< Yohanna 11 >

1 To wani mutum mai suna Li'azaru, yayi rashin lafiya. Shi mutumin Baitanya ne, wato kauyen su Maryamu da 'yar'uwarta Matta.
Linu mukwame zumwi yabali kusumpwa chezina lya Lazaro yabali kulwala. yaba kuzwa mwa Betenia, mumunzi mwabali kwikala Maria ni mukulwe Mareta.
2 Wato wannan Maryamu da ta shafe Ubangiji da mur ta kuma share masa kafafunsa da gashin kanta, wadda dan'uwanta Li'azaru ke rashin lafiya.
nji Maria yaba singi Simwine mafuta esende ni kumupemula kumatende ninsuki zakwe, imi Lazaro yabali kulwala ibala nchizyakwe.
3 'Yan'uwannan mata suka aika sako wurin yesu, cewa, “Ubangiji, duba, shi wanda kake kauna yana rashin lafiya”.
Linu banchizyakwe nichibatumina iñusa kwa Jesu, nibacho, “Simwine, bone, iye yosaka ahulu ulwala.”
4 Da Yesu ya ji, sai ya ce “Wannan ciwo ba zai kai ga mutuwa ba, amma domin daukakar Allah ne, domin Dan Allah ya sami daukaka tawurin ta”.
Linu Jesu hazuwa bulyo, nati, Uku kulwala kahena kufwa, kono bwakubonisa maata a Simwine chobulyo nimwana wa Ireeza uswanela kulumbekwa kachibatendahali.”
5 Yesu yana kaunar Matta, da 'yar'uwarta da Li'azaru.
Linu Jesu abali kusaka ahulu Mareta ni mwanchakwe ni Lazaro bulyo.
6 Da yaji cewa Li'azaru na rashin lafiya, sai ya tsaya kwana biyu a inda ya ke.
Chobulyo hazuwa kulwala kwa Lazaro, Jesu abekali mazuba amwi obele muchibaka mwabekele.
7 Bayan haka, sai ya ce wa almajiransa, “Bari mu je Yahudiya kuma.”
Linu hakumana bulyo, Chowamba kuba rutwana bakwe, “Twende tuye kwa Judea hape.”
8 Sai almajiransa suka ce masa, “Mallam, harwayau Yahudaya na neman ka domin su jefe ka da duwatsu, kuma kana son komawa can?”
Barutwana chibawamba kwali, “Muruti, munako inu Majuda basaka kukugobola nimabwe, linu iwe usaka kubola kwateni hape?”
9 Yesu ya amsa, “Ba sa'a goma sha biyu ce ta haske a rana guda ba? Idan mutum ya yi tafiya da rana, ba za ya yi tuntube ba, domin yana gani ta wurin hasken wannan duniya.
Jesu nichati, kahena kuti inhola zitenda ikumi ni obele eseli mwizuba? Linu zumwi muntu hayenda musihali, keti aholofale kapa kusitatala kakuti ubwene mwahitite cha liseli lyefasi.
10 Amma idan mutum ya yi tafiya chikin dare, za ya yi tuntube domin haske ba ya tare da shi.
Nihakuba bulyo, hayenda masiku, mwasitatale kakuli iseli kalina mwali.”
11 Ya fadi wadannan al'amura, kuma bayan wadannan abubuwa, sai ya ce masu, “Abokinmu Li'azaru ya yi barci, amma zan je don In tashe shi daga barci”.
Nichawamba izi zintu, linu hamana izo zintu, nichabawambila, “Mulikanetu Lazaro chalala, kono nikaya ili kuti nikamubuse.”
12 Sai almajirai suka ce masa, “Ubangiji, idan barci yake yi, ai za ya farka.”
Barutwana linu chibawamba kwali, “Simwine, haiba ulele, mwabe nenza.”
13 Yesu kuwa ya yi maganar mutuwar Li'azaru ne, amma su suna tsammani yana magana akan barci ne na hutu.
Linu Jesu chabataluseza kuamana niifu, Chobulyo abo babali kuhupula kuti uwamba iñonzi zakulikatulusa.
14 Sai Yesu ya yi masu bayani cewa, “Li'azaru ya mutu.
Linu Jesu nichabataluseza, “Lazaru ufwile.
