< Yohanna 4 >

1 Da Yesu ya sani cewa Farisawa sun ji cewa yana samun almajirai yana kuma yi masu baftisma fiye da Yahaya
Da Herren nu erfarede, at Farisæerne havde hørt, at Jesus vandt flere Disciple og døbte flere end Johannes
2 (ko da shike ba Yesu da kansa ke yin baftismar ba, amma almajiransa ne),
(skønt Jesus ikke døbte selv, men hans Disciple):
3 ya bar Yahudiya ya koma Galili.
da forlod han Judæa og drog atter bort til Galilæa.
4 Amma ya zamar masa dole ya ratsa ta Samariya.
Men han maatte rejse igennem Samaria.
5 Ya zo wani birnin Samariya, mai suna Sika, kusa da filin da Yakubu ya ba dansa Yusufu.
Han kommer da til en By i Samaria, som kaldes Sykar, nær ved det Stykke Land, som Jakob gav sin Søn Josef.
6 Rijiyar Yakubu na wurin. Da Yesu ya gaji da tafiyarsa sai ya zauna gefen rijiyar. Kusan karfe goma sha biyu na rana ne.
Og der var Jakobs Brønd. Jesus satte sig da, træt af Rejsen, ned ved Brønden; det var ved den sjette Time.
7 Wata mace, Ba-Samariya ta zo domin ta dibi ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha.”
En samaritansk Kvinde kommer for at drage Vand op. Jesus siger til hende: „Giv mig noget at drikke!”
8 Gama almajiransa sun tafi cikin gari don sayen abinci.
Hans Disciple vare nemlig gaaede bort til Byen for at købe Mad.
9 Sai ba-Samariyar tace masa, “Yaya kai da kake Bayahude kake tambaya ta ruwan sha, ni da nike 'yar Samariya?” Domin Yahudawa ba su harka da Samariyawa.
Da siger den samaritanske Kvinde til ham: „Hvorledes kan dog du, som er en Jøde, bede mig, som er en samaritansk Kvinde, om noget at drikke?” Thi Jøder holde ikke Samkvem med Samaritaner.
10 Sai Yesu ya amsa yace mata, “In da kin san kyautar Allah, da shi wanda yake ce da ke, 'Ba ni ruwan sha,' da kin roke shi, sai kuma ya ba ki ruwan rai.”
Jesus svarede og sagde til hende: „Dersom du kendte Guds Gave, og hvem det er, som siger til dig: Giv mig noget at drikke, da bad du ham, og han gav dig levende Vand.”
11 Matar tace masa, “Mallam, ga shi ba ka da guga, kuma rijiyar tana da zurfi. Ina za ka samu ruwan rai?
Kvinden siger til ham: „Herre! du har jo intet at drage op med, og Brønden er dyb; hvorfra har du da det levende Vand?
12 Ai ba ka fi Ubanmu Yakubu ba, ko ka fi shi, shi wanda ya ba mu rijiyar, shi kansa kuma ya sha daga cikin ta, haka kuma 'ya'yansa da shanunsa?”
Mon du er større end vor Fader Jakob, som har givet os Brønden, og han har selv drukket deraf og hans Børn og hans Kvæg?”
13 Yesu ya amsa yace mata, “duk wanda ya sha daga wannan ruwan zai sake jin kishi,
Jesus svarede og sagde til hende: „Hver den, som drikker af dette Vand, skal tørste igen.
14 amma duk wanda ya sha daga ruwa da zan ba shi ba zai sake jin kishi ba. Maimakon haka, ruwan da zan bashi zai zama mabulbular ruwa a cikinsa wanda ke bulbula zuwa rai madawwami.” (aiōn g165, aiōnios g166)
Men den, som drikker af det Vand, som jeg giver ham, skal til evig Tid ikke tørste; men det Vand, som jeg giver ham, skal blive i ham en Kilde af Vand, som fremvælder til et evigt Liv.” (aiōn g165, aiōnios g166)
15 Matar tace masa, “Mallam, ka ba ni wannan ruwa yadda ba zan kara jin kishi ba ba kuma sai na zo nan don in dibi ruwa ba.”
Kvinden siger til ham: „Herre! giv mig dette Vand, for at jeg ikke skal tørste og ikke komme hid for at drage op.”
16 Yesu ya ce mata, “Je, ki kira maigidanki ku zo nan tare.”
Jesus siger til hende: „Gaa bort, kald paa din Mand, og kom hid!”
17 Matar ta amsa tace masa, “Ba ni da miji.” Yesu yace, “Kin fadi daidai da kika ce, 'ba ni da miji,'
Kvinden svarede og sagde: „Jeg har ingen Mand.” Jesus siger til hende: „Med Rette sagde du: Jeg har ingen Mand.
18 domin kin auri mazaje har biyar, kuma wanda kike da shi yanzu ba mijin ki bane. Abinda kika fada gaskiya ne.”
