< Yohanna 19 >
1 Sai Bilatus yayi wa Yesu bulala.
After that Pilate took Jesus and had him scourged;
2 Sojojin kuwa suka saka rawanin kaya. Suka kuwa dora wa Yesu a kai suka sa mashi kaya irin na saurata.
and the soldiers plaited a crown of thorns, placed it on his head, and threw a purple cloak about him, and kept marching up to him,
3 Suka zo wurin sa sukace, “Ranka ya dade, sarkin Yahudawa! sai suka nushe shi.
saying, "Hail! King of the Jews!" They also gave him blow after blow with their hands.
4 Sai Bilatus ya sake fita waje yace masu, “Dubi, zan kawo maku mutumin domin ku sani ban same shi da wani laifi ba”,
Pilate again came forth and said to the people, "See, I am going to bring his out to you, that you may clearly know that I find no crime in him,"
5 Yesu kuwa ya fito, da rawanin kaya da kaya irin na sarauta. Sai Bilatus yace “Ga mutumin nan”.
Then as Jesus came out, wearing the crown of thorns and the purple robe, Pilate said to them, "BEHOLD, THE MAN!"
6 Da manyan firistocin tare da yan majalisar suka ga Yesu, sai suka yi ta ihu suna cewa “A gicciye shi, A gicciye shi” Sai Bilatus yace masu, “ku dauke shi ku gicciye shi, ni kam ban same shi da wani laifi ba”.
So when the chief priests and the police saw him, they shouted. "Crucify him! Crucify him!" "Take him yourselves and crucify him," said Pilate, "for I find no crime in him."
7 Sai Yahudawan sukace mashi, “Ai muna da shari'a, kuma bisa ga shari'ar ya cancanci mutuwa domin ya mai da kansa Dan Allah”.
The Jews answered him, "We have a law, and by that law he ought to die, because he made himself out to be God’s Son,"
8 Da Bilatus ya ji wannan zance sai ya tsorata kwarai.
Now when Pilate heard these words he was more alarmed than ever,
9 Sai ya sake shiga fadar Gwamna, yace wa Yesu, “Daga ina ka fito?” amma Yesu bai amsa mashi ba.
and entering the Praetorium again, he said to Jesus, "What is your origin?"
10 Sai Bilatus yace masa “Ba zaka yi mani magana ba? Baka san ina da iko in sake ka ba, kuma in gicciye ka?
Jesus made no answer. So Pilate said to him. "Do you not speak to me? Do you not know that I have power to release you, or power to crucify you?"
11 Yesu ya amsa masa, “Ai ba ka da iko a kaina sai dai in an baka daga sama, Saboda haka, wanda ya mika ni a gare ka shine mafi zunubi”.
"You would have no power over me," answered Jesus, "unless it had been given you from above. For this reason he who has betrayed me to you has the greater sin."
12 Da jin haka, sai Bilatus yayi kokari a sake shi, amma sai Yahudawa suka tada murya sukace, “In ka saki mutumin nan, kai ba abokin Kaisar bane, duk wanda ya maida kansa sarki, ya sabawa Kaisar”.
After that Pilate began to seek to release him, but the Jews shouted out. "If you release this man you are no friend of the Emperor. Any man who makes himself out to be king is a rebel against the Emperor."
13 Da Bilatus ya ji irin maganganunsu sai ya fito da Yesu waje ya kuma zauna akan kujeransa a inda ake kira “Dakalin shari'a,” a Yahudanci kuma, “Gabbata.”
On hearing what they said, Pilate brought Jesus out and made him sit on the judge’s seat in a place called the Mosaic Pavement (the Hebrew name is Gabbatha).
14 To a ran nan ana shirye shiryen idin ketarewa, da misalin sa'a ta shidda kenan, wato tsakar rana, Bilatus yace wa Yahudawan “Ga sarkin ku!”
And it was the day of Preparation for the Passover, about six o’clock in the morning. Then he said to the Jews, "Behold your King!"