15 Ina farinchiki domin ku, da bani a wurin domin ku gaskata. Bari mu je wurinsa.”
Nisangite, kebaka lyenu, kuti kana nibena kwateni kokuti nimubazumini. Twende kwali.”
16 Toma wanda ake kira Dan tagwaye, ya ce wa sauran almajirai, “Bari mu tafi domin mu mutu tare da Yesu.”
Tomasi yaba kunsumpwa Didima, chawamba ku Barutwana, “Tuyende naswe tukafwe ni Jesu.”
17 Da Yesu ya iso, sai ya tarar cewa Li'azaru ya rigaya ya yi kwana hudu a kabari.
Linu Jesu hakeza, neza kuwana kuti Lazaro chowina kale mwikumbu chamazuba onee.
18 Baitanya kuma tana kusa da Urushalima, 'yar tafiya marar nisa ce a tsakanin su.
Linu Betania ibena hembali ni Jerusalema, kazibima zotatwe.
19 Yahudawa dayawa sun zo wurin Maryamu da Matta domin su yi masu ta'aziyar mutuwar dan'uwansu.
Bungi bwa Majuda babali kwiza kwa Mareta ni Maria, kubaombaomba kuamana ni nchinzabo.
20 Da Matta ta ji cewa Yesu na zuwa, sai ta tafi domin ta same shi, amma Maryamu na zamne a cikin gida.
Linu Mareta, hazuwa kuti Jesu ukezite, nichibaka mukatanyeza, cobulyo Maria abekele munzubo.
21 Matta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan tare da mu, da dan'uwana baya mutu ba”.
Mareta linu chawambila Jesu, “Nfumwangu, kapa kobena kunu, nchizyangu nasena bafwi.
22 Ko yanzu na san cewa duk abinda ka roka a wurin Allah, za ya ba ka.
Nangati hanu, nizi kuti chimwi nichimwi chokumbila kwa Ireeza, mwakuhe.”
23 Yesu ya ce mata, “Dan'uwanki za ya rayu kuma.
Jesu chawamba kwali, “Nchizyako mwabuke hape.”
24 Sai Matta ta ce masa, “Na san zaya rayu kuma a tashin mattatu na ranar karshe.”
Mareta chawamba kwali, “Nizi kuti mwabuke hape he henzuho luzuba lwamamani mani.”
25 Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu, ni ne kuma rai; wanda ya bada gaskiya gare ni, ko ya mutu, za ya rayu;
Jesu chawamba kwali, “Njeme ni nzuho ni buhalo; yense yozumina kwangu, niha fwa, mwa hale;
26 Kuma duk wanda yake raye, ya kuma bada gaskiya gare ni, ba zai mutu ba dadai. Kin gaskata da wannan?” (aiōn g165)
chobulyo yense yohala ni kuzumina kwangu keti nafwe. Na muzumina iyi ndaba?” (aiōn g165)
27 Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, Na gaskata cewa kaine Almasihu, Dan Allah, wanda ke zuwa duniya.
Nichawamba kwali, “Ee, Nfumwangu, nizumina kuti njewe Kreste, mwana we Ireeza, yokezite mwi nkanda.”
28 Sa'adda ta fadi haka, sai ta koma ta kira yar'uwarta Maryamu gefe guda. Ta ce, “mallam ya iso, kuma yana kiran ki.”
Hamana kuwamba izi, chozwa mwateni nikusumpa mwanchakwe Maria kakuli ungula. chamuwambila, “Muruti chasika mi ukusumpa.”
29 Da ta ji haka, sai ta tashi da sauri ta tafi wurin sa.
Linu hazuwa bulyo, chonyamuka kapili nikuya kwali.
30 Yesu bai rigaya ya shiga kauyen ba, yana nan inda Matta ta zo ta same shi.
Linu Jesu kanabeni kusika mumunzi abali kusina kuchibaka kwaba kamukatanyezi Mareta.
31 Da Yahudawan nan dake tare da Maryamu, wato wadannan da suka zo mata ta'aziya, suka ga ta fita daga chikin gida da sauri, sai suka bi ta, suna tsammanin cewa ta tafi ta yi kuka ne a kabari.
