< Yohanna 6 >
1 Bayan waddannan abubuwa, Yesu ya ketare tekun Galili, wanda a ke kira tekun Tibariya.
Depois destas coisas, Jesus foi para o outro lado do mar da Galiléia, que também é chamado de Mar de Tiberíades.
2 Sai taro mai yawa suka bi shi domin suna ganin alamu da yake yi akan marasa lafiya.
Uma grande multidão o seguiu, porque viram seus sinais que ele fez sobre aqueles que estavam doentes.
3 Sai Yesu ya hau dutse ya zauna a can tare da almajiransa.
Jesus subiu à montanha, e sentou-se ali com seus discípulos.
4 (Kuma da idin Ketarewa, wato idin Yahudawa, ya kusato.)
Agora a Páscoa, a festa dos judeus, estava próxima.
5 Da Yesu ya daga kai sai ya ga babban taro yana zuwa wurinsa, sai ya ce ma Filibus, “Ina za mu sayi gurasar da Mutanen nan za su ci?”
Jesus, portanto, levantando os olhos e vendo que uma grande multidão vinha até ele, disse a Filipe: “Onde vamos comprar pão, para que estes possam comer?
6 ( Ya fadi haka ne domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi.)
Ele disse isto para testá-lo, pois ele mesmo sabia o que iria fazer.
7 Filibus ya amsa masa, “gurasar dinari biyu ma ba zata ishi kowannensu ya samu ko kadan ba.”
Philip respondeu-lhe: “Duzentos denários de pão não são suficientes para eles, para que cada um deles possa receber um pouco”.
8 Daya daga cikin almajiransa, wato Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus, ya ce masa,
Um de seus discípulos, André, irmão de Simão Pedro, disse-lhe:
9 “Ga wani dan yaro nan da dunkule biyar na sha'ir, da kifi biyu. Amma menene wadannan za su yi wa mutane masu yawa?”
“Há aqui um menino que tem cinco pães de cevada e dois peixes, mas o que são estes entre tantos”?
10 Yesu ya ce, “ku sa mutane su zauna.”( wurin kuwa akwai ciyawa.) Sai mazajen suka zauna, sun kai wajen dubu biyar.
Jesus disse: “Mande o povo se sentar”. Agora havia muita grama naquele lugar. Então os homens se sentaram, em número de cerca de cinco mil.
11 Sai Yesu ya dauki gurasar, bayan da ya yi godiya, sai ya rarraba wa wadanda suke zaune. Haka kuma ya rarraba kifin gwargwadon abin da zai ishe su.
Jesus tomou os pães, e tendo dado graças, distribuiu aos discípulos, e os discípulos aos que estavam sentados, também dos peixes, tanto quanto eles desejavam.
12 Da Mutanen suka ci suka kuma koshi, sai ya ce wa almajiransa, ku tattara gutsattsarin da suka rage, kada ya zama asara.”
Quando estavam cheios, ele disse a seus discípulos: “Recolham os pedaços que sobram, que nada se perca”.
13 Sai suka cika kwanduna goma sha biyu da gutsattsarin gurasar nan biyar da ya rage bayan da kowa ya ci.
Então eles os reuniram, e encheram doze cestas com pedaços quebrados dos cinco pães de cevada, que foram deixados por aqueles que haviam comido.
14 Da jama'a suka ga alamar da ya yi, sai suka ce, “Hakika wannan shi ne annabin nan mai zuwa cikin duniya.
Quando as pessoas viram o sinal que Jesus fez, disseram: “Este é verdadeiramente o profeta que vem ao mundo”.
15 “Da Yesu ya gane suna shirin zuwa su dauke shi da karfi da yaji su nada shi sarki, sai ya sake komawa kan dutsen da kansa.
Jesus, portanto, percebendo que eles estavam prestes a vir e levá-lo à força para fazê-lo rei, retirou-se novamente para a montanha por si mesmo.
16 Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara teku.
Quando chegou a noite, seus discípulos desceram ao mar.
17 Suka shiga cikin jirgi, suka haye teku zuwa kafarnahum. (A lokacin duhu ya yi, Yesu kuwa bai riga ya iso wurinsu ba tukuna.)
Eles entraram no barco e estavam indo sobre o mar até Cafarnaum. Agora estava escuro, e Jesus não tinha vindo até eles.
18 Iska mai karfin gaske tana kadawa, kuma tekun yana hargowa.
O mar foi atirado por um grande vento que soprava.
19 Bayan da almajiran suka yi tuki na wajen kimanin mil ashirin da biyar ko talatin, sai suka hango Yesu yana tafiya a kan teku ya kuma kusa da jirgin, sai suka firgita.
