< Yohanna 11 >

1 To wani mutum mai suna Li'azaru, yayi rashin lafiya. Shi mutumin Baitanya ne, wato kauyen su Maryamu da 'yar'uwarta Matta.
Men der laa en Mand syg, Lazarus fra Bethania, den Landsby, hvor Maria og hendes Søster Martha boede.
2 Wato wannan Maryamu da ta shafe Ubangiji da mur ta kuma share masa kafafunsa da gashin kanta, wadda dan'uwanta Li'azaru ke rashin lafiya.
Men Maria var den, som salvede Herren med Salve og tørrede hans Fødder med sit Haar; hendes Broder Lazarus var syg.
3 'Yan'uwannan mata suka aika sako wurin yesu, cewa, “Ubangiji, duba, shi wanda kake kauna yana rashin lafiya”.
Da sendte Søstrene Bud til ham og lod sige: „Herre! se, den, du elsker, er syg.”
4 Da Yesu ya ji, sai ya ce “Wannan ciwo ba zai kai ga mutuwa ba, amma domin daukakar Allah ne, domin Dan Allah ya sami daukaka tawurin ta”.
Men da Jesus hørte dette, sagde han: „Denne Sygdom er ikke til Døden, men for Guds Herligheds Skyld, for at Guds Søn skal herliggøres ved den.”
5 Yesu yana kaunar Matta, da 'yar'uwarta da Li'azaru.
Men Jesus elskede Martha og hendes Søster og Lazarus.
6 Da yaji cewa Li'azaru na rashin lafiya, sai ya tsaya kwana biyu a inda ya ke.
Da han nu hørte, at han var syg, blev han dog to Dage paa det Sted, hvor han var.
7 Bayan haka, sai ya ce wa almajiransa, “Bari mu je Yahudiya kuma.”
Derefter siger han saa til Disciplene: „Lader os gaa til Judæa igen!”
8 Sai almajiransa suka ce masa, “Mallam, harwayau Yahudaya na neman ka domin su jefe ka da duwatsu, kuma kana son komawa can?”
Disciplene sige til ham: „Rabbi! nylig søgte Jøderne at stene dig, og du drager atter derhen?”
9 Yesu ya amsa, “Ba sa'a goma sha biyu ce ta haske a rana guda ba? Idan mutum ya yi tafiya da rana, ba za ya yi tuntube ba, domin yana gani ta wurin hasken wannan duniya.
Jesus svarede: „Har Dagen ikke tolv Timer? Vandrer nogen om Dagen, da støder han ikke an; thi han ser denne Verdens Lys.
10 Amma idan mutum ya yi tafiya chikin dare, za ya yi tuntube domin haske ba ya tare da shi.
Men vandrer nogen om Natten, da støder han an; thi Lyset er ikke i ham.”
11 Ya fadi wadannan al'amura, kuma bayan wadannan abubuwa, sai ya ce masu, “Abokinmu Li'azaru ya yi barci, amma zan je don In tashe shi daga barci”.
Dette sagde han, og derefter siger han til dem: „Lazarus, vor Ven, er sovet ind; men jeg gaar hen for at vække ham af Søvne.”
12 Sai almajirai suka ce masa, “Ubangiji, idan barci yake yi, ai za ya farka.”
Da sagde Disciplene til ham: „Herre! sover han, da bliver han helbredet.”
13 Yesu kuwa ya yi maganar mutuwar Li'azaru ne, amma su suna tsammani yana magana akan barci ne na hutu.
Men Jesus havde talt om hans Død; de derimod mente, at han talte om Søvnens Hvile.
14 Sai Yesu ya yi masu bayani cewa, “Li'azaru ya mutu.
Derfor sagde da Jesus dem rent ud: „Lazarus er død!
15 Ina farinchiki domin ku, da bani a wurin domin ku gaskata. Bari mu je wurinsa.”
Og for eders Skyld er jeg glad over, at jeg ikke var der, for at I skulle tro; men lader os gaa til ham!”
16 Toma wanda ake kira Dan tagwaye, ya ce wa sauran almajirai, “Bari mu tafi domin mu mutu tare da Yesu.”
Da sagde Thomas (hvilket betyder Tvilling), til sine Meddisciple: „Lader os ogsaa gaa, for at vi kunne dø med ham!”
17 Da Yesu ya iso, sai ya tarar cewa Li'azaru ya rigaya ya yi kwana hudu a kabari.
Da Jesus nu kom, fandt han, at han havde ligget i Graven allerede fire Dage.
18 Baitanya kuma tana kusa da Urushalima, 'yar tafiya marar nisa ce a tsakanin su.
Men Bethania var nær ved Jerusalem, omtrent femten Stadier derfra.
19 Yahudawa dayawa sun zo wurin Maryamu da Matta domin su yi masu ta'aziyar mutuwar dan'uwansu.
Og mange af Jøderne vare komne til Martha og Maria for at trøste dem over deres Broder.
20 Da Matta ta ji cewa Yesu na zuwa, sai ta tafi domin ta same shi, amma Maryamu na zamne a cikin gida.
Da Martha nu hørte, at Jesus kom, gik hun ham i Møde; men Maria blev siddende i Huset.