Imi Majuda, babena naye mwinzubo babali kumuomba omba nibabona Maria hanyamuka kapili pili kuzwila hanze, chiba mwichilila, kuhupula kuti chokaya kwikumbu aka siliseze kwateni.
32 Da Maryamu ta kai inda Yesu ya ke, sai ta fadi gaban sawayensa, ta ce, “Ubangiji, inda kana tare da mu, da dan'uwana bai mutu ba”.
Linu Maria, hakeza kwabekele Jesu imi namubona, chowila hamatende akwe ni kumuwambila, “Simwine, kapa kobena kunu, nchinzyangu nasena abafwi,”
33 Da Yesu ya gan ta tana kuka, da wadannan Yahudawa da suka bi ta, sai ya yi juyayi a ruhu ya damu kuma;
Linu Jesu chamubona nasilisa, imi ni Mujuda wakeza naye chokwete usilisa,
34 sai ya ce, “A ina kuka kwantar da shi?” Sai suka ce masa, “Ubangiji, zo ka gani.”
chabahinditwe muluhuho lwakwe mi abali kubilela; chawamba, “Mubamulaziki kuhi?” Niba mwitaba, “Nfumwangu, wize zo bone.”
35 Yesu ya yi kuka.
Jesu nasilisa.
36 Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake kaunar Li'azaru!”
Linu Majuda cibawamba, Mubone mwaba kusakila Lazaru!”
37 Amma wadansun su suka ce, “Shi wannan mutum da ya iya ba makaho ganin gari, da bai iya hana wannan mutum mutuwa ba?
Imi bamwi chibawamba, “Kanjiyena uzu mukwame, yabeyaluli menso amukwame wamuhofu, hape ibaleti kuti uzu mukwame kuti afwe?”
38 Yesu yana cikin juyayi kuma a cikin kansa, sai ya tafi kabarin. Kabarin a kogo ne an kuma rufe bakinsa da dutse.
Linu Jesu hape, nalizuwa kutomoha inkulo hape, nayenda kwikumbu. linu chibali ilindi, imi ibwe libatulitwe hateni.
39 Sai Yesu ya ce, “A kawar da dutsen.” Matta yar'uwar Li'azaru wanda ya mutu, ta ce wa Yesu, “Ubangiji, Yanzu jikin ya ruba domin ya kai kwana hudu da mutuwa”.
Jesu nati, “Muzwise hateni ibwe.” Mareta, nchinzye wa Lazaro, iye yofwile, nawambila Jesu, “Nfumwangu, cheinu inako chitupu chichinunka, kakuti chikwahinda mazuba onee kuzwa habafwili.”
40 Yesu ya ce mata, “Ba na ce maki idan kin gaskata za ki ga daukakar Allah ba?”
Linu Jesu nati kwali, Naa kana nibakuwambili kuti, heba uzumina, mokabone mubuso wa Ireeza?”
41 Sai suka kawar da dutsen. Yesu ya daga idanunsa ya ce, “Uba, na gode maka domin kana ji na.”
Linu chibazwisa ibwe hekumbu. Jesu nakatula menso akwe kulola kwiulu imi nati, “Tate, Nilitumela kakuti wateka kwangu.
42 Na san kana ji na a kowane lokaci, amma domin wannan taro da ke tsaye kewaye da ni nike wannan magana, domin su bada gaskiya cewa kaine ka aiko ni.”
Nizi kuti utekanga kwangu inako yonse, kono niwamba bulyo kebaka lyekunga linizimbulukite kunibika mukati, ili kuti bazumine kuti ubanitumi.”
43 Bayan ya yi wannan magana, sai ya daga murya ya ce, “Li'azaru, ka fito!”
Chobulyo nawamba buti, nahuweleza chalizwi lizuweka ahulu, “Lazaro, wize hanze!”
44 Sai mataccen ya fito; kafafunsa da hannayensa na daure da likkafani, fuskarsa kuma na lullube da tsumma. Yesu ya ce masu, “Ku kwance shi, ya tafi”.