15 Su kuwa suka yi ihu, a tafi da shi, a tafi da shi, a gicciye shi, Bilatus yace masu “In gicciye sarkin ku? Sai manyan firistocin sukace “Ba mu da wani sarki sai Kaisar”.
Then they shouted. "Away with him! Away with him! Crucify him!" "Crucify your King?" said Pilate. The chief priests answered, "We have no king but Caesar!"
16 Sai Bilatus ya mika Yesu domin su gicciye shi.
So then he gave him over to them to be crucified.
17 Sai suka tafi da Yesu, ya fito yana dauke da gicciyen zuwa wurin da ake kira “Wurin kwalluwa” da Yahudanci kuma “Golgota”.
So they took Jesus, who went forth bearing his own cross, to a place called The Place of a Skull - in the Hebrew tongue, Golgotha.
18 Suka gicciye Yesu a wurin, tare da wasu mutum biyu, daya a kowane gefe, Yesu kuwa na tsikiya.
There they crucified him; and with him two others, one on either side, and Jesus between them.
19 Bilatus kuwa ya rubuta wata alama a kan gicciyen, “YESU BANAZARE, SARKIN YAHUDAWA”.
And Pilate moreover wrote an inscription and placed it above the cross. What he wrote was, "JESUS, THE NAZARENE, KING OF THE JEWS"
20 Yahudawa da yawa kuwa suka karanta wannan alama domin wurin da aka gicciye Yesu yana kusa da Birnin. Alamar kuwa an rubuta ta da Yahudanci, da Romanci, da Helenanci.
This inscription was read by many of the Jews, because the place where they crucified Jesus was near the city, and the inscription was written in Hebrew, Latin, and Greek.
21 Sai manyan firistocin yahudawa sukace wa Bilatus, kada ka rubuta sarkin Yahudawa, amma kace, 'wannan yace “Ni ne sarkin Yahudawa”'.
So the high priests of the Jews said to Pilate, "Do not write ‘King of the Jews,’ but ‘He said, I am King of the Jews.’"
22 Bilatus kuwa ya amsa, “Abinda na rubuta na rubuta kenan.”
Pilate answered, "What I have written, I have written!"
23 Bayan da sojojin suka gicciye Yesu, sai suka yayyaga rigarsa kashi hudu, kowane soja da nasa, kashin, sai kuma alkyabbar. Alkyabbar kuwa bata da dinki an saka tane daga sama har kasa.
After the soldiers had crucified Jesus, they took his garments and divided them into four parts, to each soldier a part, and the tunic. Now the tunic was seamless, woven in one piece from top to bottom;
24 Sai sukace wa junansu, “Kada mu yaga alkyabbar, amma kuzo mu jefa kuri'a a kan ta mu gani ko wanene zai dauke ta, anyi haka ne domin a cika nassi cewa “Sun raba rigata a tsakaninsu, sun kuwa jefa kuri'a domin alkyabbata.
so the soldiers said one to another. "Let us not tear it. Let us draw lots, to see whose it shall be" - that the Scripture might be fulfilled. They divided my garments among them, For my raiment did they cast lots. This was what the soldiers did.
25 Sojojin suka yi wadannan abubuwa. Uwar Yesu, da 'yar'uwarta, da Maryamu matar Kilofas, da kuma Maryamu Magadaliya. Wadannan mataye suna tsaye kusa da gicciyen Yesu.
Now there stood near the cross of Jesus, his mother and his mother’s sister, Mary the wife of Clopas, and Mary Magdalene.
26 Da Yesu ya ga mahaifiyarsa da almajirin nan da yake kauna tsaye kusa da juna, yace, “Mace, dubi, dan ki!”
When Jesus saw his mother, and standing near her the disciple whom he loved, he said to his mother, "Woman behold your son."
27 Sai yace wa almajirin, “Dubi, mahaifiyarka!” Daga wannan sa'a almajirin ya dauke ta zuwa gidansa.
Then he said to the disciple, "Behold your mother." And from that hour the disciple took her to his home.
28 Bayan wannan Yesu, saboda ya san yanzu komai ya kammala, domin a cika nassin, sai yace “Ina jin kishi.
After that, when Jesus knew that everything was now accomplished, he said in fulfilment of the words of Scripture, "I am thirsty."