Thi du har haft fem Mænd; og han, som du nu har, er ikke din Mand. Det har du sagt sandt.”
19 Matar tace masa, “Mallam, Na ga kai annabi ne.
Kvinden siger til ham: „Herre! jeg ser, at du er en Profet.
20 Ubaninmu sun yi sujada a wannan dutse, amma kun ce Urushalima ce wurin da ya kamata mutane su yi sujada.”
Vore Fædre have tilbedet paa dette Bjerg, og I sige, at i Jerusalem er Stedet, hvor man bør tilbede.”
21 Yesu ya ce mata, “Mace, ki gaskata ni, cewa lokaci na zuwa wanda ba za ku yi wa Uban sujada ba ko akan wannan dutse ko a Urushalima.
Jesus siger til hende: „Tro mig, Kvinde, at den Time kommer, da det hverken skal være paa dette Bjerg eller i Jerusalem, at I tilbede Faderen.
22 Ku kuna bauta wa abinda ba ku sani ba. Mu muna bauta wa abinda muka sani, gama ceto daga Yahudawa yake.
I tilbede det, I ikke kende; vi tilbede det, vi kende; thi Frelsen kommer fra Jøderne.
23 Sai dai, sa'a tana zuwa, har ma ta yi, wadda masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a cikin ruhu da gaskiya, domin irin wadannan ne Uban ke nema su zama masu yi masa sujada.
Men den Time kommer, ja, den er nu, da de sande Tilbedere skulle tilbede Faderen i Aand og Sandhed; thi det er saadanne Tilbedere, Faderen vil have.
24 Allah Ruhu ne, kuma mutanen da ke yi masa sujada, dole su yi sujada cikin ruhu da gaskiya.”
Gud er Aand, og de, som tilbede ham, bør tilbede i Aand og Sandhed.”
25 Matar ta ce masa, “Na san Almasihu na zuwa (wanda ake kira Kristi). Sa'adda ya zo, zai bayyana mana kowane abu.
Kvinden siger til ham: „Jeg ved, at Messias kommer (hvilket betyder Kristus); naar han kommer, skal han kundgøre os alle Ting.”
26 Yesu ya ce mata, “Ni ne shi, wanda ke yi maki magana.”
Jesus siger til hende: „Det er mig, jeg, som taler med dig.”
27 A daidai wannan lokaci, almajiransa suka dawo. Suna ta mamakin dalilin da yasa yake magana da mace, amma babu wanda yace, “Me kake so?” Ko kuma, “Don me ka ke magana da ita?”
Og i det samme kom hans Disciple, og de undrede sig over, at han talte med en Kvinde; dog sagde ingen: „Hvad søger du?” eller: „Hvorfor taler du med hende?”
28 Sai matar ta bar tulunta, ta koma cikin gari, tace wa mutanen,
Da lod Kvinden sin Vandkrukke staa og gik bort til Byen og siger til Menneskene der:
29 “Ku zo ku ga wani mutum wanda ya gaya mani duk wani abu da na taba yi. Wannan dai ba Almasihun bane, ko kuwa?”
„Kommer og ser en Mand, som har sagt mig alt det, jeg har gjort; mon han skulde være Kristus?”
30 Suka bar garin suka zo wurinsa.
De gik ud af Byen og kom gaaende til ham.
31 A wannan lokacin, almajiransa suna rokansa, cewa, “Mallam, ka ci.”
Imidlertid bade Disciplene ham og sagde: „Rabbi, spis!”
32 Amma ya ce masu, “ina da abinci da ba ku san komai akai ba.”
Men han sagde til dem: „Jeg har Mad at spise, som I ikke kende.”
33 Sai almajiran suka ce da junansu, “Babu wanda ya kawo masa wani abu ya ci, ko akwai ne?”
Da sagde Disciplene til hverandre: „Mon nogen har bragt ham noget at spise?”
34 Yesu ya ce masu, “Abincina shine in yi nufin wanda ya aiko ni, in kuma cika aikinsa.
Jesus siger til dem: „Min Mad er, at jeg gør hans Villie, som udsendte mig, og fuldbyrder hans Gerning.
35 Ba ku kan ce, 'akwai wata hudu tukuna kafin girbi ya zo ba?' Ina gaya maku, daga idanunku ku ga gonakin, sun rigaya sun isa girbi.
Sige I ikke: Der er endnu fire Maaneder, saa kommer Høsten? Se, jeg siger eder, opløfter eders Øjne og ser Markerne; de ere allerede hvide til Høsten.
36 Shi wanda ke girbi yakan karbi sakamako ya kuma tattara amfanin gona zuwa rai na har abada, ta haka shi mai shuka da shi mai girbi za su yi farinciki tare. (aiōnios g166)
Den, som høster, faar Løn og samler Frugt til et evigt Liv, saa at de kunne glæde sig tilsammen, baade den, som saar, og den, som høster. (aiōnios g166)
37 Gama cikin wannan maganar take, 'Wani na shuka, wani kuma na girbi.'
Thi her er det Ord sandt: En saar, og en anden høster.
