< Yohanna 12 >
1 Kwana shidda kafin idin ketarewa, Yesu ya zo Baitanya inda Li'azaru yake, wato wannan da Yesu ya tada daga matattu.
Then, six days before the Passover, Jesus came to Bethany, where Lazarus was (the deceased whom He raised from the dead).
2 Sai suka shirya masa abinci a wurin kuma Matta ce ke hidima, Li'azaru kuwa ya kasance cikin wadanda ke kan tebiri tare da Yesu.
So they gave a dinner for Him there—Martha was serving, while Lazarus was one of those reclining at the table with Him.
3 Sai Maryamu ta dauki wani turare da aka yi da man nard, ta shafe kafafun Yesu da shi, ta kuma share kafafun nasa da gashin kanta. Sai gida ya cika da kamshin turaren.
Then Mary, bringing a pound of pure oil of nard, very costly, anointed Jesus' feet, and wiped His feet with her hair! And the house was filled with the fragrance of the oil.
4 Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin almajiransa, wanda zai bashe shi, ya ce, “
Then one of His disciples, Judas Iscariot, Simon's son (who was about to betray Him), said,
5 “Me yasa ba a sayar da wannan turare dinari dari uku a ba gajiyayyu ba?”
“Why wasn't this oil sold for 300 denarii and given to the poor?”
6 Ya fadi haka ba don ya damu da gajiyayyu ba, amma domin shi barawo ne: shi ne ma'aji, kuma yana sata daga jakkar kudi.
(Now he did not say this because the poor mattered to him, but because he was a thief and had the money box; and used to pilfer what was put in it.)
7 Yesu ya ce, “Ku kyale ta ta ajiye abinda ta tanada domin jana'iza ta.
So Jesus said: “Let her be; she has performed this with a view to my burial.
8 Gajiyayyu suna tare da ku a koyaushe, ni kuwa ba zan kasance da ku koyaushe ba.
For you always have the poor with you, but you do not always have me.”
9 To babban taron Yahudawa sun ji cewa Yesu yana wurin, sai suka zo, ba don Yesu kawai ba amma domin su ga Li'azaru, wanda Yesu ya tada daga matattu.
Then a large crowd of the Jews learned that He was there; and they came, not only because of Jesus but also to see Lazarus, whom He had raised from the dead.
10 Sai manyan firistoci suka kulla makirci akan yadda za su kashe Li'azaru shima;
So the chief priests decided to kill Lazarus as well,
11 domin saboda shi ne yahudawa dayawa suka je suka bada gaskiya ga Yesu.
in that because of him many of the Jews were defecting and believing into Jesus.
12 Kashegari, babban taro suka zo idin. Da suka ji cewa Yesu na zuwa Urushalima,
The next day a large crowd that had come to the feast, when they heard that Jesus was coming into Jerusalem,
13 Sai suka dauki ganyen dabino suka fita gari suka tare shi da kira mai karfi suna cewa, “Hosanna! Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji, Sarkin Isra'ila.
took branches from palm trees and went out to meet Him. And they started shouting: “Hosanna!” “Blessed is He who comes in the name of the Lord!” “King of Israel!”
14 Yesu ya sami wani Aholakin jaki, ya hau kansa; kamar yadda aka rubuta,
And finding a young donkey Jesus sat on it; just as it is written:
15 “Kada ki ji tsoro ke 'yar Sihiyona; duba, ga Sarkinki na zuwa, zaune a kan danJaki”.
“Fear no more, daughter of Zion. Look, your King is coming, sitting on a donkey's colt!”
16 Almajiransa basu fahimci wannan al'amari ba da farko, amma bayan da aka daukaka Yesu, sai suka tuna cewa an rubuta wadannan abubuwa game da shi, kuma sun yi masa wadannan abubuwa.
(Now His disciples did not understand these things at first; but when Jesus was glorified, then they remembered that these things were written about Him, and they had done them to Him.)
17 Sai taron da ke tare da Yesu a ranar da ya kira Li'azaru daga kabari ya kuma tashe shi daga matattu, suka bada shaida.
So the crowd that had been with Him when He called Lazarus out of the tomb and raised him from the dead continued to testify.
