< Yohanna 16 >

1 “Na fada maku wannan ne domin kada kuyi tuntube.
Nibhajobhili mambo agha ili msibhwesi kukwazibhwa.
2 Zasu fitar da ku daga majami'u. Amma, sa'a tana zuwa, wadda idan wani ya kasheku, zai yi zaton aikin Allah yake yi.
Bhibeta kubhapisya kwibhala mu masinagogi; hakika saa jhihida ambajho khila jha ibetakubhakhoma ibetakufikiri ibhomba mbombo jhinofu kwa ndabah jha K'yara.
3 Za suyi haka ne kuwa domin ba su san Uban ko ni ba.
Bhibetakubhabhombela mambo agha kwa ndabha bhammanyilepi Dadi wala bhanimanyilepi nene.
4 Na fada maku wadannan abubuwa ne domin in lokacin da zasu faru yayi, ku tuna na fada maku.” Ban fada maku wadannan abubuwa ba tun da farko, domin ina tare da ku.
Nibhajobhili mambo agha ili kwamba wakati ukafikayi ghwa agha kutokela, mwibhwesya kughakhomboka na jinsi kyanibhajobhili mubhwesiajhi bhene. Nabhajobhilepi kuhusu mambo agha kuh'omela kubhwandelu kwa ndabha najhele pamonga namu.
5 Yanzu kuwa za ni wurin wanda ya aiko ni, duk da haka a cikinku, ba wanda ya tambaye ni, 'Ina za ka?'
Japokujha, henu nilota kwa jhola jhaanilaghisi; lakini ajhelepi kati jha muenga jha akanikota, “Wilotandakhu?”
6 Amma saboda na fada maku wadannan abubuwa, bakin ciki ya cika zuciyarku.
Kwa ndabha nijobhili malobhi agha kwa muenga, huzuni imemili mu mioyo jha jhomu.
7 Amma ina gaya maku gaskiya: zai fi ye maku in na tafi. Domin in ban tafi ba, Mai Ta'aziyya ba zai zo gare ku ba, in kuwa na tafi, zan aiko shi gare ku.
Hata naha, nikabhajobhela ukweli: ni vyema kwa muenga nikabhokayi; kwa ndabha nikabelakubhoka, mfariji ibetalepi kuhida kwa muenga; lakini nikalotayi nibetakundaghisya kwa muenga.
8 Idan kuwa ya zo, Mai Ta'aziyyar zai fadarkar da duniya a kan zunubi, da adalci, da kuma hukunci.
Akahidayi, mfariji ojhu ibetakuubitisha ulimwengu kuhusiana ni dhambi, kuhusiana ni haki na kuhusiana ni hukumu.
9 Game da zunubi, domin basu gaskata da ni ba,
Kuhusiana ni dhambi, kwa ndabha bhabelikunikiera nene,
10 Game da adalci, domin za ni wurin Uba, kuma ba za ku sake ganina ba,
kuhusiana ni haki, kwa ndabha nilota kwa dadi, na mwibetalepi kunibhona kabhele'
11 game da hukunci kuma, domin an yanke wa mai mulki duniyan nan hukunci.
ni kuhusiana ni hukumu kwa ndabha mbaha ghwa ulimwengu obho ahukumibhu.
12 “Akwai abubuwa da yawa da zan gaya maku, amma ba za ku iya fahimta a yanzu ba.
Nijhenaku mingi gha kubhajobhela, lakini mwibetalepi kughatekelesya henu.
13 Saboda haka, sa'adda Ruhu na gaskiya ya zo, zai bishe ku a cikin dukan gaskiyar, domin ba zai yi magana don kansa ba, sai dai duk abin da ya ji, shi zai fada, zai kuma sanar da ku al'amuran da zasu faru.
Lakini, muene, Roho ghwa kweli, akahidayi, ibetakubhalongosya mu bhukweli ghoha; kwa kujha ibetalepi kulongela kwa ndabha jha muene; lakini ghoha ghaibetakughap'eleka, ibetakughajobha mambo aghu; na ibetakughadhihirisha kwa jhomu mambo agha ghaghibetakuhida.
14 Zai daukaka ni, domin zai dauko abubuwa dake nawa ya sanar da ku.
Muene jha ibetakunitukusya nene, kwa ndabha ibetakughatola mambo ghangu ni kughatangasya kwa muenga.
15 Duk abinda Uba yake da shi, nawa ne. Domin wannan ne nace zai dauko abubuwa da yake nawa ya sanar da ku.
Fenu fyoha fya ajhenafu Dadi ndo fya nene; henu, nijobhili kujha Roho ibetakutola mambo ghangu ni kughadhihirisha kwa muenga.
16 “Bayan dan lokaci kadan, ba zaku kara ganina kuma ba. bayan dan lokaci kadan kuma, zaku gan ni.”
Bado muda bhufupi, mwibetalepi kunibhona kabhele; ni baada jha muda bhufupi kabhele, mwibetakunibhona.”
17 Sai wadansu almajiransa sukace wa juna, “Me nene wannan da yake fadi mana, 'Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni?' da kuma, ' zan tafi wurin Uba'?”
Baadhi jha bhanafunzi bha muene bhakajobhesana, “Kiki yaakatujobhela, “muda bhufupi, na mwibetalepi kunibhona kabhele,' na, kisha, mda bhufupi mkanibhona,' na, 'kwandabha nilota kwa Dadi?”
18 Saboda haka sukace, “Me nene wannan da yake fada, 'Bayan dan lokaci kadan'? Bamu san abinda yake fada mana ba.”
Henu, bhakajobha, 'Khenu kheleku kyaijobha, 'Bado mda mfupi'? Tumanyilepi kyaijobha.
