< Yohanna 6 >

1 Bayan waddannan abubuwa, Yesu ya ketare tekun Galili, wanda a ke kira tekun Tibariya.
Après ces choses Jésus s'en alla au delà de la mer de Galilée, qui est [la mer] de Tibériade.
2 Sai taro mai yawa suka bi shi domin suna ganin alamu da yake yi akan marasa lafiya.
Et de grandes troupes le suivaient, à cause qu'ils voyaient les miracles qu'il faisait en ceux qui étaient malades.
3 Sai Yesu ya hau dutse ya zauna a can tare da almajiransa.
Mais Jésus monta sur une montagne, et il s'assit là avec ses Disciples.
4 (Kuma da idin Ketarewa, wato idin Yahudawa, ya kusato.)
Or [le jour de] Pâque, qui était la Fête des Juifs, était proche.
5 Da Yesu ya daga kai sai ya ga babban taro yana zuwa wurinsa, sai ya ce ma Filibus, “Ina za mu sayi gurasar da Mutanen nan za su ci?”
Et Jésus ayant levé ses yeux, et voyant que de grandes troupes venaient à lui, dit à Philippe: d'où achèterons-nous des pains, afin que ceux-ci aient à manger?
6 ( Ya fadi haka ne domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi.)
Or il disait cela pour l'éprouver: car il savait bien ce qu'il devait faire.
7 Filibus ya amsa masa, “gurasar dinari biyu ma ba zata ishi kowannensu ya samu ko kadan ba.”
Philippe lui répondit: [quand nous aurions] pour deux cents deniers de pain, cela ne leur suffirait point, quoique chacun d'eux n'en prît que tant soit peu.
8 Daya daga cikin almajiransa, wato Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus, ya ce masa,
Et l'un de ses Disciples, [savoir] André, frère de Simon Pierre, lui dit:
9 “Ga wani dan yaro nan da dunkule biyar na sha'ir, da kifi biyu. Amma menene wadannan za su yi wa mutane masu yawa?”
Il y a ici un petit garçon qui a cinq pains d'orge et deux poissons; mais qu'est-ce que cela pour tant de gens?
10 Yesu ya ce, “ku sa mutane su zauna.”( wurin kuwa akwai ciyawa.) Sai mazajen suka zauna, sun kai wajen dubu biyar.
Alors Jésus dit: faites asseoir les gens; (or il y avait beaucoup d'herbe en ce lieu-là), les gens donc s'assirent au nombre d'environ cinq mille.
11 Sai Yesu ya dauki gurasar, bayan da ya yi godiya, sai ya rarraba wa wadanda suke zaune. Haka kuma ya rarraba kifin gwargwadon abin da zai ishe su.
Et Jésus prit les pains; et après avoir rendu grâces, il les distribua aux Disciples, et les Disciples à ceux qui étaient assis, et de même des poissons, autant qu'ils en voulaient.
12 Da Mutanen suka ci suka kuma koshi, sai ya ce wa almajiransa, ku tattara gutsattsarin da suka rage, kada ya zama asara.”
Et après qu'ils furent rassasiés, il dit à ses Disciples: amassez les pièces qui sont de reste, afin que rien ne soit perdu.
13 Sai suka cika kwanduna goma sha biyu da gutsattsarin gurasar nan biyar da ya rage bayan da kowa ya ci.
Ils les amassèrent donc, et ils remplirent douze corbeilles des pièces des cinq pains d'orge, qui étaient demeurées de reste à ceux qui en avaient mangé.
14 Da jama'a suka ga alamar da ya yi, sai suka ce, “Hakika wannan shi ne annabin nan mai zuwa cikin duniya.
Or ces gens ayant vu le miracle que Jésus avait fait, disaient: celui-ci est véritablement le Prophète qui devait venir au monde.
15 “Da Yesu ya gane suna shirin zuwa su dauke shi da karfi da yaji su nada shi sarki, sai ya sake komawa kan dutsen da kansa.