21 Matta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan tare da mu, da dan'uwana baya mutu ba”.
Da sagde Martha til Jesus: „Herre! havde du været her, da var min Broder ikke død.
22 Ko yanzu na san cewa duk abinda ka roka a wurin Allah, za ya ba ka.
Men ogsaa nu ved jeg, at hvad som helst du beder Gud om, vil Gud give dig.”
23 Yesu ya ce mata, “Dan'uwanki za ya rayu kuma.
Jesus siger til hende: „Din Broder skal opstaa.”
24 Sai Matta ta ce masa, “Na san zaya rayu kuma a tashin mattatu na ranar karshe.”
Martha siger til ham: „Jeg ved, at han skal opstaa i Opstandelsen paa den yderste Dag.”
25 Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu, ni ne kuma rai; wanda ya bada gaskiya gare ni, ko ya mutu, za ya rayu;
Jesus sagde til hende: „Jeg er Opstandelsen og Livet; den, som tror paa mig, skal leve, om han end dør.
26 Kuma duk wanda yake raye, ya kuma bada gaskiya gare ni, ba zai mutu ba dadai. Kin gaskata da wannan?” (aiōn g165)
Og hver den, som lever og tror paa mig, skal i al Evighed ikke dø. Tror du dette?” (aiōn g165)
27 Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, Na gaskata cewa kaine Almasihu, Dan Allah, wanda ke zuwa duniya.
Hun siger til ham: „Ja, Herre! jeg tror, at du er Kristus, Guds Søn, den, som kommer til Verden.”
28 Sa'adda ta fadi haka, sai ta koma ta kira yar'uwarta Maryamu gefe guda. Ta ce, “mallam ya iso, kuma yana kiran ki.”
Og da hun havde sagt dette, gik hun bort og kaldte hemmeligt sin Søster Maria og sagde: „Mesteren er her og kalder ad dig.”
29 Da ta ji haka, sai ta tashi da sauri ta tafi wurin sa.
Da hun hørte det, rejste hun sig hastigt og gik til ham.
30 Yesu bai rigaya ya shiga kauyen ba, yana nan inda Matta ta zo ta same shi.
Men Jesus var endnu ikke kommen til Landsbyen, men var paa det Sted, hvor Martha havde mødt ham.
31 Da Yahudawan nan dake tare da Maryamu, wato wadannan da suka zo mata ta'aziya, suka ga ta fita daga chikin gida da sauri, sai suka bi ta, suna tsammanin cewa ta tafi ta yi kuka ne a kabari.
Da nu Jøderne, som vare hos hende i Huset og trøstede hende, saa, at Maria stod hastigt op og gik ud, fulgte de hende, idet de mente, at hun gik ud til Graven for at græde der.
32 Da Maryamu ta kai inda Yesu ya ke, sai ta fadi gaban sawayensa, ta ce, “Ubangiji, inda kana tare da mu, da dan'uwana bai mutu ba”.
Da Maria nu kom derhen, hvor Jesus var, og saa ham, faldt hun ned for hans Fødder og sagde til ham: „Herre! havde du været her, da var min Broder ikke død.”
33 Da Yesu ya gan ta tana kuka, da wadannan Yahudawa da suka bi ta, sai ya yi juyayi a ruhu ya damu kuma;
Da nu Jesus saa hende græde og saa Jøderne, som vare komne med hende, græde, harmedes han i Aanden og blev heftigt bevæget i sit Indre; og han sagde:
34 sai ya ce, “A ina kuka kwantar da shi?” Sai suka ce masa, “Ubangiji, zo ka gani.”
„Hvor have I lagt ham?” De sige til ham: „Herre! kom og se!”
35 Yesu ya yi kuka.
Jesus græd.
36 Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake kaunar Li'azaru!”
Da sagde Jøderne: „Se, hvor han elskede ham!”
37 Amma wadansun su suka ce, “Shi wannan mutum da ya iya ba makaho ganin gari, da bai iya hana wannan mutum mutuwa ba?
Men nogle af dem sagde: „Kunde ikke han, som aabnede den blindes Øjne, have gjort, at ogsaa denne ikke var død?”
38 Yesu yana cikin juyayi kuma a cikin kansa, sai ya tafi kabarin. Kabarin a kogo ne an kuma rufe bakinsa da dutse.
Da harmes Jesus atter i sit Indre og gaar hen til Graven. Men det var en Hule, og en Sten laa for den.
39 Sai Yesu ya ce, “A kawar da dutsen.” Matta yar'uwar Li'azaru wanda ya mutu, ta ce wa Yesu, “Ubangiji, Yanzu jikin ya ruba domin ya kai kwana hudu da mutuwa”.
Jesus siger: „Tager Stenen bort!” Martha, den dødes Søster, siger til ham: „Herre! han stinker allerede; thi han har ligget der fire Dage.”
40 Yesu ya ce mata, “Ba na ce maki idan kin gaskata za ki ga daukakar Allah ba?”
Jesus siger til hende: „Sagde jeg ikke, at dersom du tror, skal du se Guds Herlighed?”