19 Yesu kuwa ya ga suna so su tambaye shi, sai ya ce masu, “Wato kuna tambayar juna ne abinda nake nufi da cewa, “Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni'?
Yesu abhuene bhinoghela kun'kota, ni muene akabhajobhela, “Mwikikota, mwe bhene kuhusu e'le, kyanijobhili, 'Bado mda mfupi, mwibetalepi kunibhona kabhele; na baada jha muda mfupi mwibetakunibhona'?
20 Hakika, hakika, ina gaya maku, zaku yi kuka da makoki, amma duniya za ta yi farin ciki, zaku cika da bakin ciki, amma bakin cikinku zai koma farin ciki.
Aminiayi, aminiayi, nikabhajobhela, mwibetakulela ni kuombolesya, lakini ulimwengu wibetakushangilila, mwibetakujha ni huzuni lakini huzuni jha muenga ibetakugeuka kujha furaha.
21 Mace takan ji zafi lokacin da take nakuda don lokacin haihuwa ya zo. Amma da zarar ta haifi jinjirin nan, ba ta kara tunawa da zafin, domin ta na fariciki an haifi mutum a duniya.
N'dala ijha ni huzuni wakati paijha ni uchungu kwandabha wakati ghwa kwifungula ufikili; lakini paikifungula muana, ikhomboka lepi kabhele maumivu kwandabha jha furaha jha muene kwamba muana ahogoliki pa duniani.
22 To yanzu dai kuna bakin ciki, amma zan sake ganinku, kuma ba wanda zai iya kwace maku wannan farin ciki.
Muenga mujheni huzuni henu, lakini nibetakubhabhona kabhele; ni mioyo jha jhomu ibetakuhobhoka na ajhelepi jhaibeta kubhwesya kujhibhosya furaha jha muenga.
23 A rannan, ba zaku tambaye ni komai ba. Hakika hakika, ina gaya maku, komai kuka roki Uba a cikin sunana zai ba ku shi.
Ligono e'le mwibetata lepi kunikota maswali. Aminiayi, Aminiayi, nikabhajobhela,
24 Harwa yau, ba ku roki komai cikin sunana ba. Ku roka, zaku karba, domin farin cikin ku ya zama cikakke.”
Mkas'okayi kyokyoha kwa Dadi, ibetakubhap'ela kwa lihina lya nene; musokayi, namu mwibetakupokela ili kwamba furaha jha muenga ikamilikayi.
25 “Na fada maku wadannan abubuwa cikin karin magana. Amma sa'a tana zuwa da ba zan kara fada maku komai ba cikin karin magana, amaimakon haka zan gaya maku komai a sarari game da Uba.
Nilongilili ni muenga kwa lugha jha jhibelikujhelebhweka, lakini saa jhihida ambapo nibetalepi kulongela kwa lugha jhajhiyeleweka lepi, lakini badala jhiake nibetakubhajobhela waziwazi kuhusu Dadi.
26 A ranar nan, zaku yi roko a cikin sunana kuma bance maku zan yi addu'a ga Uba a madadinku ba,
Ligono e'lu mwibetakus'oka kwa lihina lya nene, na nikabhajobhela lepi kujha nibetakus'oka kwa Dadi kwa ndabha jha muenga;
27 domin Uba da kansa yana kaunarku, domin kun kaunace ni, kun kuma gaskata daga wurin Uban na fito.
Kwa kujha Dadi muene abhaganili kwandabha mniganili nene na kwandabha muniamini kujha nihomili kwa Dadi.
28 Daga wurin Uban na fito, kuma na shigo duniya. Har wa yau, kuma zan bar duniya in koma wurin Uba.”
Nah'omili kwa Dadi na nahidili ku ulimwengu; kabhele, nibhoka ulimwenguni na nilota kwa Dadi”.
29 Almajiransa sukace, duba, “Yanzu kake magana a sarari, ba cikin karin magana ba!
Bhanafunzi bha muene bhakan'jobhela, “Ghwilola, henu ghwilongela wazi wazi na witumila lepi mafumbo.
30 Yanzu mun sani ka san komai, ba sai wani ya tambaye ka ba. Ta haka muka gaskata daga wurin Allah ka fito.”
Henu, tumanyili kujha umanyili mambo ghoha, na wilonda lepi munu jhejhioha akukotayi maswali. Kwandabha ejhe twikiera kujha ghwihomela kwa K'yara.
31 Yesu ya amsa masu yace, “Ashe, yanzu kun gaskata?
Yesu akabhajibu, “Henu muamini?”
32 Duba, sa'a na zuwa, I, sa'ar ta yi, da za a warwatsa ku, kowa ya koma gidansa, kuma ku bar ni ni kadai. Duk da haka kuwa ba ni kadai nake ba, domin Ubana yana tare da ni.
Langayi, saa jhihida, ena na hakika jhifikili, ambapo mwibetakutabhwanyika khila mmonga ni kwa bhene mwibetakunileka najhoni. Lakini nijhelepi ne muene kwandabha Dadi ajhele nani.
33 Na fada maku wannan ne domin a ciki na ku sami salama. A duniya kuna shan tsanani, amma ku karfafa: na yi nasara da duniya,”
Nikabhajobhela mambo agha ili kwamba mugati mwa nene mujhelayi ni amani. Duniani mujhe ni matatizo, lakini mukipelayi muoyo, nibhushindili ulimwengu.

< Yohanna 16 >