< Yohanna 18 >
1 Bayan Yesu ya fadi wadannan maganganu, ya fita shi da almajiransa zuwa daya barayin kwarin Kidiron, inda wani lambu ya ke, ya kuma shiga da almajiransa.
Ayant dit ces choses, Jésus s’en alla avec ses disciples au-delà du torrent du Cédron, où était un jardin, dans lequel il entra, lui et ses disciples.
2 Yahuza ma wanda zai bashe shi ya san wurin, domin Yesu ya saba zuwa wurin da almajiransa.
Et Judas aussi, qui le livrait, connaissait le lieu; car Jésus s’y était souvent assemblé avec ses disciples.
3 Yahuza kuwa, bayan ya dauko kungiyar soja daga manyan firistoci, da Farisawa, da 'yan majalisa, suka zo wurin, rike da fitilu, da cociloli, da makamai.
Judas donc, ayant pris la compagnie [de soldats], et des huissiers, de la part des principaux sacrificateurs et des pharisiens, vient là, avec des lanternes et des flambeaux et des armes.
4 Sai Yesu, da ya san duk abinda ke faruwa da shi, yayiwo gaba, yace masu, ''Wa kuke nema''
Jésus donc, sachant toutes les choses qui devaient lui arriver, s’avança et leur dit: Qui cherchez-vous?
5 Suka amsa masa su ka ce, ''Yesu Banazare'' Yesu yace masu, Ni ne'' Yahuza kuma, wanda ya bashe shi, yana tsaye tare da sojojin.
Ils lui répondirent: Jésus le Nazaréen. Jésus leur dit: C’est moi. Et Judas aussi qui le livrait était là avec eux.
6 Sa'adda ya ce masu, ''Ni ne'', suka koma da baya, suka fadi a kasa.
Quand donc il leur dit: C’est moi, ils reculèrent, et tombèrent par terre.
7 Ya sake tambayarsu kuma, ''Wa ku ke nema?'' su ka ce, ''Yesu Banazare.''
Il leur demanda donc de nouveau: Qui cherchez-vous? Et ils dirent: Jésus le Nazaréen.
8 Yesu ya amsa, ''Ai, na gaya maku cewa, Ni ne. In kuwa ni ku ke nema, ku bar wadannan su tafi abinsu;''
Jésus répondit: Je vous ai dit que c’est moi; si donc vous me cherchez, laissez aller ceux-ci,
9 Wannan kuwa domin maganar daya fada ta cika, ''Daga cikin wadanda ka ba ni, ko daya bai bace mani ba.''
– afin que fût accomplie la parole qu’il avait dite: De ceux que tu m’as donnés, je n’en ai perdu aucun.
10 Saminu Bitrus kuwa, da ya ke yana da takobi, ya zaro ya kai wa bawan babban firist sara, ya dauke masa kunnensa na dama, sunan bawan Malkus ne.
Simon Pierre donc, ayant une épée, la tira et frappa l’esclave du souverain sacrificateur et lui coupa l’oreille droite; et le nom de l’esclave était Malchus.
11 Yesu ya ce wa Bitrus, ''Mai da takobin ka kubenta. Ba zan sha kokon da Uba ya ba ni ba.'?
Jésus donc dit à Pierre: Remets l’épée dans le fourreau: la coupe que le Père m’a donnée, ne la boirai-je pas?
12 Sai sojojin da hafsan, da 'yan majalisar Yahudawa, suka kama Yesu, suka daure shi.
La compagnie [de soldats] donc, et le chiliarque, et les huissiers des Juifs, se saisirent de Jésus et le lièrent,
13 Da fari suka tafi da shi wurin Hanana, don shi surukin Kayafa ne, wanda ya ke shi ne babban firist a shekaran nan.
et l’amenèrent premièrement à Anne; car il était beau-père de Caïphe, qui était souverain sacrificateur cette année-là.
14 Kayafa kuma shi ne ya ba Yahudawa shawara, cewa ya fiye masu mutum daya ya mutu domin mutane.
Or Caïphe était celui qui avait donné aux Juifs le conseil, qu’il était avantageux qu’un seul homme périsse pour le peuple.