Mais Jésus ayant connu qu'ils devaient venir l'enlever afin de le faire Roi, se retira encore tout seul en la montagne.
16 Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara teku.
Et quand le soir fut venu, ses Disciples descendirent à la mer.
17 Suka shiga cikin jirgi, suka haye teku zuwa kafarnahum. (A lokacin duhu ya yi, Yesu kuwa bai riga ya iso wurinsu ba tukuna.)
Et étant montés dans la nacelle, ils passaient au delà de la mer vers Capernaüm, et il était déjà nuit, que Jésus n'était pas encore venu à eux.
18 Iska mai karfin gaske tana kadawa, kuma tekun yana hargowa.
Et la mer s'éleva par un grand vent qui soufflait.
19 Bayan da almajiran suka yi tuki na wajen kimanin mil ashirin da biyar ko talatin, sai suka hango Yesu yana tafiya a kan teku ya kuma kusa da jirgin, sai suka firgita.
Mais après qu'ils eurent ramé environ vingt-cinq ou trente stades, ils virent Jésus marchant sur la mer, et s'approchant de la nacelle; et ils eurent peur.
20 Amma ya ce masu, “Ni ne! kada ku firgita.”
Mais il leur dit: c'est moi, ne craignez point.
21 Sa'an nan suka yarda suka karbe shi a cikin jirgin, kuma nan da nan jirgin ya kai gacci.
Ils le reçurent donc avec plaisir dans la nacelle, et aussitôt la nacelle prit terre [au lieu] où ils allaient.
22 Kashe gari, sauran taron da suke tsaye a dayan hayin tekun suka ga cewa babu wani jirgi a wajen sai dayan, Yesu kuma bai shiga ciki da almajiransa ba, amma almajiransa suka tafi su kadai.
Le lendemain les troupes qui étaient demeurées de l'autre côté de la mer, voyant qu'il n'y avait point là d'autre nacelle que celle-là seule dans laquelle ses Disciples étaient entrés, et que Jésus n'était point entré avec ses Disciples dans la nacelle, mais que ses Disciples s'en étaient allés seuls;
23 Sai dai, akwai wadansu jirage da suka zo daga Tibariya kusa da wurin da taron suka ci gurasa bayan da Ubangiji ya yi godiya.
Et d'autres nacelles étant venues de Tibériade près du lieu où ils avaient mangé le pain, après que le Seigneur eut rendu grâces;
24 Sa'anda taron suka gane cewa Yesu da almajiransa ba su wurin, su da kansu su ka shiga cikin jiragen suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
Ces troupes donc qui voyaient que Jésus n'était point là, ni ses Disciples, montèrent aussi dans ces nacelles, et vinrent à Capernaüm, cherchant Jésus.
25 Da suka same shi a hayin tekun, suka ce masa, “Mallam, yaushe ka zo nan?”
Et l'ayant trouvé au delà de la mer, ils lui dirent: Maître, quand es-tu arrivé ici?
26 Yesu ya amsa masu, da cewa, “hakika, kuna nema na ne, ba don kun ga alamu ba, amma domin kun ci gurasar nan kun koshi.
Jésus leur répondit, et leur dit: en vérité, en vérité je vous dis: vous me cherchez, non parce que vous avez vu des miracles, mais parce que vous avez mangé des pains, et que vous avez été rassasiés.
27 Ku daina yin wahala a kan neman abinci mai lalacewa, sai dai a kan abinci mai dawwama wanda zai kaiku ga rai madawwami wanda Dan Mutum zai ba ku, domin Ubangiji Allah ya sa hatiminsa a kansa.” (aiōnios g166)
Travaillez, non point après la viande qui périt, mais après celle qui est permanente jusque dans la vie éternelle, laquelle le Fils de l'homme vous donnera; car le Père, [savoir] Dieu, l'a approuvé de son cachet. (aiōnios g166)
28 Sai suka ce Masa, “Me za mu yi, domin mu aikata ayyukan Allah?
Ils lui dirent donc: que ferons-nous pour faire les œuvres de Dieu?