Mukwame yabafwile nazwa mwikumbu; matende akwe nimayanza abali kuzingeletwe masila. Jesu nawamba kubali, “Mumusumunune imi mumusiye ayende.”
45 To dayawa daga cikin yahudawan da suka zo wurin Maryamu suka kuma ga abinda Yesu ya yi, suka gaskata da shi;
Linu bungi bwa Majuda babakezi kwa Maria imi nibabona zabatendi Jesu, niba zumina kwali,
46 amma wadansu suka koma wurin farisawa suka fada masu abubuwan da Yesu ya yi.
kono bamwi mukati kabo chibayenda ku Bafalisi imi chibakawamba zabatendi Jesu.
47 Sai manyan firistoci da farisawa suka tara majalisa wuri guda, suka ce, “menene za mu yi?” Mutumin nan yana alamu masu yawa.
Cwale mapurita bakulwana ni Bafalisi chibakopanya inkuta hamwina imi nibawamba, “Mutupange chihi? Uzu mukwame upanga imakazo zingi.
48 Idan mun kyale shi haka, duka za su gaskata da shi; Romawa za su zo su kwace wurinmu da al'ummar mu.
heba mutumusiye yenke sina buti, bonse mubazumine kwali; Maroma mubatunyange minzi yetu yonse ni nkanda yetu.”
49 Duk da haka, wani daga cikin su wato, Kayafas wanda shine babban firist a wannan shekara, ya ce da su, “baku san komai ba”.
Nihakuba bulyo, zumwi mukwame mukati kabo, Kayafa, yabali muprisita mukulwana mwecho chilimo, nati kubali, “Kakwina chimwizi.
50 Ba ku lura cewa ya fi maku kyau mutum daya ya mutu domin mutane, a maimakon dukan al'umma ta hallaka.”
Kamubwene kuti kulotu nibutuka kuti mukwame yenke afwile chichaba kundeye kuti inkanda yonse imaniswe.”
51 Ya fadi wannan ne ba don kansa ba, amma sabo da shine babban firist, ya yi anabci ne cewa ya kamata Yesu ya mutu domin al'ummar;
Lyahanu izi zawamba kazizwi kwali mwine. kono, kakuti abali muprisita mukulwana icho chilimo, aba polofiti kuti Jesu mwafwile inkanda;
52 kuma ba don alummar kawai ba, amma domin a tattara 'ya'yan Allah da suke warwatse ko'ina wuri daya.
kono isini inkanda bulyo imi kono kuti bana ba Ireeza bahasene bekale hamwina kalusika lonke.
53 Tun daga wannan rana suka fara neman hanyar da za su kashe Yesu.
Linu kuzwa ulo luzuba niba zuminzana mwete behaile Jesu.
54 Tun daga nan Yesu ya dena tafiya a sarari chikin Yahudawa, amma sai ya koma wani yanki kusa da jeji a wani gari da ake kira Ifraimu. A can kuma ya zamna da almajiransa.
Kelyo ibaka Jesu nasiya kuyenda mukati ka Majuda nibamubwene, imi chozwa mweyo inkanda nikuya mwihalaupa mumuleneñi wa Efraimi. Uko abakekali ni barutwana.
55 Idin ketarewa na Yahudawa ya yi kusa, da yawa sun tafi Urushalima daga yankin kasar kamin ranar idi domin su tsarkake kan su.
Lyahanu i Paseka ya Majuda chibena hafuhi, imi bungi bwabo nibaya mwa Jerusalema kuzwa mwinkanda i Paseka niseni kusika kuti bakalijoloze abo bene.
56 Suka shiga neman Yesu, suna magana da junan su yayin da suke tsaitsaye a haikali, cewa “me kuke tunani? Ba za ya zo idin bane?”
Babali kukabulola Jesu, imi nibena mwi Tempele nibakwete balibuza buza, “Muhupula bule? Na sanzi akezi kumukiti?”
57 Babban firist da farisawa sun rigaya sun ba da umurni cewa duk inda aka ga Yesu a zo a shaida domin su kama shi.
Linu muprisita mukulwana ni Bafalisi niba hewa mulao kuti haiba kwina yowizi kwena Jesu, uswanela kuwamba ili kuti bamukwate.

< Yohanna 11 >