Quando eles tinham remado cerca de vinte e cinco ou trinta estádios, viram Jesus caminhando sobre o mar e se aproximando do barco; e ficaram com medo.
20 Amma ya ce masu, “Ni ne! kada ku firgita.”
Mas ele lhes disse: “Eu Sou Ele. Não tenham medo”.
21 Sa'an nan suka yarda suka karbe shi a cikin jirgin, kuma nan da nan jirgin ya kai gacci.
Eles estavam, portanto, dispostos a recebê-lo dentro do barco. Imediatamente o barco estava na terra para onde eles estavam indo.
22 Kashe gari, sauran taron da suke tsaye a dayan hayin tekun suka ga cewa babu wani jirgi a wajen sai dayan, Yesu kuma bai shiga ciki da almajiransa ba, amma almajiransa suka tafi su kadai.
No dia seguinte, a multidão que estava do outro lado do mar viu que não havia outro barco ali, exceto aquele em que seus discípulos haviam embarcado, e que Jesus não havia entrado com seus discípulos no barco, mas que seus discípulos haviam ido embora sozinhos.
23 Sai dai, akwai wadansu jirage da suka zo daga Tibariya kusa da wurin da taron suka ci gurasa bayan da Ubangiji ya yi godiya.
No entanto, barcos de Tiberíades aproximaram-se do lugar onde comeram o pão depois que o Senhor lhes deu graças.
24 Sa'anda taron suka gane cewa Yesu da almajiransa ba su wurin, su da kansu su ka shiga cikin jiragen suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
Quando a multidão viu que Jesus não estava lá, nem seus discípulos, eles mesmos entraram nos barcos e vieram para Cafarnaum, procurando Jesus.
25 Da suka same shi a hayin tekun, suka ce masa, “Mallam, yaushe ka zo nan?”
Quando o encontraram do outro lado do mar, perguntaram-lhe: “Rabino, quando você veio aqui?”.
26 Yesu ya amsa masu, da cewa, “hakika, kuna nema na ne, ba don kun ga alamu ba, amma domin kun ci gurasar nan kun koshi.
Jesus lhes respondeu: “Certamente eu lhes digo, vocês me procuram, não porque viram sinais, mas porque comeram dos pães e se encheram.
27 Ku daina yin wahala a kan neman abinci mai lalacewa, sai dai a kan abinci mai dawwama wanda zai kaiku ga rai madawwami wanda Dan Mutum zai ba ku, domin Ubangiji Allah ya sa hatiminsa a kansa.” (aiōnios )
Não trabalheis pela comida que perece, mas pela comida que resta à vida eterna, que o Filho do Homem vos dará”. Porque Deus, o Pai, o selou”. (aiōnios )
28 Sai suka ce Masa, “Me za mu yi, domin mu aikata ayyukan Allah?
Disseram-lhe portanto: “O que devemos fazer, para que possamos trabalhar as obras de Deus”?
29 Yesu ya amsa, “Wannan shi ne aikin Allah: wato ku gaskata da wanda ya aiko.”
Jesus lhes respondeu: “Esta é a obra de Deus, que vós credes naquele que Ele enviou”.
30 Sai suka ce masa, “To wace alama za ka yi, don mu gani mu gaskata ka?
Disseram-lhe então: “O que você faz então por um sinal, para que possamos ver e acreditar em você? Que trabalho você faz?
31 Me za ka yi? Kakanninmu sun ci manna a jeji, kamar yadda aka rubuta, “Ya ba su gurasa daga sama su ci.”
Nossos pais comeram o maná no deserto. Como está escrito: “Ele lhes deu pão do céu para comer”.
32 Sa'an nan Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, ina gaya maku ba Musa ne ya ba ku gurasa nan daga sama ba, amma Ubana ne ya baku gurasa ta gaskiya daga sama.
Jesus, portanto, lhes disse: “Certamente, eu lhes digo, não foi Moisés quem lhes deu o pão do céu, mas meu Pai lhes dá o verdadeiro pão do céu”.
33 Gurasar Allah itace mai saukowa daga sama mai kuma bada rai ga duniya,”
Pois o pão de Deus é o que desce do céu e dá vida ao mundo”.
34 Sai suka ce masa, “Mallam, ka rika ba mu irin wannan gurasa kodayaushe.”
Disseram-lhe portanto: “Senhor, dá-nos sempre este pão”.
35 Yesu ya ce masu, “Ni ne gurasa mai ba da rai. Wanda ya zo wurina ba zai ji yunwa ba, wanda kuma ya gaskanta da ni ba zai kara jin kishi ba.