38 Na aike ku ku yi girbin abinda ba ku yi aiki a kai ba. Wandansu sun yi aiki, ku kuma kun shiga cikin wahalarsu.
Jeg har udsendt eder at høste det, som I ikke have arbejdet paa; andre have arbejdet, og I ere gaaede ind i deres Arbejde.”
39 Yawancin Samariyawan da ke wannan birni suka gaskata da shi sabili da labarin matar data bada shaida, “Ya gaya mani duk abinda na taba yi.”
Men mange af Samaritanerne fra den By troede paa ham paa Grund af Kvindens Ord, da hun vidnede: „Han har sagt mig alt det, jeg har gjort.”
40 To sa'adda Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roke shi ya zauna tare da su, ya kuwa zauna wurin kwana biyu.
Da nu Samaritanerne kom til ham, bade de ham om at blive hos dem; og han blev der to Dage.
41 Wasu da dama kuma suka gaskata domin maganarsa.
Og mange flere troede for hans Ords Skyld.
42 Suka cewa matar, “Mun bada gaskiya, ba saboda maganar ki kadai ba, amma mu kanmu munji, yanzu kuma mun sani cewa wannan lallai shine mai ceton duniya.”
Og til Kvinden sagde de: „Vi tro nu ikke længer for din Tales Skyld; thi vi have selv hørt, og vi vide, at denne er sandelig Verdens Frelser.”
43 Bayan wadannan kwana biyu, ya bar wurin zuwa Galili.
Men efter de to Dage gik han derfra til Galilæa.
44 Domin Yesu da kansa yace, ba a girmama annabi a kasarsa.
Thi Jesus vidnede selv, at en Profet ikke bliver æret i sit eget Fædreland.
45 Da ya zo Galili, Galiliyawan suka marabce shi. Sun ga dukan abubuwan da ya yi a Urushalima wurin idin, domin su ma sun je idin.
Da han nu kom til Galilæa, toge Galilæerne imod ham, fordi de havde set alt det, som han gjorde i Jerusalem paa Højtiden; thi ogsaa de vare komne til Højtiden.
46 Kuma ya koma Kana ta Galili inda ya mayar da ruwa zuwa ruwan inabi. Akwai wani ma'aikacin fada wanda dansa na rashin lafiya a Kafarnahum.
Han kom da atter til Kana i Galilæa, hvor han havde gjort Vandet til Vin. Og der var en kongelig Embedsmand, hvis Søn laa syg i Kapernaum.
47 Da ya ji cewa Yesu ya bar Yahudiya ya koma Galili, sai ya tafi wurin Yesu ya roke shi ya sauko ya warka da dansa wanda ke bakin mutuwa.
Da denne hørte, at Jesus var kommen fra Judæa til Galilæa, gik han til ham og bad om, at han vilde komme ned og helbrede hans Søn; thi han var Døden nær.
48 Yesu yace masa, “Idan ba ku ga alamu da mu'ujizai ba, ba za ku gaskata ba.”
Da sagde Jesus til ham: „Dersom I ikke se Tegn og Undergerninger, ville I ikke tro.”
49 Ma'aikacin ya ce masa, “Mallam, ka sauko kafin da na ya mutu.”
Embedsmanden siger til ham: „Herre! kom, før mit Barn dør.”
50 Yesu yace masa, “Je ka. Dan ka ya rayu.” Mutumin ya gaskata maganar da Yesu ya gaya masa, Sai yayi tafiyarsa.
Jesus siger til ham: „Gaa bort, din Søn lever.” Og Manden troede det Ord, som Jesus sagde til ham, og gik bort.
51 Yayin da yake sauka kasa, bayinsa suka same shi, suna cewa, danka yana raye.
Men allerede medens han var paa Hjemvejen, mødte hans Tjenere ham og meldte, at hans Barn levede.
52 Sai ya tambaye su sa'ar da ya fara samun sauki. Suka amsa masa, “Jiya a sa'a ta bakwai zazabin ya bar shi.”
Da udspurgte han dem om den Time, i hvilken det var blevet bedre med ham; og de sagde til ham: „I Gaar ved den syvende Time forlod Feberen ham.”
53 Sai Uban ya gane cewa wannan sa'a ce Yesu ya ce masa, “Jeka, danka na raye.” Sabili da haka, shi da dukan gidansa suka bada gaskiya.
Da skønnede Faderen, at det var sket i den Time, da Jesus sagde til ham: „Din Søn lever;” og han troede selv og hele hans Hus.
54 Wannan ce alama ta biyu da Yesu ya yi bayan da ya bar Yahudiya zuwa Galili.
Dette var det andet Tegn, som Jesus gjorde, da han var kommen fra Judæa til Galilæa.

< Yohanna 4 >