< Yohanna 3 >
1 akwai wani Bafarise da ake kira Nikodimu, shugaba a cikin Yahudawa.
Havia um fariseu chamado Nicodemos, membro do conselho superior judeu.
2 Wannan mutum ya zo wurin Yesu da dare ya ce masa, “Rabbi, mun sani cewa kai malami ne da kazo daga wurin Allah, gama ba wanda zai iya yin wadannan alamu da kake yi sai idan Allah na tare da shi.”
Certa noite, ele foi ao lugar em que Jesus estava e disse: “Rabi, nós sabemos que você é um mestre enviado por Deus, pois ninguém pode fazer os milagres que você faz se Deus não estiver com ele.”
3 Yesu ya amsa masa, “Hakika, hakika, idan ba a sake haifuwar mutum ba, ba zai iya ganin mulkin Allah ba.”
Jesus respondeu: “Eu lhe digo que isto é verdade: a não ser que tenha renascido, você não poderá vivenciar o Reino de Deus.”
4 Nikodimu ya ce masa, “Yaya za a sake haifuwar mutum bayan ya tsufa? Ba zai iya sake shiga cikin cikin uwarsa kuma a haife shi ba, zai iya?”
“Como pode um homem velho nascer de novo?”, Nicodemos perguntou. “Não é possível voltar para o útero de sua mãe e nascer uma segunda vez.”
5 Yesu ya amsa, “Hakika, hakika, idan ba a haifi mutum da ruwa da kuma Ruhu ba, ba zai iya shiga cikin mulkin Allah ba.
Jesus lhe disse: “Eu lhe digo que isto é verdade: você não pode entrar no Reino de Deus, a não ser que nasça da água e do Espírito.
6 Abin da aka haifa ta wurin jiki, jiki ne, kuma abin da aka haifa ta wurin Ruhu, Ruhu ne.
Quem nasce da carne é um ser de natureza humana, e quem nasce do Espírito é um ser de natureza espiritual.
7 Kada ka yi mamaki don na ce maka, 'dole a maya haifuwar ka.'
Não fique surpreso por eu lhe dizer que todos vocês devem nascer de novo.
8 Iska takan hura duk inda ta ga dama. Ka kan ji motsin ta, amma ba ka san inda ta fito ko inda za ta tafi ba. Haka duk wanda aka haifa daga Ruhu.”
O vento sopra onde quer, você consegue ouvi-lo, mas não sabe de onde vem e nem para onde vai. O mesmo acontece com todas as pessoas que nascem do Espírito.”
9 Nikodimu ya amsa yace masa, “Yaya wannan zai yiwu?”
“Como isso é possível?”, Nicodemos perguntou.
10 Yesu ya amsa yace masa, “Kai malami ne a Israila amma ba ka san wadannan al'amura ba?
Jesus respondeu: “Você é um importante mestre em Israel e, ainda assim, não entende isso?”, Jesus respondeu.
11 Hakika, hakika, ina gaya maka, muna fadin abubuwan da muka sani, kuma muna shaida abubuwan da muka gani. Duk da haka ba ku karbi shaidar mu ba.
“Eu lhe digo que isto é verdade: nós falamos sobre o que sabemos e damos provas em relação ao que vimos, mas vocês se recusam a aceitar o nosso testemunho.
12 Idan na gaya maka abubuwan da ke na duniya amma baka gaskata ba, to yaya zaka gaskata idan na gaya maka abubuwa na sama?
Se vocês não creem no que eu digo quando eu falo sobre as coisas deste mundo, como poderiam acreditar no que eu falo se eu contasse a vocês sobre as coisas do céu?
13 Babu wanda ya taba hawa zuwa sama sai dai shi wanda ya sauko daga sama: wato Dan Mutum.
Ninguém subiu ao céu, a não ser o Filho do Homem, que desceu do céu.
14 Kamar yadda Musa ya ta da maciji a jeji, haka ma dole a ta da Dan Mutum
Exatamente como Moisés levantou a serpente no deserto, assim o Filho do Homem deve ser levantado,
15 domin dukan wadanda suka bada gaskiya gareshi su sami rai na har abada. (aiōnios )
para que todos os que acreditam nele tenham a vida eterna. (aiōnios )
16 Gama Allah ya kaunaci duniya sosai, har ya ba da makadaicin Dansa, domin duk wanda ya bada gaskiya gareshi, kada ya mutu, amma ya samu rai madawwami. (aiōnios )
Pois Deus amou tanto o mundo, que deu o seu único Filho, para que todos os que acreditam nele não morram, mas, sim, tenham a vida eterna. (aiōnios )
17 Gama Allah bai aiko da Dansa cikin duniya domin ya kayar da duniya ba, amma domin a ceci duniya ta wurin sa.
Deus não mandou o Filho ao mundo para condená-lo, mas para que o mundo encontre a salvação por meio dele.
18 Duk wanda ya bada gaskiya gare shi ba a kayar da shi ba, amma duk wanda bai bada gaskiya gare shi ba an riga an kayar da shi, domin bai bada gaskiya ga sunan wannan da shi kadai ne Dan Allah ba.