Jesus disse a eles: “Eu sou o pão da vida”. Quem vem a mim não terá fome, e quem acredita em mim nunca terá sede”.
36 Amma na gaya maku cewa, hakika kun gan ni, duk da haka ba ku ba da gaskiya ba.
Mas eu lhes disse que vocês me viram, e ainda assim não acreditam.
37 Duk wanda Uba ya bani zai zo gare ni, wanda kuwa ya zo gare ni ba zan kore shi ba ko kadan.
Todos aqueles que o Pai me dá virão até mim. Aquele que vem a mim, eu não vou de forma alguma expulsar.
38 Gama na sauko daga sama, ba domin in bi nufin kaina ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni.
Pois eu desci do céu, não para fazer minha própria vontade, mas a vontade d'Aquele que me enviou.
39 Wannan shi ne nufin wanda ya aiko ni, kada in rasa ko daya daga cikin wadannan da ya bani, sai dai in tashe su a ranar karshe.
Esta é a vontade de meu Pai que me enviou, que de tudo o que ele me deu eu não perca nada, mas que o ressuscite no último dia.
40 Gama wannan shi ne nufin Ubana, duk wanda yake ganin Dan ya kuma gaskata da shi zai sami rai madawwami, ni kuma zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios )
Esta é a vontade daquele que me enviou, que todo aquele que vê o Filho e acredita nele tenha a vida eterna; e eu o ressuscitarei no último dia”. (aiōnios )
41 Sai Yahudawa suka yi gunaguni akansa, domin ya ce, “Nine Gurasar da ta sauko daga sama.”
Os judeus, portanto, murmuraram a seu respeito, porque ele disse: “Eu sou o pão que desceu do céu”.
42 Suka ce, “Ba wannan ne Yesu Dan Yusufu, wanda Ubansa da Uwarsa mun san su ba? Ta yaya yanzu zai ce, 'Na ya sauko daga sama'?
Eles disseram: “Não é este Jesus, o filho de José, cujo pai e mãe nós conhecemos? Como então ele diz: “Eu desci do céu”?”
43 Yesu ya amsa, ya ce masu, “Kada ku yi gunaguni a junanku.
Therefore Jesus lhes respondeu: “Não murmurem entre vocês.
44 Ba mai iya zuwa wurina sai dai in Uba wanda ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta karshe.
Ninguém pode vir a mim a menos que o Pai que me enviou o atraia; e eu o levantarei no último dia”.
45 A rubuce yake cikin litattafan anabawa cewa, 'Dukkansu Allah zai koya masu'. Duk wanda ya ji ya kuma koya daga wurin Uba, ya kan zo gare ni.
Está escrito nos profetas: “Todos eles serão ensinados por Deus”. Portanto, todo aquele que ouve do Pai e aprendeu, vem a mim.
46 Ba cewa wani ya taba ganin Uban ba, sai shi wanda yake daga wurin Allah - shine ya ga Uban.
Não que alguém tenha visto o Pai, exceto aquele que é de Deus. Ele tem visto o Pai.
47 Hakika, hakika, wanda ya bada gaskiya, yana da rai Madawwami. (aiōnios )
Certamente, eu lhes digo, aquele que acredita em mim tem a vida eterna. (aiōnios )
49 Ubanninku sun ci manna cikin jeji, suka kuma mutu.
Seus pais comeram o maná no deserto e morreram.
50 Ga gurasa da ta sauko daga sama, domin mutum ya ci daga cikinta ba kuwa zai mutu ba.
Este é o pão que desce do céu, para que qualquer um possa comer dele e não morrer.
51 Ni ne gurasa mai rai da ya sauko daga sama. Duk wanda ya ci daga gurasar, zai rayu har abada. Wannan gurasar da zan bayar jiki na ne don ceton duniya.” (aiōn )
Eu sou o pão vivo que desceu do céu. Se alguém comer deste pão, ele viverá para sempre. Sim, o pão que eu darei pela vida do mundo é a minha carne”. (aiōn )
52 Sai Yahudawa suka fusata a tsakanin junansu suka kuma fara gardama, cewa, “Yaya mutumin nan zai iya bamu naman jikinsa mu ci?
Os judeus, portanto, se defrontaram, dizendo: “Como este homem pode nos dar sua carne para comer”?
53 Sai Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, in ba ku ci naman jikin Dan mutum ba, ba ku kuma sha jininsa ba, ba za ku sami rai a cikin ku ba.
