< Yohanna 13 >

1 Kamin bukin idin ketarewa, sa'adda Yesu ya san lokaci ya yi da zai tashi daga wannan duniya zuwa wurin Uba, da yake ya kaunaci nasa wadanda ke duniya- ya kaunace su har karshe.
When it was the evening before the Passover celebration, Jesus knew that it was time for him to leave this world and [to return] to [his] Father [in heaven]. He loved us who [were his disciples]. He knew [we would continue to live here] in this world, so now he [showed us] how completely he loved us.
2 Iblis ya rigaya ya sa a zuciyar Yahuza Iskariyoti dan Saminu, ya bashe da Yesu.
We were eating [the Passover meal]. (The devil/Satan) had already suggested to Judas Iscariot (OR, Judas, the man from Kerioth [Town]), the son of Simon, that he should (betray Jesus/enable Jesus’ enemies to seize him).
3 Ya san cewa Uba ya bada kome a hannunsa, kuma ya zo daga wurin Allah, kuma zai koma wurin Allah.
But Jesus knew that his Father had given to him complete authority [to control the situation]. He knew that he had come from God and would soon return to God.
4 Ya tashi daga cin abincin, ya tube tufafinsa, ya dauki tawul ya lullube kansa da shi.
[But before he left us, he wanted to show us how we should love each other]. [So] he got up from where he was eating. He took off his [outer] cloak and wrapped a [long] towel around his waist, [as a slave would do].
5 Sa'an nan ya zuba ruwa a bangaji, ya fara wanke kafafun almajiran, yana shafe su da tawul din da ya lullube jikinsa da shi.
Then he poured some water in a basin. He began to wash our feet, and then dry them with the towel that he had wrapped around himself.
6 Ya zo wurin Bitrus Saminu, sai Bitrus ya ce masa,”Ubangiji, za ka wanke mani kafa?”
When he came to Simon Peter, Peter said to him, “Lord, it is not right for you [RHQ] to [humble yourself by] washing my feet!”
7 Yesu ya amsa ya ce, “Abin da nake yi ba za ka fahimce shi yanzu ba, amma daga baya za ka fahimta.”
Jesus replied to him, “Now you do not understand [the meaning of] what I am doing, but you will understand later.”
8 Bitrus ya ce masa, “Ba za ka taba wanke mani kafa ba.” Yesu ya amsa masa ya ce, “In ban wanke maka ba, ba ka da rabo da ni”. (aiōn g165)
Peter said, “I will never, ever, [allow you to] wash my feet!” Jesus replied to him, “If I do not wash you, you cannot continue (to be my [disciple/to belong to] me).” (aiōn g165)
9 Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ba kafafuna kadai za ka wanke ba, amma da hannayena da kaina.”
So Simon Peter said to him, “Lord, [in that case], do not wash only my feet. Wash my hands and my head, [too]!”
10 Yesu ya ce masa, “Duk wanda ya yi wanka ba ya da bukata, sai dai a wanke kafafunsa, amma shi tsarkakakke ne baidaya; ku tsarkakakku ne, amma ba dukanku ba.”
[Then, to show him that after God had cleansed people from being guilty for sin, they needed only for God to forgive their daily sins] [MET], Jesus said to him, “Those who have recently bathed need only to have their feet washed, [because they get dirty very quickly on the dusty roads]. The [rest of their bodies are] clean. Similarly, I have made you [disciples] free/clean [from the guilt of your sins], although not all of you are free from guilt.”
11 (Don Yesu ya san wanda zai bashe shi, shiyasa ya ce, “Ba dukanku ne ke da tsarki ba.”)
He knew which one [of us] was going to betray him. That is the reason he said, “Not all of you are free from guilt.”
12 Bayan Yesu ya wanke masu kafafu, ya dauki tufafinsa ya zauna kuma, ya ce masu, “Kun san abin da na yi muku?
After he finished washing our feet, he put his cloak back on. Then he sat down and said to us, “Do you understand what I have done for you?
13 kuna kirana, 'Malam, da Ubangiji,' kun fadi daidai, don haka Nake.
You [show that you respect me by] calling me ‘Teacher’ and ‘Lord’. You are right to say that, because I am your teacher and your Lord.
14 Idan ni Ubangiji da kuma mallam, na wanke maku kafafu, ya kamata kuma ku wanke wa junan ku kafafu.
But if I, who am your teacher and your Lord, have washed your feet, you ought to [serve each other by doing things like] washing each other’s feet.
15 Gama na baku misali, saboda ku yi yadda na yi maku.
I have made myself an example for you in order that you should [humbly serve each other] as I have done for you.
16 Lalle hakika ina gaya muku, bawa ba ya fi mai gidansa girma ba; dan aike kuma ba ya fi wanda ya aiko shi girma ba.
Listen to this carefully: A servant is not greater than his master. A messenger is not greater than the one who has sent him. [So, since you are not greater than I am, you should not be proud and unwilling to serve each other].
17 Idan kun san wadannan abubuwa, ku masu albarka ne idan kun aikata su.
Since you now know these things, [God will] be pleased with you if you do them.”
18 Ba ina magana akan dukanku ba; Na san wadanda na zaba. Amma domin Nassi ya cika: 'Shi Wanda ya ci gurasata, ya tayar mani'.
“I am not saying that [God will bless] all of you. I knew [what all of you were like when] I chose you. But [I also chose the one who will betray me], in order that what is written in Scripture might be fulfilled {to fulfill what someone/the psalmist wrote in Scripture}, ‘The one who is [acting like he is my friend by] eating with me has become my enemy [IDM].’