As pessoas que creem nele não são condenadas; ao passo que, os que não creem nele são condenados, pois eles não acreditam no único Filho de Deus.
19 Wannan shi ne dalilin shari'ar, domin haske ya zo duniya, amma mutane suka kaunaci duhu fiye da hasken, sabili da ayyukan su na mugunta ne.
É assim que os casos são decididos: a luz veio ao mundo, mas as pessoas amaram mais as trevas do que a luz, pois as suas ações eram más.
20 Domin duk wanda ke mugayen ayyuka ya ki haske, kuma baya zuwa wurin hasken domin kada ayyukansa su bayyanu.
Todos aqueles que fazem o mal odeiam a luz e se afastam dela, porque eles não querem que as suas ações sejam mostradas.
21 Sai dai duk wanda yake aikata gaskiya kan zo wurin hasken domin ayyukansa, da ake aiwatarwa ga Allah, su bayyanu.
Mas, as pessoas que fazem o bem vão para a luz, para que as suas ações, que são realizadas de acordo com a vontade de Deus, sejam reveladas.”
22 Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi kasar Yahudiya. A can ya dan zauna tare da su ya kuma yi Baftisma.
Depois disso, Jesus e seus discípulos foram para a Judeia e passaram algum tempo lá batizando as pessoas.
23 Yahaya ma yana Baftisma a Ainon kusa da Salim domin akwai ruwa da yawa a can. Mutane na zuwa wurin sa yana masu Baftisma,
João também estava batizando em Enom, perto de Salim, porque lá havia muita água e as pessoas continuavam a chegar para serem batizadas.
24 domin a lokacin ba a jefa Yahaya a kurkuku ba tukuna.
(Isso foi antes de João Batista ser preso.)
25 Sai gardama ta taso tsakanin almajiran Yahaya da wani Bayahude akan al'adun tsarkakewa.
Surgiu uma discussão entre os discípulos de João e os judeus em relação à purificação cerimonial.
26 Suka je wurin Yahaya suka ce, “Rabbi, wanda yake tare da kai a dayan ketaren kogin Urdun, kuma ka shaida shi, duba, yana baftisma, kuma mutane duka suna zuwa wurin sa.”
Eles foram até João e lhe disseram: “Rabi, o homem com quem você estava no outro lado do rio Jordão, para quem deu o seu apoio, agora está batizando e todos estão indo até ele!”
27 Yahaya ya amsa, “Mutum ba zai iya samun wani abu ba sai an ba shi daga sama.
João respondeu: “Uma pessoa só recebe o que é dado pelo céu.
28 Ku da kanku zaku shaida na ce, 'Ba ni ne Almasihu ba' amma amaimakon haka, 'an aiko ni kafin shi.'
Vocês mesmos são testemunhas de que eu disse: ‘Eu não sou o Messias. Eu fui enviado para preparar o caminho dele.’
29 Amaryar ta angon ce. Yanzu abokin angon, wanda ke tsaye yana saurarensa, yana murna sosai saboda muryan angon. Murnata ta cika domin wannan.
Em um casamento, a noiva pertence ao noivo. O padrinho espera, escutando o que o noivo tem a falar e fica muito feliz ao ouvir a voz do noivo. A minha felicidade está agora igualmente completa.
30 Dole shi ya karu, ni kuma in ragu.
Ele deve se tornar mais importante, e a minha importância vai diminuir na mesma proporção.”
31 Shi wanda ya fito daga sama ya fi kowa. Shi Wanda ya zo daga duniya, na duniya ne, kuma game da duniya yake magana. Shi wanda ya fito daga sama yana saman kowa.
Aquele que vem de cima é mais importante do que tudo. Quem vem da terra pertence à terra e fala sobre as coisas terrenas. Quem vem do céu é mais importante do que tudo.
32 Ya shaida abubuwan da ya ji ya kuma gani, amma babu wanda ya karbi shaidarsa.
Ele dá provas em relação ao que viu e ouviu, mas ninguém aceita o que ele diz.
33 Duk wanda ya karbi shaidarsa ya tabbatar Allah gaskiya ne.
Entretanto, aquele que aceita o que ele fala confirma que Deus é verdadeiro.
34 Domin duk wanda Allah ya aika kan yi magana da kalmomin Allah. Domin bai bada Ruhun da ma'auni ba.
Pois aquele que Deus enviou fala as palavras de Deus, porque Deus lhe dá o Espírito sem limitações.
35 Uban ya kaunaci Dan, ya kuma ba da dukan komai a hanunsa.
O Pai ama o Filho e colocou tudo em suas mãos.
36 Shi wanda ya bada gaskiya ga Dan ya na da rai madawwami, amma wanda ya ki yiwa Dan biyayya ba zai ga rai ba, amma fushin Allah na kansa. (aiōnios )
Quem crê no Filho tem a vida eterna. Porém, quem se recusar a crer no Filho não terá a vida eterna, mas sofrerá o castigo de Deus. (aiōnios )