Jesus, portanto, lhes disse: “Certamente vos digo que, se não comerdes a carne do Filho do Homem e não beberdes seu sangue, não tereis vida em vós mesmos”.
54 Dukan wanda ya ci nama na ya kuma sha jinina yana da rai Madawwami, ni kuwa zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios )
Aquele que come minha carne e bebe meu sangue tem a vida eterna, e eu o ressuscitarei no último dia. (aiōnios )
55 Domin namana abinci ne na gaske, jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
Pois minha carne é comida de fato, e meu sangue é bebida de fato.
56 Duk wanda ya ci namana, ya kuma sha jinina yana zamne a ciki na, ni kuma a cikinsa.
Aquele que come minha carne e bebe meu sangue vive em mim, e eu nele.
57 Kamar yadda rayayyen Uba ya aiko ni, nake kuma rayuwa saboda Uban, haka ma wanda ya ci namana, zai rayu sabo da ni.
Como o Pai vivo me enviou, e eu vivo por causa do Pai, assim aquele que se alimenta de mim também viverá por causa de mim.
58 Wannan itace gurasar da ta sauko daga sama, ba irin wadda Ubanninku suka ci suka mutu ba. Dukan wanda ya ci gurasar zai rayu har abada.” (aiōn )
Este é o pão que desceu do céu - não como nossos pais comeram o maná e morreram. Aquele que comer este pão viverá para sempre”. (aiōn )
59 Yesu ya fadi wadan nan abubuwa a cikin majami'a sa'ad da yake koyarwa a Kafarnahum.
Ele disse estas coisas na sinagoga, como ele ensinou em Cafarnaum.
60 Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan Magana yana da karfi, wa zai iya jinta?”
Portanto, muitos de seus discípulos, quando ouviram isto, disseram: “Este é um ditado difícil! Quem pode ouvi-lo?”
61 Yesu, kuwa da yake ya sani a ransa da cewa almajiransa suna gunagunin wannan, sai ya ce masu, “Wannan ya zamar maku laifi?
Mas Jesus, sabendo em si mesmo que seus discípulos murmuravam com isso, disse-lhes: “Será que isso vos faz tropeçar?
62 Yaya Ke nan in kun ga Dan Mutum yana hawa inda yake a da?
Então e se vocês vissem o Filho do Homem ascendendo para onde ele estava antes?
63 Ruhu shine mai bayar da rai; Jiki ba ya amfana komai. Kalmomin da na fada maku ruhu ne, da kuma rai.
É o espírito que dá vida. A carne não lucra nada. As palavras que vos digo são espírito, e são vida.
64 Amma fa akwai wadansun ku da ba su ba da gaskiya ba. Domin tun farko Yesu ya san wadanda ba su ba da gaskiya ba, da kuma wanda zai bashe shi.
Mas há alguns de vocês que não acreditam”. Pois Jesus sabia desde o início quem eram aqueles que não acreditavam, e quem era quem o trairia.
65 Ya fada cewa, “shiyasa na gaya maku, ba mai iya zuwa wurina, sai ta wurin Uban.”
Ele disse: “Por isso vos disse que ninguém pode vir a mim, a menos que seja dado a ele por meu Pai”.
66 Bayan haka, da yawa daga cikin almajiransa suka koma da baya, ba su kara tafiya tare da shi ba.
Nisso, muitos de seus discípulos voltaram e não andaram mais com ele.
67 Sai Yesu ya ce wa goma sha biyun, “ku ba kwa so ku tafi, ko ba haka ba?
Jesus disse, portanto, aos doze: “Você não quer ir embora também, quer?”.
68 Bitrus ya amsa masa ya ce, “Ya Ubangiji, gun wa za mu je? kai kake da maganar rai madawwami. (aiōnios )
Simon Peter respondeu-lhe: “Senhor, a quem iríamos nós? Você tem as palavras da vida eterna. (aiōnios )
69 Mu kwa mun gaskata mun kuma sani kai ne mai tsarkin nan na Allah.”
Nós viemos a acreditar e a saber que você é o Cristo, o Filho do Deus vivo”.
70 Yesu ya ce masu, “Ba ni na zabe ku, goma sha biyu ba, amma dayanku Iblis ne?”
Jesus lhes respondeu: “Eu não escolhi vocês, os doze, e um de vocês é um demônio?”
71 Wato yana magana akan Yahuda dan Siman Iskariyoti, shi kuwa daya daga cikin sha-biyun ne, wanda zai ba da Yesu.
Agora ele falava de Judas, o filho de Simão Iscariotes, pois era ele quem o trairia, sendo um dos doze.