< Yohanna 5 >
1 Bayan haka akwai idi na yahudawa, kuma Yesu ya tafi Urashalima.
After these things was a festival day of the Jews, and Jesus went up to Jerusalem.
2 To a cikin Urashilima kusa da kofar tumaki akwai tabki, wanda ake kira Baitasda da harshen Ibraniyanci, yana da shirayi biyar.
Now there is at Jerusalem a pond, called Probatica, which in Hebrew is named Bethsaida, having five porches.
3 Taron mutane dayawa masu ciwo da, makafi da guragu da shanyayyu suna kwance a wurin [suna jira a dama ruwan].
In these lay a great multitude of sick, of blind, of lame, of withered; waiting for the moving of the water.
4 Gama mala'ikan Ubangiji kan sabko a cikin tabkin ya dama ruwan, wanda ya fara taba ruwan sai ya warke komai cutar da yake da ita.
And an angel of the Lord descended at certain times into the pond; and the water was moved. And he that went down first into the pond after the motion of the water, was made whole, of whatsoever infirmity he lay under.
5 Akwai wani mutum a bakin tabki yana kwance yana da rashin lafiya har shekara talatin da takwas.
And there was a certain man there, that had been eight and thirty years under his infirmity.
6 Da Yesu ya gan shi yana kwance a wurin sai ya gane ya dade a wurin, sai ya ce masa, “Ko kana so ka warke?”
Him when Jesus had seen lying, and knew that he had been now a long time, he saith to him: Wilt thou be made whole?
7 Sai mai rashin lafiyar ya amsa ya ce, “Malam, bani da kowa da zai sa ni a cikin tabkin idan ruwan ya motsa. Yayinda na ke kokari sai wani ya riga ni.”
The infirm man answered him: Sir, I have no man, when the water is troubled, to put me into the pond. For whilst I am coming, another goeth down before me.
8 Yesu ya ce masa,” Ka tashi ka dauki shimfidarka ka tafi.”
Jesus saith to him: Arise, take up thy bed, and walk.
9 Nan dan nan Mutumin ya warke, ya dauki shimfidarsa ya tafi. Ranar kuwa Asabar ce.
And immediately the man was made whole: and he took up his bed, and walked. And it was the sabbath that day.
10 Sai Yahudawa suka ce da wanda aka warkar din, “Ai, Asabar ce, bai kuwa halatta ka dauki shimfidarka ba.”
The Jews therefore said to him that was healed: It is the sabbath; it is not lawful for thee to take up thy bed.
11 Sai ya amsa ya ce, “Ai wanda ya warkar da ni, shine ya ce mani 'Dauki shimfidarka, ka tafi.”
He answered them: He that made me whole, he said to me, Take up thy bed, and walk.
12 Suka tambaye shi, “wane mutum ne ya ce maka, 'Dauki shimfidar ka yi tafiya'?”
They asked him therefore: Who is that man who said to thee, Take up thy bed, and walk?
13 Sai dai, shi wanda aka warka din, ba san ko wanene ya warkar da shi ba, domin Yesu ya riga ya tafi aboye, saboda akwai taro a wurin.
But he who was healed, knew not who it was; for Jesus went aside from the multitude standing in the place.
14 Bayan haka, Yesu ya same shi a Haikalin, ya ce masa, “ka ga fa, ka warke. To, kada ka kara yin zunubi don kada wani abu da ya fi wannan muni ya same ka.”
Afterwards, Jesus findeth him in the temple, and saith to him: Behold thou art made whole: sin no more, lest some worse thing happen to thee.
15 Sai mutumin ya tafi ya gaya wa Yahuduwa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
The man went his way, and told the Jews, that it was Jesus who had made him whole.
16 To saboda haka Yahudawa suka fara tsanantawa Yesu, don ya yi wadannan abubuwa ran Asabar.
Therefore did the Jews persecute Jesus, because he did these things on the sabbath.
17 Yesu kuwa ya amsa masu ya ce, “Ubana yana aiki har yanzu, ni ma ina aiki.”
But Jesus answered them: My Father worketh until now; and I work.
18 Saboda haka, Yahudawa suka kara nema su kashe shi ba don ya keta Asabar kadai ba, amma kuma domin ya ce Allah Ubansa ne, wato yana maida kansa dai-dai da Allah.
Hereupon therefore the Jews sought the more to kill him, because he did not only break the sabbath, but also said God was his Father, making himself equal to God.
19 Yesu ya amsa masu ya ce, hakika hakika, ina gaya maku, Dan ba ya yin kome shi kadai, sai abin da ya ga Uba yana yi.
Then Jesus answered, and said to them: Amen, amen, I say unto you, the Son cannot do any thing of himself, but what he seeth the Father doing: for what things soever he doth, these the Son also doth in like manner.
20 Domin Uban na kaunar Dan, yana kuma nuna masa dukan abinda shi da kansa yake yi, kuma zai nuna masa abubuwan da suka fi wadannan, domin ku yi mamaki.
For the Father loveth the Son, and sheweth him all things which himself doth: and greater works than these will he shew him, that you may wonder.
21 Gama kamar yadda Uba yakan tada matattu ya kuma basu rai, haka Dan ma yake bada rai ga duk wanda ya nufa.
For as the Father raiseth up the dead, and giveth life: so the Son also giveth life to whom he will.
22 Gama Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya damka dukan hukunci ga Dan,
For neither doth the Father judge any man, but hath given all judgment to the Son.
