< Yohanna 21 >

1 Bayan wadannan abubuwa, Yesu ya sake bayyana kansa ga almajiran a bakin tekun Tibariya. Ga yadda ya bayyana kansa:
After these things, Jesus showed himself again to his disciples, at the sea of Tiberias: and he showed himself thus:
2 Saminu Bitrus na tare da Toma wanda ake kira Dan Tagwai, da Natana'ilu daga Kana ta kasar Galili, da 'ya'yan nan na Zabadi, da kuma wadansu almajiran Yesu biyu.
There were together, Simon Cephas, and Thomas called the Twin, and Nathaniel who was of Cana in Galilee, and the sons of Zebedee, and two other of the disciples.
3 Saminu Bitrus yace masu, “Zani su.” sukace masa “Mu ma za mu je tare da kai.” Sai suka fita suka shiga jirgi, amma a daren nan basu kama komai ba.
Simon Cephas said to them: I will go and catch fishes. They said to him: We will go with thee. And they went, and embarked in a ship: and that night, they caught nothing.
4 To, gari na wayewa, sai ga Yesu tsaye a bakin gaci, amma almajiran basu gane cewa Yesu bane.
And when it was morning, Jesus stood on the shore of the sea: and the disciples did not know that it was Jesus.
5 Sai Yesu yace masu, “Samari, kuna da wani abinda za a ci?” Suka amsa masa sukace “A'a”.
And Jesus said to them: Lads, have ye any thing to eat? They say to him: No.
6 Yace masu, “Ku jefa taru dama da jirgin zaku samu wasu.” Suka jefa tarunsu har suka kasa jawo shi don yawan kifin.
He said to them: Cast your net on the right side of the ship, and ye will find them. And they cast; and they could not draw up the net, because of the multitude of fishes it contained.
7 Sai almajirin nan da Yesu yake kauna yace wa Bitrus, “Ubangiji ne fa!” Da Saminu Bitrus yaji, Ashe, Ubangiji ne, yayi damara da taguwarsa, (don a tube yake), ya fada a tekun.
And that disciple whom Jesus loved, said to Cephas That is our Lord. And Simon, when he heard that it was our Lord, took his tunic, and girded his loins, (for he had been naked, ) and threw himself into the sea, to go to Jesus.
8 Sauran almajiran kuwa suka zo a cikin karamin jirgi, (domin basu da nisa da kasa, kamar kamu dari biyu zuwa sama), janye da tarun cike da kifi.
But the other disciples came in the ship, (for they were not very far from the land, only about two hundred cubits, ) and they dragged the net with the fishes.
9 Da isowarsu gaci, sai suka ga garwashin wuta a wurin da kifi akai, da kuma gurasa.
And when they came upon the land, they saw coals placed, and fish laid on them, and bread.
10 Yesu ya ce masu “Ku kawo wandansu daga cikin kifin da kuka kama yanzu”.
And Jesus said to them: Bring some of the fishes, which ye have just caught.
11 Sai Saminu Bitrus ya hau, ya jawo tarun gaci, cike da manyan kifaye dari da hamsin da uku. Amma duk da yawansu, tarun bai tsage ba.
And Simon Cephas embarked, and drew the net to land, full of huge fishes, one hundred and fifty and three. And with all this weight, the net was not rent.
12 Yesu yace masu, “Ku zo ku karya kumallo”. Daga cikin almajiran kuwa babu wanda yayi karfin halin tambayarsa “Ko shi wanene?” Domin sunsani Ubangiji ne.
And Jesus said to them: Come and dine. And no one of the disciples presumed to ask him, who he was; for they knew that it was our Lord.
13 Yesu zo ya dauki gurasar ya ba su, haka kuma kifin.
And Jesus came, and took bread and fishes, and gave to his disciples.
14 Wannan shine karo na uku da Yesu ya bayyana ga almajiransa bayan tashinsa daga matattu.
This is the third time that Jesus appeared to his disciples when he had arisen from the dead.