19 Ina fada maku wannan yanzu tun kafin haka ta faru domin sa'adda ta faru, ku gaskata Ni ne.
I am telling you [about someone betraying me] before it happens, in order that when it happens, you may continue to believe that I am ([the Messiah/who I say I am]).
20 Hakika, hakika, Ina gaya maku, wanda ya karbi wanda na aiko, Ni ya karba, wanda kuma ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni.
Listen to this carefully: Those who accept any one of you whom I am sending out, [God will consider that] they are accepting me. And those who accept me, [God will consider that] they are accepting [my Father], who sent me.”
21 Bayan Yesu ya fadi haka, ya damu a ruhu, ya yi shaida ya ce, “Lalle hakika, ina gaya muku cewa daya daga cikinku zai bashe ni.”
After Jesus said this, he was very troubled. He solemnly declared, “Listen to this carefully: One of you is going to enable [my enemies] to seize me.”
22 Almajiran suka kalli juna, suna juyayin ko akan wa yake magana.
We looked at each other. We had no way [to know] whom he was talking about.
23 Daya daga cikin almajiransa, wanda Yesu yake kauna, yana a teburi, jingine a kirjin Yesu.
[I], the [man other people call] ‘the one Jesus loved’, was sitting very close to Jesus.
24 Siman Bitrus ya ce wa almajirin, “ka fada mana ko akan wa ya ke magana.”
Simon Peter motioned to me to indicate that I should ask Jesus whom he was talking about.
25 Sai ya sake jingina a kirjin Yesu, ya ce masa, “Ubangiji, wanene?”
So I leaned close to Jesus and asked him, “Lord, who is it?”
26 Sannan Yesu ya amsa, “Shine wanda zan tsoma gutsuren gurasa in ba shi.” Sannan bayan ya tsoma gurasar, sai ya ba Yahuza Dan Siman Iskariyoti.
Jesus answered, “It is the one to whom I will give this piece of bread after I dip it [in the sauce in the dish].” Then, [to show us that he knew who would enable his enemies to seize him], after he dipped the bread [in the sauce], he gave it to Judas Iscariot (OR, Judas, the man from Kerioth [Town]).
27 To bayan gurasar, sai shaidan ya shige shi, sai Yesu ya ce masa, “Abinda kake yi, ka yi shi da sauri.”
As soon as [Judas ate] the bread, Satan took control of him. Then Jesus said to him, “What you are going to do, do quickly.”
28 Babu wani a teburin da ya san dalilin dayasa ya fada masa wannan.
But none of the rest of us who were sitting there knew why Jesus said that to him.
29 Wadansu sun yi tsamanin cewa, tun da Yahuza ne ke rike da jakkar kudi, Yesu ya ce masa, “Ka sayi abinda muke bukata don idin”, ko kuma ya bada wani abu domin gajiyayyu.
Since Judas took care of the money [people gave us to help us], some thought Jesus was telling him to [go and] buy some things we needed for the [Passover] celebration. [Some thought he was telling him] to give some money to poor people.
30 Bayan Yahuza ya karbi gurasar, sai ya fita nan da nan. Da daddare ne kuwa.
As soon as Judas had eaten the bread, he left. It was dark [outside], and it was dark [MET] [in his soul, too].
31 Bayan Yahuza ya tafi, Yesu ya ce, “Yanzu an daukaka Dan mutum, kuma an daukaka Allah a cikinsa.
After Judas left, Jesus said, “Now it will be shown {[my Father] will show} how wonderful I, the one who came from heaven, am. And by what I do it will be seen {people will see} how great God is.
32 Allah zai daukaka shi a cikin kansa, kuma zai daukaka shi nan da nan.
Since by what I do people will see how awesome God is, God himself will show people how awesome I am. And he will do that very soon.
33 'Ya'ya kanana, ina tare da ku na wani gajeren lokaci. Zaku neme ni, kuma kamar yadda na fadawa Yahudawa, 'in da zan tafi ba za ku iya zuwa ba.' Yanzu kuma na fada maku wannan.
[You whom I love as though you were] my children, I will continue with you only a short time longer. Then you will look for me, but I will not be here. Just like I told the Jewish [leaders] [SYN], I am telling you now, that where I am going, you cannot come [yet].
34 Ina baku sabuwar doka, ku kaunaci juna; kamar yadda na kaunace ku, haka kuma ku kaunaci juna.
Now I am giving you a new commandment: You must love each other. You must love each other in the way that I have loved you.
35 Ta haka kowa zai san ku almajiraina ne, idan kuna kaunar juna.”
If you keep loving each other, everyone [who is aware of that] [HYP] will know that you are my disciples.”
36 Siman Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Inda za ni, ba zaka iya bi na ba yanzu, amma zaka bini daga baya.”
Simon Peter said to him, “Lord, where are you going?” Jesus replied, “The place where I am going, you cannot come with me now, but you will come there later.”
37 Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan iya binka a yanzu ba? Zan bada raina domin ka.”
Peter said, “Lord, why can I not come with you now? I [am ready] to die for you!”
38 Yesu ya amsa ya ce, “Za ka bada ranka domina? Lalle hakika, ina gaya maka, kafin zakara ya yi cara zaka yi musu na sau uku.”
Jesus answered, “[You say] [RHQ] that you [are ready] to die for me. But the truth is that before the rooster crows [early tomorrow morning], you will say three times that you do not [know] me!”

< Yohanna 13 >