til mig og drikke!
38 Shi wanda ya bada gaskiya gare ni kamar yadda nassi ya fadi, daga cikin sa rafukan ruwa na rai za su bulbulo.”
Den, som tror paa mig, af hans Liv skal der, som Skriften har sagt, flyde levende Vandstrømme.”
39 Amma ya fadi haka a kan Ruhu, wanda wadanda suka bada gaskiya gare shi za su karba; ba a ba da Ruhun ba tukuna, saboda ba a rigaya an daukaka Yesu ba.
Men dette sagde han om den Aand, som de, der troede paa ham, skulde faa; thi den Helligaand var der ikke endnu, fordi Jesus endnu ikke var herliggjort.
40 Wadansu a cikin taron, sa'anda suka ji wadannan kalmomi, suka ce, “Wannan lallai annabi ne.”
Nogle af Mængden, som hørte disse Ord, sagde nu: „Dette er sandelig Profeten.”
41 Wadansu suka ce, “Wannan Almasihu ne.” Amma wadansu suka ce, “Almasihu zai fito daga Gallili ne?
Andre sagde: „Dette er Kristus;” men andre sagde: „Mon da Kristus kommer fra Galilæa?
42 Ba nassi ya ce Almasihu zai fito daga cikin dangin Dauda daga Baitalami ba, daga kauyen da Dauda ya fito?”
Har ikke Skriften sagt, at Kristus kommer af Davids Sæd og fra Bethlehem, den Landsby, hvor David var?”
43 Sai aka sami rabuwa a cikin taron saboda shi.
Saaledes blev der Splid iblandt Mængden om ham.
44 Da wadansun su sun kama shi, amma ba wanda ya sa masa hannu.
Men nogle af dem vilde gribe ham; dog lagde ingen Haand paa ham.
45 Sa'annan jami'an suka dawo wurin manyan Fristoci da Farisawa, wadanda suka ce,” me yasa ba ku kawo shi ba?”
Tjenerne kom nu til Ypperstepræsterne og Farisæerne, og disse sagde til dem: „Hvorfor have I ikke ført ham herhen?”
46 Jami'an su ka amsa, “Ba mutumin da ya taba yin magana kamar haka.”
Tjenerne svarede: „Aldrig har noget Menneske talt saaledes som dette Menneske.”
47 Farisawa suka amsa masu, “kuma an karkatar da ku?
Da svarede Farisæerne dem: „Ere ogsaa I forførte?
48 Ko wani daga cikin mahukunta ya bada gaskiya gare shi, ko kuwa daga cikin Farisawa?
Mon nogen af Raadsherrerne har troet paa ham, eller nogen af Farisæerne?
49 Amma wannan taro da basu san shari'a ba, la'anannu ne.”
Men denne Hob, som ikke kender Loven, er forbandet.”
50 Nikodimus ya ce masu, (shi wanda ya zo wurin Yesu da, daya daga cikin Farisawa),
Nikodemus, han, som var kommen til ham om Natten og var en af dem, sagde til dem:
51 “Ko shari'armu bata hana hukunta mutum ba, sai ta ji daga gare shi ta kuma san abin da ya aikata ba?”
„Mon vor Lov dømmer et Menneske, uden at man først forhører ham og faar at vide, hvad han gør?”
52 Suka amsa masa suka ce,”kai ma daga Galili ka fito? Ka yi bincike ka gani ba annanbin da zai fito daga Galili.”
De svarede og sagde til ham: „Er ogsaa du fra Galilæa? Ransag og se, at der ikke fremstaar nogen Profet fra Galilæa.”
53 Daga nan sai kowa ya tafi gidansa.
[Og de gik hver til sit Hus.]