< Yohanna 17 >
1 Da Yesu ya fadi wandannan abubuwa, sai ya tada idanunsa sama ya ce, ya Uba, sa'a ta zo; ka daukaka Danka, domin Dan shi ya daukaka ka,
Jesus spoke these things, raising His eyes to Heaven and saying: “Father, the hour has come! Glorify Your Son, so that Your Son also may glorify You,
2 kamar yadda ka ba shi iko akan dukkan 'yan adam, ya ba da rai madawwami ga duk wanda ka ba shi. (aiōnios )
just as You gave Him authority over all humanity, so that He will give eternal life to all those whom You have given Him. (aiōnios )
3 Wannan ne rai madawwami: wato su san ka, Allah makadaici na gaskiya, da shi kuma wanda ka aiko, Yesu Almasihu. (aiōnios )
Now eternal life is this: that they may know You, the only true God, and the One whom You sent—Jesus Christ. (aiōnios )
4 Na daukaka ka a duniya, na gama aikin da ka ba ni in yi.
I have glorified You on the earth. I have finished the work that You have given me to do.
5 Yanzu, ya Uba, ka daukaka ni tare da kai da daukaka wadda ni ke da ita tare da kai tun kafin duniya ta kasanci.
So now, Father, You glorify me by Your side with the glory that I had along with You before the world existed!
6 Na bayyana sunanka ga mutunen da ka ba ni acikin duniya. Na ka suke, ka ba ni su, sun kuwa kiyaye maganarka.
“I have revealed Your name to the men whom You have given me out of the world. They were Yours and You gave them to me, and they have kept Your word.
7 Yanzu kuwa sun san duk iyakar abinda ka ba ni daga gare ka yake,
They now know that everything You have given to me is from You;
8 don kuwa maganganun da ka fada mani. Na fada masu, sun kuma karba, sun sani kuwa hakika na fito daga gareka ne, kuma sun gaskata kai ne ka aiko ni.
because I have given them the sayings which You have given to me; and they have received and known for sure that I came forth from You, and they have believed that You sent me.
9 Ina yi masu addu'a. Ba domin duniya ni ke yin addu'a ba, amma domin wadanda ka bani gama na ka ne.
I am praying for them; I am not praying for the world but for those whom You have given me, because they are yours.
10 Gama dukan abinda ke nawa na ka ne, naka kuwa nawa ne, an kuma daukaka ni a cikinsu.
Actually, all my things are Yours and Yours are mine, and I have been glorified in them.
11 Ba na cikin duniya kuma, amma wadannan mutane suna cikin duniya, ni kuwa ina zuwa wurin ka. Ya Uba mai Tsarki, ka adanasu cikin sunanka da ka ba ni domin su zama daya, kamar dai yadda muke daya.
Now I am no longer in the world, yet these are in the world, and I am coming to You. “Holy Father, keep them in Your name which You have given to me, so that they may be one just as we are.
12 Lokacin da ina tare da su, na adanasu acikin sunanka da ka ba ni. Na kiyaye su, kuma ko daya kuwa daga cikinsu ba ya bace ba, sai dai dan hallakar nan, domin Nassi ya cika.
While I was with them in the world I kept them in Your name. I protected those whom You gave me, and not one of them was lost except the son of perdition, so that the Scripture might be fulfilled.
13 Amma yanzu ina zuwa wurinka, Ina fadar wadannan abubuwa tun ina duniya, domin farin cikina ya zama cikakke a zukatansu.
But now I am coming to You, and I speak these things in the world so that they may have my joy made full in them.
14 Na ba su maganarka, kuma duniya ta tsane su domin su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
“I have given them Your word; and the world has hated them because they are not of the world, just as I am not of the world.
15 Ba ina roko ka dauke su daga cikin duniya ba, amma domin ka tsare su daga mugun nan.
I am not asking that You take them out of the world, but that You keep them from the malignant one.
16 Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
They are not of the world, just as I am not of the world.
17 Ka kebe su domin kanka cikin gaskiya. maganarka gaskiya ce.
Sanctify them by Your Truth; Your Word is Truth.
18 Kamar dai yadda ka aiko ni cikin duniya, haka kuma na aike su cikin duniya.
Just as You sent me into the world, I also have sent them into the world.
19 Na kebe kaina gareka sabili da su, domin su ma kansu a kebe su gareka cikin gaskiya.
And for their sakes I sanctify myself, so that they also may be sanctified in truth.
20 Ina addu'a ba domin wadannan kadai ba, amma har da wadanda zasu gaskata da ni ta wurin maganarsu,
“I pray not only for these, but also for those who believe into me through their word;
21 Domin su zama daya dukansu, kamar yadda kai, ya Uba, ka ke ciki na, ni kuma na ke cikin ka. Ina roko suma su kasance a cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa ka aiko ni
that they all may be one, just as You, Father, are in me and I in You; that in Us they also may be one, so that the world may believe that You sent me.
22 Daukakar da ka bani, ita nake basu, domin su zama daya, kamar yadda mu ke daya;
In fact, the glory that You gave to me I have given to them, so that they may be one just as We are one:
23 ni a cikinsu, kai kuma a ciki na. Domin su kammalu cikin zama daya, domin duniya ta sani cewa ka aiko ni, kuma ka kaunace su, kamar yadda ka kaunace ni.
I in them and You in me, so that they may be perfected into one; also so that the world may know that You sent me, and have loved them just as You have loved me.
24 Ya Uba, ina so wadanda ka ba ni, su ma su kasance tare da ni inda nake, domin su dubi daukakata da ka yi mani. Domin ka kaunace ni tun kafin halittar duniya.
“Father, those whom You have given to me, I desire that they also may be with me where I am, so that they may observe my glory, which You have given me, because You loved me before the founding of the world.
25 Ya Uba mai adalci, duniya kam, ba ta sanka ba, amma ni na sanka; kuma wadannan sun sani kai ne ka aiko ni.
Righteous Father! Indeed the world has not known You, but I have known You; and these have known that You sent me.
26 Na sanar masu da sunanka, zan kuma sanar da shi domin kaunar da ka yi mani ta kasance a cikinsu, ni kuma in kasance a cikinsu,
Yes, I have made Your name known to them and will make it known, so that the love with which You have loved me may be in them, and I in them.”