29 Yesu ya amsa, “Wannan shi ne aikin Allah: wato ku gaskata da wanda ya aiko.”
Jésus répondit, et leur dit: c'est ici l'œuvre de Dieu, que vous croyiez en celui qu'il a envoyé.
30 Sai suka ce masa, “To wace alama za ka yi, don mu gani mu gaskata ka?
Alors ils lui dirent: quel miracle fais-tu donc, afin que nous le voyions, et que nous te croyions? quelle œuvre fais-tu?
31 Me za ka yi? Kakanninmu sun ci manna a jeji, kamar yadda aka rubuta, “Ya ba su gurasa daga sama su ci.”
Nos pères ont mangé la manne au désert; selon ce qui est écrit: il leur a donné à manger le pain du ciel.
32 Sa'an nan Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, ina gaya maku ba Musa ne ya ba ku gurasa nan daga sama ba, amma Ubana ne ya baku gurasa ta gaskiya daga sama.
Mais Jésus leur dit: en vérité, en vérité je vous dis: Moïse ne vous a pas donné le pain du ciel; mais mon Père vous donne le vrai pain du ciel;
33 Gurasar Allah itace mai saukowa daga sama mai kuma bada rai ga duniya,”
Car le pain de Dieu c'est celui qui est descendu du ciel, et qui donne la vie au monde.
34 Sai suka ce masa, “Mallam, ka rika ba mu irin wannan gurasa kodayaushe.”
Ils lui dirent donc: Seigneur, donne-nous toujours ce pain-là.
35 Yesu ya ce masu, “Ni ne gurasa mai ba da rai. Wanda ya zo wurina ba zai ji yunwa ba, wanda kuma ya gaskanta da ni ba zai kara jin kishi ba.
Et Jésus leur dit: je suis le pain de vie. Celui qui vient à moi, n'aura point de faim; et celui qui croit en moi, n'aura jamais soif.
36 Amma na gaya maku cewa, hakika kun gan ni, duk da haka ba ku ba da gaskiya ba.
Mais je vous ai dit que vous m'avez vu, et cependant vous ne croyez point.
37 Duk wanda Uba ya bani zai zo gare ni, wanda kuwa ya zo gare ni ba zan kore shi ba ko kadan.
Tout ce que mon Père me donne, viendra à moi; et je ne mettrai point dehors celui qui viendra à moi.
38 Gama na sauko daga sama, ba domin in bi nufin kaina ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni.
Car je suis descendu du ciel non point pour faire ma volonté, mais la volonté de celui qui m'a envoyé.
39 Wannan shi ne nufin wanda ya aiko ni, kada in rasa ko daya daga cikin wadannan da ya bani, sai dai in tashe su a ranar karshe.
Et c'est ici la volonté du Père qui m'a envoyé, que je ne perde rien de tout ce qu'il m'a donné, mais que je le ressuscite au dernier jour.
40 Gama wannan shi ne nufin Ubana, duk wanda yake ganin Dan ya kuma gaskata da shi zai sami rai madawwami, ni kuma zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios g166)
Et c'est ici la volonté de celui qui m'a envoyé, que quiconque contemple le Fils, et croit en lui, ait la vie éternelle; c'est pourquoi je le ressusciterai au dernier jour. (aiōnios g166)
41 Sai Yahudawa suka yi gunaguni akansa, domin ya ce, “Nine Gurasar da ta sauko daga sama.”
Or les Juifs murmuraient contre lui de ce qu'il avait dit: je suis le pain descendu du ciel.
42 Suka ce, “Ba wannan ne Yesu Dan Yusufu, wanda Ubansa da Uwarsa mun san su ba? Ta yaya yanzu zai ce, 'Na ya sauko daga sama'?