15 Da suka karya kumallon, Yesu yace wa Saminu Bitrus, “Bitrus dan Yahaya, kana kaunata fiye da wadannan?” Bitrus yace masa “I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka” Yesu yace masa “Ka ciyar da 'ya'yan tumakina”.
And when they had dined, Jesus said to Simon Cephas: Simon, son of Jonas, lovest thou me, more than these do? He said to him: Yes, my Lord: thou knowest that I love thee. Jesus said to him: Feed my lambs for me.
16 Ya sake fada masa karo na biyu, “Saminu Dan Yahaya, kana kaunata?” Bitrus Yace masa “I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka”. Yesu yace masa, “Ka lura da Tumakina”.
Again, he said to him the second time: Simon, son of Jonas, lovest thou me? He said to him: Yes, my Lord; thou knowest that I love thee. Jesus said to him: Feed my sheep for me.
17 Ya sake fada masa, karo na uku, “Bitrus Dan Yahaya, kana kaunata? Sai Bitrus bai ji dadi ba domin Yesu ya fada masa karo na uku, “Kana kaunata” Yace masa, “Ubangiji ka san komai duka, ka sani ina kaunarka.” Yesu yace masa “Ka ciyar da tumaki na.
Again, Jesus said to him the third time: Simon, son of Jonas, lovest thou me? And it grieved Cephas, that he said to him the third time, Lovest thou me; and he said to him: My Lord, thou understandest all things, thou knowest that I love thee. Jesus said to him: Feed my sheep for me.
18 Hakika, hakika, Ina gaya maka, lokacin da kake kuruciyarka, kakan yi wa kanka damara, ka tafi inda ka ga dama. amma in ka tsufa, zaka mike hannuwanka wani yayi maka damara, ya kai ka inda baka nufa ba.”
Verily, verily, I say to thee: When thou wast young, thou girdedst thy own loins, and walkedst whither it pleased thee: but when thou shalt be old, thou wilt extend thy hands, and another will gird thy loins for thee, and will conduct thee whither thou wouldst not.
19 To Yesu ya fadi haka ne domin ya nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi ga daukakar Allah. Bayan ya fadi haka, sai yace wa Bitrus, ka biyo ni.
And this he said, to show by what death he was to glorify God. And having said these things, he said to him: Follow me.
20 Bitrus ya juya sai ya ga almajirin da Yesu yake kauna yana biye dasu; wanda ya jingina a kirgin Yesu lokacin cin jibin nan da yace “Ya Ubangiji, wanene zai bashe ka?”
And Simon turned himself, and saw coming after him, that disciple whom Jesus loved, who fell on the breast of Jesus at the supper, and said, My Lord, who is it will betray thee?
21 Da Bitrus ya gan shi, yace wa Yesu “Ya Ubangiji, Me mutumin nan zai yi?”
Him Cephas saw, and said to Jesus: My Lord, as for this man, what?
22 Yesu yace masa, “Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka? Ka biyo ni.”
Jesus said to him: If I will, that he abide here until I come, what is that to thee? Follow thou me.
23 Wannan zance ya yadu cikin 'yan'uwa cewa, wannan almajirin ba zai mutu ba. Alhali Yesu bai cewa Bitrus, wannan almajirin ba zai mutu ba, Amma “Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka?”
And this saying went forth among the brethren, that this disciple would not die. Yet Jesus did not say, that he would not die; but, If I will that he abide here until I come, what is that to thee.
24 Wannan shine almajirin da yake shaida wadannan abubuwa, wanda ya rubuta su, kuma mun tabbata shaidarsa gaskiya ne.
This is the disciple who hath testified of all these things, and hath written them: and we know, that his testimony is true.
25 Akwai kuma sauran abubuwa da yawa wanda Yesu yayi. Idan da an rubuta kowannensu daya bayan daya, ina gaya maku, ko duniya bazata iya daukar litattafan da za a rubuta ba.
And there are also many other things, which Jesus did; which, if written out with particularity, the world itself, as I suppose, would not suffice for the books that would be written. Completion of the Holy Gospel, the announcement of John the Evangelist; which he uttered, in Greek, at Ephesus.

< Yohanna 21 >