< Yohanna 20 >
1 To da sassafe ranar farko ta mako, da sauran duhu, Maryamu Magadaliya ta zo kabarin, ta tarar an kawar da dutsen daga kabarin.
Then on the first Sabbath, Mary Magdalene went to the tomb early, while it was still dark, and she saw that the stone had been rolled away from the tomb.
2 Sai ta ruga da gudu zuwa wurin Saminu Bitrus tare da almajirin nan da Yesu ke kauna, tace masu, “Sun dauke Ubangiji daga kabarin, bamu kuwa san inda aka sa shi ba.”
Therefore, she ran and went to Simon Peter, and to the other disciple, whom Jesus loved, and she said to them, “They have taken the Lord away from the tomb, and we do not know where they have laid him.”
3 Sai Bitrus tare da almajirin nan suka fita, kuma suka tafi kabarin,
Therefore, Peter departed with the other disciple, and they went to the tomb.
4 dukansu suka ruga da gudu tare, amma daya almajirin ya riga Bitrus isowa kabarin,
Now they both ran together, but the other disciple ran more quickly, ahead of Peter, and so he arrived at the tomb first.
5 Sai ya sunkuya ya leka ciki, ya ga likkafanin lillin a wurin, amma fa bai shiga ciki ba.
And when he bowed down, he saw the linen cloths lying there, but he did not yet enter.
6 Sai Saminu Bitrus ya iso daga bayansa sai ya shiga kabarin, ya tarar da likkafanin lillin a ajiye.
Then Simon Peter arrived, following him, and he entered the tomb, and he saw the linen cloths lying there,
7 sai fallen kuma da yake kansa. Ba'a ajiye tare da likkafanin ba amma aka linkeshi aka ajiye shi daban.
and the separate cloth which had been over his head, not placed with the linen cloths, but in a separate place, wrapped up by itself.
8 Sai almajirin nan da ya riga isa kabarin shi ma ya shiga ya gani, sai ya ba da gaskiya.
Then the other disciple, who had arrived first at the tomb, also entered. And he saw and believed.
9 Har ya zuwa wannan lokacin basu san nassin daya ce zai tashi daga matattu ba.
For as yet they did not understand the Scripture, that it was necessary for him to rise again from the dead.
10 Sai almajiran suka sake komawa gida kuma.
Then the disciples went away again, each by himself.
11 Amma Maryamu tana tsaye a bakin kabarin tana kuka. Yayin da take kuka, sai ta sunkuya ta leka cikin kabarin.
But Mary was standing outside the tomb, weeping. Then, while she was weeping, she bowed down and gazed into the tomb.
12 Sai ta ga mala'iku guda biyu cikin fararen kaya zaune, daya ta wurin kai daya kuma ta wurin kafafu inda aka kwantar da Yesu.
And she saw two Angels in white, sitting where the body of Jesus had been placed, one at the head, and one at the feet.
13 Sukace mata, “Uwargida don me kike kuka? Sai tace masu, “Domin sun dauke Ubangijina, ban kuwa san inda suka ajiye shi ba.
They said to her, “Woman, why are you weeping?” She said to them, “Because they have taken away my Lord, and I do not know where they have placed him.”
14 Bayan ta fadi haka, ta juya sai ta ga Yesu tsaye a wurin. Amma bata san cewa Yesu bane,
When she had said this, she turned around and saw Jesus standing there, but she did not know that it was Jesus.
15 Yesu yace mata, “Uwargida, me yasa kike kuka? Wa kuma kike nema? Domin tana zaton shine mai kula da lambun, sai tace masa, “Maigida in kaine ka dauke shi, gaya mani inda ka sa shi, ni kuwa in dauke shi.”
Jesus said to her: “Woman, why are you weeping? Who are you seeking?” Considering that it was the gardener, she said to him, “Sir, if you have moved him, tell me where you have placed him, and I will take him away.”
16 Yesu yace mata, “Maryamu”. Sai ta juya, tace masa da Armaniyanci “Rabboni!” wato mallam.
Jesus said to her, “Mary!” And turning, she said to him, “Rabboni!” (which means, Teacher).
17 Yesu yace mata, kada ki taba ni, domin har yanzu ban hau wurin Uba ba tukuna, amma kije wurin 'yan'uwana kice masu, zan je wurin Ubana da Ubanku, Allahna da kuma Allahnku”.