Car ils disaient: n'est-ce pas ici Jésus, le fils de Joseph, duquel nous connaissons le père et la mère? comment donc dit celui-ci: je suis descendu du ciel?
43 Yesu ya amsa, ya ce masu, “Kada ku yi gunaguni a junanku.
Jésus donc répondit, et leur dit: ne murmurez point entre vous.
44 Ba mai iya zuwa wurina sai dai in Uba wanda ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta karshe.
Nul ne peut venir à moi, si le Père, qui m'a envoyé, ne le tire; et moi, je le ressusciterai au dernier jour.
45 A rubuce yake cikin litattafan anabawa cewa, 'Dukkansu Allah zai koya masu'. Duk wanda ya ji ya kuma koya daga wurin Uba, ya kan zo gare ni.
Il est écrit dans les Prophètes: et ils seront tous enseignés de Dieu. Quiconque donc a écouté le Père, et a été instruit [de ses intentions], vient à moi.
46 Ba cewa wani ya taba ganin Uban ba, sai shi wanda yake daga wurin Allah - shine ya ga Uban.
Non point qu'aucun ait vu le Père, sinon celui qui est de Dieu, celui-là a vu le Père.
47 Hakika, hakika, wanda ya bada gaskiya, yana da rai Madawwami. (aiōnios g166)
En vérité, en vérité je vous dis: qui croit en moi a la vie éternelle. (aiōnios g166)
48 Ni ne Gurasa ta rai.
Je suis le pain de vie.
49 Ubanninku sun ci manna cikin jeji, suka kuma mutu.
Vos pères ont mangé la manne au désert, et ils sont morts.
50 Ga gurasa da ta sauko daga sama, domin mutum ya ci daga cikinta ba kuwa zai mutu ba.
C'est ici le pain qui est descendu du ciel, afin que si quelqu'un en mange, il ne meure point.
51 Ni ne gurasa mai rai da ya sauko daga sama. Duk wanda ya ci daga gurasar, zai rayu har abada. Wannan gurasar da zan bayar jiki na ne don ceton duniya.” (aiōn g165)
Je suis le pain vivifiant qui suis descendu du ciel; si quelqu'un mange de ce pain, il vivra éternellement; et le pain que je donnerai, c'est ma chair, laquelle je donnerai pour la vie du monde. (aiōn g165)
52 Sai Yahudawa suka fusata a tsakanin junansu suka kuma fara gardama, cewa, “Yaya mutumin nan zai iya bamu naman jikinsa mu ci?
Les Juifs donc disputaient entre eux, et disaient: comment celui-ci nous peut-il donner sa chair à manger?
53 Sai Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, in ba ku ci naman jikin Dan mutum ba, ba ku kuma sha jininsa ba, ba za ku sami rai a cikin ku ba.
Et Jésus leur dit: en vérité, en vérité je vous dis, que si vous ne mangez la chair du Fils de l'homme, et ne buvez son sang, vous n'aurez point la vie en vous-mêmes.
54 Dukan wanda ya ci nama na ya kuma sha jinina yana da rai Madawwami, ni kuwa zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios g166)
Celui qui mange ma chair, et qui boit mon sang a la vie éternelle; et je le ressusciterai au dernier jour. (aiōnios g166)
55 Domin namana abinci ne na gaske, jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
Car ma chair est une véritable nourriture, et mon sang est un véritable breuvage.
56 Duk wanda ya ci namana, ya kuma sha jinina yana zamne a ciki na, ni kuma a cikinsa.
Celui qui mange ma chair, et qui boit mon sang, demeure en moi, et moi en lui.
57 Kamar yadda rayayyen Uba ya aiko ni, nake kuma rayuwa saboda Uban, haka ma wanda ya ci namana, zai rayu sabo da ni.
Comme le Père qui est vivant m'a envoyé, et que je suis vivant par le Père; ainsi celui qui me mangera, vivra aussi par moi.