15 Saminu bitrus ya bi bayan Yesu, haka kuma wani almajirin yayi. Almajirin nan kuwa sananne ne ga babban firist, sai ya shiga har farfajiyar babban firist din tara da Yesu;
Or Simon Pierre suivait Jésus, et l’autre disciple [aussi]; et ce disciple-là était connu du souverain sacrificateur, et il entra avec Jésus dans le palais du souverain sacrificateur;
16 Amma bitrus kuwa ya tsaya a bakin kofa daga waje. Sai daya almajirin da ya ke sananne ga babban firist ya fita, yayi magana da macen da ta ke tsaron kofar, sa'an nan ya shigo da Bitrus.
mais Pierre se tenait dehors à la porte. L’autre disciple donc, qui était connu du souverain sacrificateur, sortit, et parla à la portière, et fit entrer Pierre.
17 Sai yarinyar mai tsaron kofar ta ce wa Bitrus, ''kai ma ba kana cikin almajiran mutumin nan ba?'' Yace ''bani ba.''
La servante qui était portière dit donc à Pierre: Et toi, n’es-tu pas des disciples de cet homme? Lui dit: Je n’en suis point.
18 To, barorin da dogaran Haikali suna tsaye a wurin, sun kuwa hura wutar gawayi, suna jin dumi, gama ana sanyi. Bitrus ma yana tsaye tare da su yana jin dumin.
Or les esclaves et les huissiers, ayant allumé un feu de charbon, se tenaient là, car il faisait froid, et ils se chauffaient; et Pierre était avec eux, se tenant là et se chauffant.
19 babban firist ya tambayi Yesu game da almajiransa da koyarwarsa kuma.
Le souverain sacrificateur donc interrogea Jésus touchant ses disciples et touchant sa doctrine.
20 Yesu ya amsa masa, Ai, na yi wa duniya magana a bayyane. Na kuma sha koyarwa a majami'u da Haikali in da Yahudawa duka sukan taru. Ban fadi komai a boye ba.
Jésus lui répondit: Moi, j’ai ouvertement parlé au monde; j’ai toujours enseigné dans la synagogue, et dans le temple où tous les Juifs s’assemblent, et je n’ai rien dit en secret.
21 Don me kake tambaya ta? Ka tambayi wadanda suka saurare ni a kan abinda na fada, ai, sun san abinda na fada.
Pourquoi m’interroges-tu? Interroge sur ce que je leur ai dit ceux qui m’ont entendu; voilà, ils savent, eux, ce que moi j’ai dit.
22 Sa'adda Yesu ya fadi wannan, wani daga cikin 'yan majalisar da ke tsaye a wurin ya nushi Yesu, yace, ''Kana amsa wa babban firist haka.''
Or comme il disait ces choses, un des huissiers qui se tenait là donna un soufflet à Jésus, disant: Réponds-tu ainsi au souverain sacrificateur?
23 Yesu ya amsa masa yace, ''Idan na fadi mugun abu to, ka bada shaida kan hakan. In kuwa dai dai na fada, to, dan me za ka nushe ni?''
Jésus lui répondit: Si j’ai mal parlé, rends témoignage du mal; mais si j’ai bien parlé, pourquoi me frappes-tu?
24 Sai Hanana ya aika daYesu a daure wurin Kayafa, babban firist.
Anne donc l’avait envoyé lié à Caïphe, le souverain sacrificateur.
25 To Saminu Bitrus yana tsaye yana jin dumin. Mutanen kuwa suka ce masa, ''Anya kai ma ba cikin almajiransa ka ke ba?'' Sai yayi musu yace, ''A'a, ba na ciki.''
Et Simon Pierre se tenait là, et se chauffait; ils lui dirent donc: Et toi, n’es-tu pas de ses disciples? Il le nia, et dit: Je n’en suis point.
26 Sai wani daga cikin bayin babban firist, wato dan'uwan wanda Bitrus ya fillewa kunne, yace, ''Ashe, ban gan ka tare da shi a lambun ba?
L’un d’entre les esclaves du souverain sacrificateur, parent de celui à qui Pierre avait coupé l’oreille, dit: Ne t’ai-je pas vu, moi, dans le jardin avec lui?
27 Bitrus ya sake yin musu, nan da nan kuwa zakara yayi cara.
Pierre donc nia encore; et aussitôt le coq chanta.
28 Daga wurin Kayafa kuma suka kai Yesu fadar Gwamna. Da asuba ne kuwa, su kansu ba su shiga fadar Gwamnan ba, wai don kada su kazantu su kasa cin jibin Ketarewa.