18 Domin wannan ne kuma taron suka zo domin su sadu da shi saboda sun ji cewa ya yi wannan alama.
That is also why the crowd met Him, because they heard that He had performed this sign.
19 Don haka, sai farisawa suka shiga magana a tsakanin su suna cewa “Duba, babu abinda zaku iya yi; kun ga, duniya ta gama bin sa.
So the Pharisees said among themselves: “You can see that you are not making any difference! Just look, the world has gone off after Him!”
20 Akwai wadansu Helinawa cikin wadanda suka je sujada a idin.
Now there were some Greeks among those who went up to worship at the feast.
21 Wadannan suka tafi wurin filibus, mutumin Betsaida da ke Galili, suka ce masa, “Mallam, muna so mu ga Yesu.
So these men approached Philip, who was from Bethsaida in Galilee, and requested of him saying, “Sir, we want to see Jesus.”
22 Filibus ya tafi ya fadawa Andrawus; sai Andrawus ya tafi tare da Filibus, suka kuwa gaya wa Yesu.
Philip goes and tells Andrew, and in turn Andrew and Philip tell Jesus.
23 Yesu ya amsa masu ya ce, “sa'a ta zo da za'a daukaka Dan mutum.
But Jesus answered them saying: “The hour has come for the Son of the Man to be glorified.
24 Hakika, hakika, Ina ce maku, in ba kwayar alkama ta fadi kasa ba ta mutu, za ta kasance ita kadai; amma idan ta mutu, za ta bada 'ya'ya masu yawa.
Most assuredly I say to you, if a grain of wheat, having fallen into the ground, does not die, it remains alone; but if it dies it bears a lot of fruit.
25 Duk wanda yake son ransa, zai rasa shi; amma wanda ba ya son ransa a duniyan nan za ya kiyaye shi domin rayuwa ta har abada. (aiōnios )
The one ‘loving’ his life will waste it, and the one ‘hating’ his life, in this world, will preserve it into eternal life. (aiōnios )
26 Idan wani na bauta mani, to bari ya biyo ni; kuma duk inda nike, a can bawana zai kasance kuma. Duk wanda ke bauta mani, Uban zai girmama shi.
If anyone would serve me, let him follow me; and where I am, my servant will be too. Further, if anyone serves me, the Father will honor him.
27 Yanzu raina na cikin damuwa, to me zan ce? 'Uba, ka cece ni daga wannan sa'a? Amma Saboda wannan dalili ne na zo wannan sa'a.
“Now my soul is distressed, and what should I say—‘Father, rescue me from this hour’? But this is why I came to this hour—
28 Uba, ka daukaka sunanka”. Sai wata murya daga sama ta ce, “Na daukaka shi, zan kuma sake daukaka shi.
‘Father, glorify your name!’” Then a Voice came out of Heaven, “I have both glorified it and will glorify it again!”
29 Daganan sai taron dake tsaye kuma suka ji muryar, suka ce an yi tsawa. Wasu suka ce, “Mala'ika ya yi magana da shi”.
So the crowd that was standing by and listening said that it had thundered. Others said, “An angel has spoken to Him.”
30 Yesu ya amsa ya ce, “wannnan murya ta zo ba saboda ni ba, amma domin ku.”
Jesus answered and said: “It was not for my sake that this Voice came, but for your sakes.
31 Yanzu za'a shar'anta duniya. Yanzu za'a kori mai mulkin duniyan nan.
Now is the judgment of this world; now the ruler of this world will be thrown out.
32 Sa, annan ni, idan an daga ni daga duniya, zan jawo dukan mutane zuwa gare ni”.
While I, if I be lifted up from the earth, I will draw all people to myself.”
33 Ya fadi wannan ne domin ya nuna irin mutuwar da za ya yi.
(Now He said this to indicate by what kind of death He was about to die.)
