< Yohanna 17 >
1 Da Yesu ya fadi wandannan abubuwa, sai ya tada idanunsa sama ya ce, ya Uba, sa'a ta zo; ka daukaka Danka, domin Dan shi ya daukaka ka,
When Jesus had thus spoken, He raised his eyes towards Heaven and said, "Father, the hour has come. Glorify Thy Son that the Son may glorify Thee;
2 kamar yadda ka ba shi iko akan dukkan 'yan adam, ya ba da rai madawwami ga duk wanda ka ba shi. (aiōnios )
even as Thou hast given Him authority over all mankind, so that on all whom Thou hast given Him He may bestow the Life of the Ages. (aiōnios )
3 Wannan ne rai madawwami: wato su san ka, Allah makadaici na gaskiya, da shi kuma wanda ka aiko, Yesu Almasihu. (aiōnios )
And in this consists the Life of the Ages--in knowing Thee the only true God and Jesus Christ whom Thou hast sent. (aiōnios )
4 Na daukaka ka a duniya, na gama aikin da ka ba ni in yi.
I have glorified Thee on earth, having done perfectly the work which by Thine appointment has been mine to do.
5 Yanzu, ya Uba, ka daukaka ni tare da kai da daukaka wadda ni ke da ita tare da kai tun kafin duniya ta kasanci.
And now, Father, do Thou glorify me in Thine own presence, with the glory that I had in Thy presence before the world existed.
6 Na bayyana sunanka ga mutunen da ka ba ni acikin duniya. Na ka suke, ka ba ni su, sun kuwa kiyaye maganarka.
"I have revealed Thy perfections to the men whom Thou gavest me out of the world. Thine they were, and Thou gavest them to me, and they have obeyed Thy message.
7 Yanzu kuwa sun san duk iyakar abinda ka ba ni daga gare ka yake,
Now they know that whatever Thou hast given me is from Thee.
8 don kuwa maganganun da ka fada mani. Na fada masu, sun kuma karba, sun sani kuwa hakika na fito daga gareka ne, kuma sun gaskata kai ne ka aiko ni.
For the truths which Thou didst teach me I have taught them. And they have received them, and have known for certain that I came out from Thy presence, and have believed that Thou didst send me.
9 Ina yi masu addu'a. Ba domin duniya ni ke yin addu'a ba, amma domin wadanda ka bani gama na ka ne.
"I am making request for them: for the world I do not make any request, but for those whom Thou hast given me. Because they are Thine,
10 Gama dukan abinda ke nawa na ka ne, naka kuwa nawa ne, an kuma daukaka ni a cikinsu.
and everything that is mine is Thine, and everything that is Thine is mine; and I am crowned with glory in them.
11 Ba na cikin duniya kuma, amma wadannan mutane suna cikin duniya, ni kuwa ina zuwa wurin ka. Ya Uba mai Tsarki, ka adanasu cikin sunanka da ka ba ni domin su zama daya, kamar dai yadda muke daya.
I am now no longer in the world, but they are in the world and I am coming to Thee. "Holy Father, keep them true to Thy name--the name which Thou hast given me to bear--that they may be one, even as we are.
12 Lokacin da ina tare da su, na adanasu acikin sunanka da ka ba ni. Na kiyaye su, kuma ko daya kuwa daga cikinsu ba ya bace ba, sai dai dan hallakar nan, domin Nassi ya cika.
While I was with them, I kept them true to Thy name--the name Thou hast given me to bear--and I kept watch over them, and not one of them is lost but only he who is doomed to destruction--that the Scripture may be fulfilled.
13 Amma yanzu ina zuwa wurinka, Ina fadar wadannan abubuwa tun ina duniya, domin farin cikina ya zama cikakke a zukatansu.
"But now I am coming to Thee, and I speak these words while I am in the world, in order that they may have my gladness within them filling their hearts.
14 Na ba su maganarka, kuma duniya ta tsane su domin su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
I have given them Thy Message, and the world has hated them, because they do not belong to the world, just as I do not belong to the world.
15 Ba ina roko ka dauke su daga cikin duniya ba, amma domin ka tsare su daga mugun nan.
I do not ask that Thou wilt remove them out of the world, but that Thou wilt protect them from the Evil one.
16 Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
They do not belong to the world, just as I do not belong to the world.
17 Ka kebe su domin kanka cikin gaskiya. maganarka gaskiya ce.
Make them holy in the truth: Thy Message is truth.
18 Kamar dai yadda ka aiko ni cikin duniya, haka kuma na aike su cikin duniya.
Just as Thou didst send me into the world, I also have sent them;
19 Na kebe kaina gareka sabili da su, domin su ma kansu a kebe su gareka cikin gaskiya.
and on their behalf I consecrate myself, in order that they may become perfectly consecrated in truth.
20 Ina addu'a ba domin wadannan kadai ba, amma har da wadanda zasu gaskata da ni ta wurin maganarsu,
"Nor is it for them alone that I make request. It is also for those who trust in me through their teaching;
21 Domin su zama daya dukansu, kamar yadda kai, ya Uba, ka ke ciki na, ni kuma na ke cikin ka. Ina roko suma su kasance a cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa ka aiko ni
that they may all be one, even as Thou art in me, O Father, and I am in Thee; that they also may be in us; that the world may believe that Thou didst send me.
22 Daukakar da ka bani, ita nake basu, domin su zama daya, kamar yadda mu ke daya;
And the glory which Thou hast given me I have given them, that they may be one, just as we are one:
23 ni a cikinsu, kai kuma a ciki na. Domin su kammalu cikin zama daya, domin duniya ta sani cewa ka aiko ni, kuma ka kaunace su, kamar yadda ka kaunace ni.
I in them and Thou in me; that they may stand perfected in one; that the world may come to understand that Thou didst send me and hast loved them with the same love as that with which Thou hast loved me.
24 Ya Uba, ina so wadanda ka ba ni, su ma su kasance tare da ni inda nake, domin su dubi daukakata da ka yi mani. Domin ka kaunace ni tun kafin halittar duniya.
"Father, those whom Thou hast given me--I desire that where I am they also may be with me, that they may see the glory--my glory--my gift from Thee, which Thou hast given me because Thou didst love me before the creation of the world.
25 Ya Uba mai adalci, duniya kam, ba ta sanka ba, amma ni na sanka; kuma wadannan sun sani kai ne ka aiko ni.
And, righteous Father, though the world has failed to recognize Thee, I have known Thee, and these have perceived that Thou didst send me.
26 Na sanar masu da sunanka, zan kuma sanar da shi domin kaunar da ka yi mani ta kasance a cikinsu, ni kuma in kasance a cikinsu,
And I have made known Thy name to them and will make it known, that the love with which Thou hast loved me may be in them, and that I may be in them."