< Yohanna 13 >

1 Kamin bukin idin ketarewa, sa'adda Yesu ya san lokaci ya yi da zai tashi daga wannan duniya zuwa wurin Uba, da yake ya kaunaci nasa wadanda ke duniya- ya kaunace su har karshe.
Men før påskehøitiden, da Jesus visste at hans time var kommet da han skulde gå bort fra denne verden til Faderen - likesom han hadde elsket sine egne, som var i verden, så elsket han dem inntil enden.
2 Iblis ya rigaya ya sa a zuciyar Yahuza Iskariyoti dan Saminu, ya bashe da Yesu.
Og mens de holdt måltid, da djevelen allerede hadde inngitt Judas Iskariot, Simons sønn, i hjertet at han skulde forråde ham,
3 Ya san cewa Uba ya bada kome a hannunsa, kuma ya zo daga wurin Allah, kuma zai koma wurin Allah.
og da Jesus visste at Faderen hadde gitt alt i hans hender, og at han var utgått fra Gud og gikk til Gud,
4 Ya tashi daga cin abincin, ya tube tufafinsa, ya dauki tawul ya lullube kansa da shi.
så står han op fra måltidet og legger sine klær av sig og tar et linklæde og binder om sig.
5 Sa'an nan ya zuba ruwa a bangaji, ya fara wanke kafafun almajiran, yana shafe su da tawul din da ya lullube jikinsa da shi.
Derefter slår han vann i et fat, og så begynte han å vaske disiplenes føtter og å tørke dem med linklædet som han var ombundet med.
6 Ya zo wurin Bitrus Saminu, sai Bitrus ya ce masa,”Ubangiji, za ka wanke mani kafa?”
Han kommer da til Simon Peter, og han sier til ham: Herre! vasker du mine føtter?
7 Yesu ya amsa ya ce, “Abin da nake yi ba za ka fahimce shi yanzu ba, amma daga baya za ka fahimta.”
Jesus svarte og sa til ham: Hvad jeg gjør, forstår du ikke nu, men du skal skjønne det siden.
8 Bitrus ya ce masa, “Ba za ka taba wanke mani kafa ba.” Yesu ya amsa masa ya ce, “In ban wanke maka ba, ba ka da rabo da ni”. (aiōn g165)
Peter sier til ham: Du skal aldri i evighet vaske mine føtter! Jesus svarte ham: Dersom jeg ikke vasker dig, har du ikke del med mig. (aiōn g165)
9 Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ba kafafuna kadai za ka wanke ba, amma da hannayena da kaina.”
Simon Peter sier til ham: Herre! ikke bare mine føtter, men også hendene og hodet!
10 Yesu ya ce masa, “Duk wanda ya yi wanka ba ya da bukata, sai dai a wanke kafafunsa, amma shi tsarkakakke ne baidaya; ku tsarkakakku ne, amma ba dukanku ba.”
Jesus sier til ham: Den som er badet, trenger ikke til å vaske annet enn føttene, men er ren over det hele; og I er rene, dog ikke alle.
11 (Don Yesu ya san wanda zai bashe shi, shiyasa ya ce, “Ba dukanku ne ke da tsarki ba.”)
For han visste hvem det var som skulde forråde ham; derfor sa han: I er ikke alle rene.
12 Bayan Yesu ya wanke masu kafafu, ya dauki tufafinsa ya zauna kuma, ya ce masu, “Kun san abin da na yi muku?
Da han nu hadde vasket deres føtter og tatt klærne på sig og atter satt sig til bords, sa han til dem: Skjønner I hvad jeg har gjort med eder?
13 kuna kirana, 'Malam, da Ubangiji,' kun fadi daidai, don haka Nake.
I kaller mig mester og herre, og I sier det med rette, for jeg er det.
14 Idan ni Ubangiji da kuma mallam, na wanke maku kafafu, ya kamata kuma ku wanke wa junan ku kafafu.
Har nu jeg, eders herre og mester, vasket eders føtter, så er også I skyldige å vaske hverandres føtter.
15 Gama na baku misali, saboda ku yi yadda na yi maku.
For jeg har gitt eder et forbillede, forat I skal gjøre som jeg har gjort med eder.
16 Lalle hakika ina gaya muku, bawa ba ya fi mai gidansa girma ba; dan aike kuma ba ya fi wanda ya aiko shi girma ba.
Sannelig, sannelig sier jeg eder: En tjener er ikke større enn sin herre, heller ikke en utsending større enn den som har sendt ham.
17 Idan kun san wadannan abubuwa, ku masu albarka ne idan kun aikata su.
Vet I dette, da er I salige, så sant I gjør det.
18 Ba ina magana akan dukanku ba; Na san wadanda na zaba. Amma domin Nassi ya cika: 'Shi Wanda ya ci gurasata, ya tayar mani'.
Ikke om eder alle taler jeg; jeg vet hvem jeg har utvalgt; men Skriften skulde opfylles: Den som eter sitt brød med mig, har løftet sin hæl mot mig.
19 Ina fada maku wannan yanzu tun kafin haka ta faru domin sa'adda ta faru, ku gaskata Ni ne.
Fra nu av sier jeg eder det før det skjer, forat I, når det skjer, skal tro at det er mig.