29 A gefensu kuma akwai gora cike da ruwan inabi mai tsami, sai suka tsoma soso a cikin ruwan inabin mai tsami suka daura a wata sanda sai suka mika masa a baki.
There was a jar full of vinegar standing there; and they filled a sponge with vinegar, and put it upon a stalk of hyssop, and put it to his lips.
30 Da Yesu ya tsotsi ruwan tsamin, sai yace “An gama” Sai ya sunkuyar da kansa ya kuwa saki ruhunsa.
Then after he had taken the vinegar, Jesus said, "IT IS FINISHED!" And bowing his head, he yielded up his spirit.
31 Sai Yahudawan, domin ranar shirye shirye ne, domin kada a bar jikunansu akan gicciye har ranar asabacin (domin asabacin rana ce mai muhimmanci), suka roki Bilatus ya kakkarye kafafunsu kuma ya saukar da su.
It was Preparation Day, so in order to prevent the bodies’ hanging on the cross during the Sabbath (for the Sabbath was a great day) the Jews begged Pilate to have the legs broken, and the bodies taken away.
32 Sai sojojin suka zo suka karya kafafun mutum na farko da kuma mutum na biyun wadanda aka gicciye tare da Yesu.
So the soldiers came and broke the legs of the first man and of the other who had been crucified with him.
33 Da suka iso kan Yesu sai suka tarar ya riga ya mutu, sai basu kuwa karya kafafunsa ba.
But upon coming to Jesus they saw that he was already dead, and did not break his legs.
34 Duk da haka daya daga cikin sojojin ya soki kuibin shi da mashi, nan da nan sai jini da ruwa suka fito.
One of the soldiers, however, pierced his side with a lance, and immediately blood and water flowed out.
35 Wanda ya ga wannan, shi ya zama shaida, shaidarsa kuwa gaskiya ce. Ya sani cewa abinda ya fada gaskiya ne saboda ku ma ku gaskata.
And he who saw it has borne testimony, and his testimony is trustworthy, and he knows that he is telling the truth in order that you may believe.
36 Wadannan sun faru ne domin a cika nassi, “Babu ko daya daga cikin kasusuwansa da za'a karya”.
For this happened that the Scripture might be fulfilled, Not one of his bones shall be broken.
37 Kuma wani nassin yace, “Zasu dube shi wanda suka soka.”
And again another Scripture says, They shall look on him whom they have pierced.
38 Bayan wadannan abubuwa, Yusufu mutumin Arimatiya, wanda yake almajirin Yesu ne (amma a boye saboda tsoron Yahudawa) ya roki Bilatus izini domin ya dauke jikin Yesu. Bilatus kuwa ya bashi izini, sai Yusufu yazo ya dauki jikin.
After these things Joseph of Arimathea, who was a disciple of Jesus, but in secret because of fear of the Jews, asked Pilate for permission to take the body of Jesus, and Pilate gave him leave. So he came and took the body.
39 Nikodimu ma ya zo, wanda da farko ya zo wurin Yesu da daddare, ya kawo hadin man kamshi na mur da al'ul wajen nauyin awo dari.
Nicodemus also (the one who visited Jesus by night, at first) came bringing a mixture of myrrh and aloes, weighing nearly a hundred pounds.
40 Sai suka dauki jikin Yesu suka sa shi a likkafanin lillin tare da kayan kamshin nan, domin jana'iza bisa ga al'adar Yahudawa.
So they took the body of Jesus and wound it in linen with the spices, according to the Jewish mode of burial.
41 To a wurin da aka gicciye shi kuwa akwai wani lambu, a cikin lambun kuma akwai sabon kabari wanda ba'a taba sa kowa ba.
There was a garden near the place where Jesus had been crucified, and in the garden a new tomb in which no one had ever been laid.
42 Da yake ranar shirye shirye ce ta Yahudawa, kabarin kuwa na kusa, sai suka sa Yesu a ciki.
Here, because of its being Preparation Day, and as the tomb was near by, they placed Jesus.