41 Sai suka kawar da dutsen. Yesu ya daga idanunsa ya ce, “Uba, na gode maka domin kana ji na.”
Da toge de Stenen bort. Men Jesus opløftede sine Øjne og sagde: „Fader! jeg takker dig, fordi du har hørt mig.
42 Na san kana ji na a kowane lokaci, amma domin wannan taro da ke tsaye kewaye da ni nike wannan magana, domin su bada gaskiya cewa kaine ka aiko ni.”
Jeg vidste vel, at du altid hører mig; men for Skarens Skyld, som staar omkring, sagde jeg det, for at de skulle tro, at du har udsendt mig.”
43 Bayan ya yi wannan magana, sai ya daga murya ya ce, “Li'azaru, ka fito!”
Og da han havde sagt dette, raabte han med høj Røst: „Lazarus, kom herud!”
44 Sai mataccen ya fito; kafafunsa da hannayensa na daure da likkafani, fuskarsa kuma na lullube da tsumma. Yesu ya ce masu, “Ku kwance shi, ya tafi”.
Og den døde kom ud, bunden med Jordeklæder om Fødder og Hænder, og et Tørklæde var bundet om hans Ansigt. Jesus siger til dem: „Løser ham, og lader ham gaa!”
45 To dayawa daga cikin yahudawan da suka zo wurin Maryamu suka kuma ga abinda Yesu ya yi, suka gaskata da shi;
Mange af de Jøder, som vare komne til Maria og havde set, hvad han havde gjort, troede nu paa ham;
46 amma wadansu suka koma wurin farisawa suka fada masu abubuwan da Yesu ya yi.
men nogle af dem gik hen til Farisæerne og sagde dem, hvad Jesus havde gjort.
47 Sai manyan firistoci da farisawa suka tara majalisa wuri guda, suka ce, “menene za mu yi?” Mutumin nan yana alamu masu yawa.
Ypperstepræsterne og Farisæerne sammenkaldte da et Møde af Raadet og sagde: „Hvad gøre vi? thi dette Menneske gør mange Tegn.
48 Idan mun kyale shi haka, duka za su gaskata da shi; Romawa za su zo su kwace wurinmu da al'ummar mu.
Dersom vi lade ham saaledes blive ved, ville alle tro paa ham, og Romerne ville komme og tage baade vort Land og Folk.”
49 Duk da haka, wani daga cikin su wato, Kayafas wanda shine babban firist a wannan shekara, ya ce da su, “baku san komai ba”.
Men en af dem, Kajfas, som var Ypperstepræst i det Aar, sagde til dem:
50 Ba ku lura cewa ya fi maku kyau mutum daya ya mutu domin mutane, a maimakon dukan al'umma ta hallaka.”
„I vide intet; ej heller betænke I, at det er os gavnligt, at eet Menneske dør for Folket, og at ikke det hele Folk skal gaa til Grunde.”
51 Ya fadi wannan ne ba don kansa ba, amma sabo da shine babban firist, ya yi anabci ne cewa ya kamata Yesu ya mutu domin al'ummar;
Men dette sagde han ikke af sig selv; men da han var Ypperstepræst i det Aar, profeterede han, at Jesus skulde dø for Folket;
52 kuma ba don alummar kawai ba, amma domin a tattara 'ya'yan Allah da suke warwatse ko'ina wuri daya.
og ikke for Folket alene, men for at han ogsaa kunde samle Guds adspredte Børn sammen til eet.
53 Tun daga wannan rana suka fara neman hanyar da za su kashe Yesu.
Fra den Dag af raadsloge de derfor om at ihjelslaa ham.
54 Tun daga nan Yesu ya dena tafiya a sarari chikin Yahudawa, amma sai ya koma wani yanki kusa da jeji a wani gari da ake kira Ifraimu. A can kuma ya zamna da almajiransa.
Derfor vandrede Jesus ikke mere frit om iblandt Jøderne, men gik bort derfra ud paa Landet, nær ved Ørkenen, til en By, som kaldes Efraim; og han blev der med sine Disciple.
55 Idin ketarewa na Yahudawa ya yi kusa, da yawa sun tafi Urushalima daga yankin kasar kamin ranar idi domin su tsarkake kan su.
Men Jødernes Paaske var nær; og mange fra Landet gik op til Jerusalem før Paasken for at rense sig.
56 Suka shiga neman Yesu, suna magana da junan su yayin da suke tsaitsaye a haikali, cewa “me kuke tunani? Ba za ya zo idin bane?”
Da ledte de efter Jesus og sagde mellem hverandre, da de stode i Helligdommen: „Hvad mene I? Mon han ikke kommer til Højtiden?”
57 Babban firist da farisawa sun rigaya sun ba da umurni cewa duk inda aka ga Yesu a zo a shaida domin su kama shi.
Men Ypperstepræsterne og Farisæerne havde givet Befaling om, at dersom nogen vidste, hvor han var, skulde han give det til Kende, for at de kunde gribe ham.

< Yohanna 11 >