20 Hakika, hakika, Ina gaya maku, wanda ya karbi wanda na aiko, Ni ya karba, wanda kuma ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni.
Sannelig, sannelig sier jeg eder: Den som tar imot den jeg sender, han tar imot mig; men den som tar imot mig, han tar imot den som har sendt mig.
21 Bayan Yesu ya fadi haka, ya damu a ruhu, ya yi shaida ya ce, “Lalle hakika, ina gaya muku cewa daya daga cikinku zai bashe ni.”
Da Jesus hadde sagt dette, blev han rystet i ånden, og vidnet og sa: Sannelig, sannelig sier jeg eder: En av eder skal forråde mig.
22 Almajiran suka kalli juna, suna juyayin ko akan wa yake magana.
Disiplene så på hverandre, de kunde ikke skjønne hvem det var han talte om.
23 Daya daga cikin almajiransa, wanda Yesu yake kauna, yana a teburi, jingine a kirjin Yesu.
En av hans disipler satt til bords ved Jesu side, han som Jesus elsket;
24 Siman Bitrus ya ce wa almajirin, “ka fada mana ko akan wa ya ke magana.”
til ham nikker da Simon Peter og sier til ham: Si hvem det er han taler om!
25 Sai ya sake jingina a kirjin Yesu, ya ce masa, “Ubangiji, wanene?”
Han heller sig da op til Jesu bryst og sier: Herre! hvem er det?
26 Sannan Yesu ya amsa, “Shine wanda zan tsoma gutsuren gurasa in ba shi.” Sannan bayan ya tsoma gurasar, sai ya ba Yahuza Dan Siman Iskariyoti.
Jesus svarer: Det er han som jeg gir det stykke jeg nu dypper. Han dypper da stykket, og tar og gir det til Judas, Simon Iskariots sønn.
27 To bayan gurasar, sai shaidan ya shige shi, sai Yesu ya ce masa, “Abinda kake yi, ka yi shi da sauri.”
Og efterat han hadde fått stykket, fór Satan inn i ham. Jesus sier da til ham: Hvad du gjør, det gjør snart!
28 Babu wani a teburin da ya san dalilin dayasa ya fada masa wannan.
Men ingen av dem som satt til bords, skjønte hvad han mente med det han sa til ham;
29 Wadansu sun yi tsamanin cewa, tun da Yahuza ne ke rike da jakkar kudi, Yesu ya ce masa, “Ka sayi abinda muke bukata don idin”, ko kuma ya bada wani abu domin gajiyayyu.
nogen tenkte, fordi Judas hadde pungen, at Jesus sa til ham: Kjøp det vi trenger til høitiden! eller at han skulde gi noget til de fattige.
30 Bayan Yahuza ya karbi gurasar, sai ya fita nan da nan. Da daddare ne kuwa.
Da han nu hadde fått stykket, gikk han straks ut. Men det var natt.
31 Bayan Yahuza ya tafi, Yesu ya ce, “Yanzu an daukaka Dan mutum, kuma an daukaka Allah a cikinsa.
Da han nu var gått ut, sier Jesus: Nu er Menneskesønnen herliggjort, og Gud er herliggjort i ham.
32 Allah zai daukaka shi a cikin kansa, kuma zai daukaka shi nan da nan.
Er Gud herliggjort i ham, så skal også Gud herliggjøre ham i sig, og han skal snart herliggjøre ham.
33 'Ya'ya kanana, ina tare da ku na wani gajeren lokaci. Zaku neme ni, kuma kamar yadda na fadawa Yahudawa, 'in da zan tafi ba za ku iya zuwa ba.' Yanzu kuma na fada maku wannan.
Mine barn! ennu en liten stund er jeg hos eder; I skal lete efter mig, og som jeg sa til jødene: Dit jeg går, kan I ikke komme, således sier jeg nu også til eder.
34 Ina baku sabuwar doka, ku kaunaci juna; kamar yadda na kaunace ku, haka kuma ku kaunaci juna.
Et nytt bud gir jeg eder, at I skal elske hverandre; likesom jeg har elsket eder, skal også I elske hverandre.
35 Ta haka kowa zai san ku almajiraina ne, idan kuna kaunar juna.”
Derpå skal alle kjenne at I er mine disipler, om I har innbyrdes kjærlighet.
36 Siman Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Inda za ni, ba zaka iya bi na ba yanzu, amma zaka bini daga baya.”
Simon Peter sier til ham: Herre! hvor går du hen? Jesus svarte: Dit jeg går, kan du ikke følge mig nu, men du skal følge mig siden.
37 Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan iya binka a yanzu ba? Zan bada raina domin ka.”
Peter sier til ham: Herre! hvorfor kan jeg ikke følge dig nu? Jeg vil sette mitt liv til for dig.
38 Yesu ya amsa ya ce, “Za ka bada ranka domina? Lalle hakika, ina gaya maka, kafin zakara ya yi cara zaka yi musu na sau uku.”
Jesus svarer: Vil du sette ditt liv til for mig? Sannelig, sannelig sier jeg dig: Hanen skal ikke gale før du har fornektet mig tre ganger.

< Yohanna 13 >