34 Taro suka amsa masa cewa, “Mun ji a cikin shari'a cewa Almasihu za ya kasance har abada. Yaya za ka ce, 'za'a daga dan mutum'? Wanene wannan dan mutum?” (aiōn )
The people answered Him: “We have heard from the Law that the Messiah remains forever; and so how can you say, ‘The Son of the Man must be lifted up’? Who is this ‘the Son of the Man’?” (aiōn )
35 Yesu ya ce masu, “Nan da lokaci kadan za ku kasance da haske, ku yi tafiya tun haske na tare da ku, kada duhu ya mamaye ku. Wanda ke tafiya cikin duhu, bai san inda za shi ba.
Then Jesus said to them: “The Light will be with you just a little longer. Walk while you have the light, so that darkness does not overtake you; the one who walks in the darkness does not know where he is going.
36 Ku gaskata ga haske tun yana tare da ku domin ku zama yayan haske”. Yesu ya fadi wadannan abubuwa sannan ya tafi ya boye masu.
While you have the Light, believe into the Light, so that you may become sons of light.” Jesus said these things, and going away He was hidden from them.
37 Kodashike Yesu ya yi alamu da dama a gabansu, duk da haka ba su gaskata shi ba.
Although He had performed so many signs in their presence, they were not believing into Him;
38 Saboda maganar annabi Ishaya ta cika, wadda ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata rahoton mu? Ga wa kuma hannun Ubangiji ya bayyana?
so that the word spoken by Isaiah the prophet should be fulfilled: “Lord, who has believed what we heard? And to whom has the arm of the Lord really been revealed?”
39 Saboda wannan dalili basu gaskata ba, gama Ishaya ya sake cewa,
Therefore they were unable to believe, in that Isaiah said again:
40 ya makantar da su, ya kuma taurare zuciyarsu, saboda kada su gani da idanunsu, su kuma sami fahimta da zuciyarsu, su juyo wurina in warkar da su.
“He has blinded their eyes and hardened their hearts, lest they should see with their eyes and understand with their hearts and should turn around, and I would heal them.”
41 Ishaya ya fadi wadannan abubuwa ne domin ya hangi daukakar Yesu ya kuma yi magana game da shi.
Isaiah said these things when he saw His glory and spoke concerning Him.
42 Amma duk da haka, dayawa cikin shugabanni suka gaskata Yesu. Amma saboda farisawa, basu shaida shi a sarari ba, domin kada a kore su daga majami'a.
Nevertheless, even among the rulers many believed into Him, but because of the Pharisees they did not confess Him, so they would not be expelled from the synagogue;
43 Suna son yabo daga mutane fiye da yabon dake zuwa daga Allah.
for they loved the praise of men more than the praise of God.
44 Yesu ya yi magana da babbar murya, ya ce, “Wanda ya gaskata ni, ba ni yake gaskatawa kadai ba, amma kuma yana gaskata wanda ya aiko ni,
Jesus called out and said: “The one believing into me believes not into me but into Him who sent me.
45 kuma wanda ke gani na, yana ganin shi wanda ya aiko ni.
And the one seeing me sees Him who sent me.
46 Na zo ne a matsayin haske a duniya, saboda duk wanda ya gaskata da ni ba za ya yi tafiya cikin duhu ba.
I, Light, have come into the world so that everyone who believes into me will not remain in the darkness.
47 Duk wanda ya ji maganata baya gaskata ba, ba ni hukunta shi; gama ban zo in yi wa duniya hukunci ba, amma don in ceci duniya.
Also, if someone hears my words and does not believe, I do not judge him; because I did not come to judge the world but to save the world.
48 Wanda ya ki ni, ya kuma ki ya karbi magana ta, akwai wanda za ya yi masa hukunci. Kalmar da na fada, ita ce za ta yi masa hukunci a rana ta karshe.
The one who rejects me and does not receive my sayings has that which judges him—the word that I have spoken, that is what will judge him on the last day;
49 Maganar da ni ke yi, ba ra'ayina ba ne. Amma Uba wanda ya aiko ni shi ke bani umarni game da abin da zan ce da abin da zan fadi.
because I have not spoken on my own, but the Father who sent me, He gave me a command, what I should say and what I should speak.
50 Na san umarninsa rai ne madawwami, don haka na ce - kamar yadda Uba ya fada, haka ni ma nake fadi.” (aiōnios )
And I know that His command is eternal life. So whatever I say, I say it just like the Father told me.” (aiōnios )