Jesus said to her: “Do not touch me. For I have not yet ascended to my Father. But go to my brothers and tell them: ‘I am ascending to my Father and to your Father, to my God and to your God.’”
18 Maryamu Magadaliya ta je tace wa almajiran, “Na ga Ubangiji” Ta kuma ce ya fada mata wadannan abubuwa.
Mary Magdalene went, announcing to the disciples, “I have seen the Lord, and these are the things that he said to me.”
19 Da yamma a wannan rana, a rana ta farko ta mako, almajiran suna kulle a daki saboda tsoron Yahudawa, Yesu yazo ya tsaya a tsakaninsu, yace “Salama Agareku”.
Then, when it was late on the same day, on the first of the Sabbaths, and the doors were closed where the disciples were gathered, for fear of the Jews, Jesus came and stood in their midst, and he said to them: “Peace to you.”
20 Bayan ya fadi haka, sai ya nuna masu hannuwansa da kuibinsa. Da almajiran suka ga Ubangiji, sai suka yi farin ciki.
And when he had said this, he showed them his hands and side. And the disciples were gladdened when they saw the Lord.
21 Yesu ya sake ce masu, “salama agareku. “Kamar yadda Uba ya aiko ni, haka Ni ma na aike ku”.
Therefore, he said to them again: “Peace to you. As the Father has sent me, so I send you.”
22 Da Yesu ya fadi haka, sai ya hura masu lumfashinsa, yace masu, “Ku karbi Ruhu Mai Tsarki.
When he had said this, he breathed on them. And he said to them: “Receive the Holy Spirit.
23 Duk wanda kuka gafarta wa zunubai, an gafarta masa; kowa kuka rike zunubansa, an rikesu.”
Those whose sins you shall forgive, they are forgiven them, and those whose sins you shall retain, they are retained.”
24 Toma, daya daga cikin sha biyun, wanda ake kira Dan Tagwai, baya tare dasu lokacin da Yesu ya bayyana.
Now Thomas, one of the twelve, who is called the Twin, was not with them when Jesus arrived.
25 Sauran almajiran sukace masa “Mun ga Ubangiji”. Sai yace masu, “In ban ga gurbin kusoshi a hannuwansa ba, in sa yatsana a gurbin kusoshin ba, in kuma sa hannuna cikin kuibinsa ba, ba zan bada gaskiya ba.
Therefore, the other disciples said to him, “We have seen the Lord.” But he said to them, “Unless I will see in his hands the mark of the nails and place my finger into the place of the nails, and place my hand into his side, I will not believe.”
26 Bayan kwana takwas har wa yau almajiran na cikin gida, Toma ma na tare dasu, kofofin suna kulle, sai ga Yesu a tsakaninsu yace, “Salama agareku”.
And after eight days, again his disciples were within, and Thomas was with them. Jesus arrived, though the doors had been closed, and he stood in their midst and said, “Peace to you.”
27 Sa'an nan yace wa Toma, “Iso nan da yatsanka, dubi hannuwana. Miko hannunka kuma kasa a kuibina, kada ka zama marar bada gaskiya, sai dai, mai bada gaskiya”.
Next, he said to Thomas: “Look at my hands, and place your finger here; and bring your hand close, and place it at my side. And do not choose to be unbelieving, but faithful.”
28 Toma ya amsa yace “Ya Ubangijina da Allahna!”
Thomas responded and said to him, “My Lord and my God.”
29 Yesu yace masa, “Wato saboda ka gan ni, ka bada gaskiya? Albarka ta tabbata ga wadanda basu gani ba, amma kuwa sun bada gaskiya.
Jesus said to him: “You have seen me, Thomas, so you have believed. Blessed are those who have not seen and yet have believed.”
30 Yesu yayi wadansu alamu da yawa dabam dabam a gaban almajiransa, wadanda ba'a rubuta a littafin nan ba.
Jesus also accomplished many other signs in the sight of his disciples. These have not been written in this book.
31 Amma an rubuta wadannan ne, domin ku bada gaskiya Yesu shine Almasihu, Dan Allah, ta wurin gaskatawa kuma ku sami rai cikin sunansa.
But these things have been written, so that you may believe that Jesus is the Christ, the Son of God, and so that, in believing, you may have life in his name.