58 Wannan itace gurasar da ta sauko daga sama, ba irin wadda Ubanninku suka ci suka mutu ba. Dukan wanda ya ci gurasar zai rayu har abada.” (aiōn g165)
C'est ici le pain qui est descendu du ciel, non point comme vos pères ont mangé la manne, et ils sont morts; celui qui mangera ce pain, vivra éternellement. (aiōn g165)
59 Yesu ya fadi wadan nan abubuwa a cikin majami'a sa'ad da yake koyarwa a Kafarnahum.
Il dit ces choses dans la Synagogue, enseignant à Capernaüm.
60 Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan Magana yana da karfi, wa zai iya jinta?”
Et plusieurs de ses disciples l'ayant entendu, dirent: cette parole est dure, qui la peut ouïr?
61 Yesu, kuwa da yake ya sani a ransa da cewa almajiransa suna gunagunin wannan, sai ya ce masu, “Wannan ya zamar maku laifi?
Mais Jésus sachant en lui-même que ses disciples murmuraient de cela, leur dit: ceci vous scandalise-t-il?
62 Yaya Ke nan in kun ga Dan Mutum yana hawa inda yake a da?
[Que sera-ce] donc si vous voyez le Fils de l'homme monter où il était premièrement?
63 Ruhu shine mai bayar da rai; Jiki ba ya amfana komai. Kalmomin da na fada maku ruhu ne, da kuma rai.
C'est l'esprit qui vivifie; la chair ne profite de rien; les paroles que je vous dis, sont esprit et vie.
64 Amma fa akwai wadansun ku da ba su ba da gaskiya ba. Domin tun farko Yesu ya san wadanda ba su ba da gaskiya ba, da kuma wanda zai bashe shi.
Mais il y en a [plusieurs] entre vous qui ne croient point; car Jésus savait dès le commencement qui seraient ceux qui ne croiraient point, et qui serait celui qui le trahirait.
65 Ya fada cewa, “shiyasa na gaya maku, ba mai iya zuwa wurina, sai ta wurin Uban.”
Il leur dit donc: c'est pour cela que je vous ai dit, que nul ne peut venir à moi, s'il ne lui est donné de mon Père.
66 Bayan haka, da yawa daga cikin almajiransa suka koma da baya, ba su kara tafiya tare da shi ba.
Dès cette heure-là plusieurs de ses Disciples l'abandonnèrent, et ils ne marchaient plus avec lui.
67 Sai Yesu ya ce wa goma sha biyun, “ku ba kwa so ku tafi, ko ba haka ba?
Et Jésus dit aux douze: et vous, ne vous en voulez-vous point aussi aller?
68 Bitrus ya amsa masa ya ce, “Ya Ubangiji, gun wa za mu je? kai kake da maganar rai madawwami. (aiōnios g166)
Mais Simon Pierre lui répondit: Seigneur! auprès de qui nous en irons-nous? tu as les paroles de la vie éternelle: (aiōnios g166)
69 Mu kwa mun gaskata mun kuma sani kai ne mai tsarkin nan na Allah.”
Et nous avons cru, et nous avons connu que tu es le Christ, le Fils du Dieu vivant.
70 Yesu ya ce masu, “Ba ni na zabe ku, goma sha biyu ba, amma dayanku Iblis ne?”
Jésus leur répondit: ne vous ai-je pas choisis vous douze? et toutefois l'un de vous est un démon.
71 Wato yana magana akan Yahuda dan Siman Iskariyoti, shi kuwa daya daga cikin sha-biyun ne, wanda zai ba da Yesu.
Or il disait cela de Judas Iscariot, [fils] de Simon; car c'était celui à qui il devait arriver de le trahir, quoiqu'il fût l'un des douze.

< Yohanna 6 >