Ils mènent donc Jésus de chez Caïphe au prétoire (or c’était le matin); et eux-mêmes, ils n’entrèrent pas au prétoire, afin qu’ils ne soient pas souillés; mais qu’ils puissent manger la pâque.
29 Sai bilatus fa ya fita zuwa wurinsu, yace, 'Wane zargi ku ke kawowa akan mutumin nan?'
Pilate donc sortit vers eux, et dit: Quelle accusation portez-vous contre cet homme?
30 ''Sai suka amsa suka ce, ''idan da mutumin nan bai yi mugun abu ba, me zai sa mu yi kararsa a wurin ka''
Ils répondirent et lui dirent: Si cet homme n’était pas un malfaiteur, nous ne te l’aurions pas livré.
31 bilatus yace masu, ''Ku tafi da shi da kan ku mana, ku hukunta shi bisa ga shari'arku!'' Sai Yahudawa su kace masa, ''Ai, ba mu da ikon zartar da hukuncin kisa akan kowa.''
Pilate donc leur dit: Prenez-le, vous, et jugez-le selon votre loi. Les Juifs donc lui dirent: Il ne nous est pas permis de faire mourir personne;
32 Sun fadi Wannan ne don a cika maganar da Yesu yayi, wadda ta kwatanta irin mutuwar da zai yi.
afin que fût accomplie la parole que Jésus avait dite, indiquant de quelle mort il devait mourir.
33 Sai bilatus ya sake shiga cikin fadar Gwamnan, ya kira Yesu ya ce masa, ''kai sarkin Yahudawa ne?''
Pilate donc entra encore dans le prétoire, et appela Jésus, et lui dit: Toi, tu es le roi des Juifs?
34 Yesu ya amsa, '' wannan fadarka ce, ko kuwa wadansu ne suka ce da ni haka a wurinka?''
Jésus lui répondit: Dis-tu ceci de toi-même, ou d’autres te l’ont-ils dit de moi?
35 Bilatus ya amsa “Ni ba Bayahude bane, ko kuwa?'' Ai, jama'arka ne da manyan firistoci suka bashe ka gareni. ''Me ka yi?''
Pilate répondit: Suis-je Juif, moi? Ta nation et les principaux sacrificateurs t’ont livré à moi; qu’as-tu fait?
36 Yesu ya amsa, ''Mulkina ba na duniya nan ba ne. Da mulkina na duniyan nan ne da barorina za su yi yaki kada a bashe ni ga Yahudawa. To, mulkina ba daga nan ya ke ba.''
Jésus répondit: Mon royaume n’est pas de ce monde. Si mon royaume était de ce monde, mes serviteurs auraient combattu, afin que je ne sois pas livré aux Juifs; mais maintenant mon royaume n’est pas d’ici.
37 Sai Bilatus yace masa, ''Wato ashe, sarki ne kai?'' Yesu ya amsa, ''Yadda ka fada, ni sarki ne. Domin wannan dalili aka haife ni, domin kuma wannan dalili na zo cikin duniya, don in bada shaida game da gaskiya. Kowane mai kaunar gaskiya kuma yakan saurari muryata.''
Pilate donc lui dit: Tu es donc roi? Jésus répondit: Tu le dis que moi je suis roi. Moi, je suis né pour ceci, et c’est pour ceci que je suis venu dans le monde, afin de rendre témoignage à la vérité. Quiconque est de la vérité, écoute ma voix.
38 Bilatus yace masa, ''Menene gaskiya?'' Bayan da ya fadi haka, ya sake fitowa wurin Yahudawa, yace masu, ''Ni kam, ban sami mutumin nan da wani laifi ba.
Pilate lui dit: Qu’est-ce que la vérité? Et ayant dit cela, il sortit encore vers les Juifs; et il leur dit: Moi, je ne trouve aucun crime en lui;
39 Amma dai kuna da wata al'ada, in Idin Ketarewa ya yi, na kan sakar maku mutum daya. To, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?''
mais vous avez une coutume, que je vous relâche quelqu’un à la Pâque; voulez-vous donc que je vous relâche le roi des Juifs?
40 Sai suka sake daukar kururuwa suna cewa, ''A; a, ba wannan mutum ba, sai dai Barabbas.'' Barabbas din nan kuwa dan fashi ne.
Ils s’écrièrent donc tous encore, disant: Non pas celui-ci, mais Barabbas. Or Barabbas était un brigand.