23 domin kowa ya girmama Dan, kamar yadda suke girmama Uban. Shi wanda ba ya girmama Dan, ba ya girmama Uban da ya aiko shi.
That all men may honour the Son, as they honour the Father. He who honoureth not the Son, honoureth not the Father, who hath sent him.
24 Hakika, hakika, duk mai jin Maganata, yana kuma gaskata wanda ya aiko ni, yana da rai madawwami ba kuma za a kashe shi ba, domin ya ratse daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios )
Amen, amen I say unto you, that he who heareth my word, and believeth him that sent me, hath life everlasting; and cometh not into judgment, but is passed from death to life. (aiōnios )
25 Hakika hakika, ina gaya maku, lokaci na zuwa, har ma ya yi da matattatu za su ji muryar Dan Allah, wadanda suka ji kuwa za su rayu.
Amen, amen I say unto you, that the hour cometh, and now is, when the dead shall hear the voice of the Son of God, and they that hear shall live.
26 Kammar yada Uba ya ke da rai a cikinsa, haka ya ba Dan don ya zama da rai cikin kansa.
For as the Father hath life in himself, so he hath given the Son also to have life in himself:
27 Uban ya kuma ba Dan ikon zartar da hukunci, saboda shi ne Dan Mutum.
And he hath given him power to do judgment, because he is the Son of man.
28 Kada ku yi mamakin wannan, domin lokaci na zuwa da duk wadanda suke kaburbura za su ji muryarsa,
Wonder not at this; for the hour cometh, wherein all that are in the graves shall hear the voice of the Son of God.
29 su kuma fito: wadanda suka aikata nagarta zawa tashi na rai, wadanda suka aikata mugunta kuwa zuwa tashi na hukunci.
And they that have done good things, shall come forth unto the resurrection of life; but they that have done evil, unto the resurrection of judgment.
30 Ba na iya yin kome ni da kai na. Yadda na ke ji, haka nake yin hukunci, Hukunci na kuwa na adalci ne, domin ba nufin kaina nake bi ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni.
I cannot of myself do any thing. As I hear, so I judge: and my judgment is just; because I seek not my own will, but the will of him that sent me.
31 Idan zan yi shaida game da kaina, shaidata baza ta zama gaskiya ba.
If I bear witness of myself, my witness is not true.
32 Akwai wani wanda ya ke bada shaida game da ni, na kuwa sani shaidar da yake bayarwa game da ni gaskiya ce.
There is another that beareth witness of me; and I know that the witness which he witnesseth of me is true.
33 Kun aika zuwa wurin Yahaya, shi kuma ya yi shaidar gaskiya.
You sent to John, and he gave testimony to the truth.
34 Duk da haka shaidar da na karba bata mutum bace. Na fadi wadanan abubuwa domin ku sami ceto.
But I receive not testimony from man: but I say these things, that you may be saved.
35 Yahaya fitila ne mai ci, mai haske ne kuma, kun yarda ku yi farinciki da haskensa dan lokaci kadan.
He was a burning and a shining light: and you were willing for a time to rejoice in his light.
36 Amma shaidar da ni ke da ita ta fi ta Yahaya karfi. Domin ayyukan da Uba ya bani ni in yi, wato ainihin ayyukan da nake yi, su ne suke shaida ta cewa, Uba ne ya aiko ni.
But I have a greater testimony than that of John: for the works which the Father hath given me to perfect; the works themselves, which I do, give testimony of me, that the Father hath sent me.
37 Uba wanda ya aiko ni, shi da kansa ya shaide ni. Ba ku taba jin muryar sa ba, ko ganin kamanninsa.
And the Father himself who hath sent me, hath given testimony of me: neither have you heard his voice at any time, nor seen his shape.
38 Maganarsa kuwa ba ta zaune a zuciyarku, domin baku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
And you have not his word abiding in you: for whom he hath sent, him you believe not.
39 Kuna nazarin littattafai, don a tsammaninku a cikinsu za ku sami rai Madawwami, alhali kuwa su ne suke shaidata. (aiōnios )
Search the scriptures, for you think in them to have life everlasting; and the same are they that give testimony of me. (aiōnios )
40 kuma baku niyyar zuwa wurina domin ku sami rai.
And you will not come to me that you may have life.
41 Ba na karbar yabo daga wurin mutane,
I receive glory not from men.
42 amma na sani baku da kaunar Allah a zuciyarku.
But I know you, that you have not the love of God in you.
43 Na zo a cikin sunan Ubana, amma ba ku karbe ni ba. Idan wani ya zo da sunan kansa, za ku karbe shi.
I am come in the name of my Father, and you receive me not: if another shall come in his own name, him you will receive.
44 Ta yaya za ku ba da gaskiya, ku da kuke karban yabo daga junanku, amma ba ku neman yabon dake zuwa daga wurin Allah?
How can you believe, who receive glory one from another: and the glory which is from God alone, you do not seek?
45 Kada ku yi tunani zan zarge ku a wurin Uba. Mai zargin ku shine Musa, wanda kuka sa begenku a cikin sa.
Think not that I will accuse you to the Father. There is one that accuseth you, Moses, in whom you trust.
46 Inda kun gaskata Musa, da kun gaskata da ni domin ya yi rubutu game da ni.
For if you did believe Moses, you would perhaps believe me also; for he wrote of me.
47 Idan kuwa ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, ta yaya za ku gaskata maganata?”
But if you do not believe his writings, how will you believe my words?