< Yohanna 1 >

1 A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
Au commencement était le Verbe, et le Verbe était en Dieu, et le Verbe était Dieu.
2 Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
C’est lui qui au commencement était en Dieu.
3 Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
Toutes choses ont été faites par lui; et sans lui rien n’a été fait de ce qui a été fait.
4 A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
En lui était la vie, et la vie était la lumière des hommes;
5 Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
Et la lumière luit dans les ténèbres, et les ténèbres ne l’ont pas comprise.
6 Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
Il y eut un homme envoyé de Dieu dont le nom était Jean.
7 Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
Celui-ci vint comme témoin pour rendre témoignage à la lumière, afin que tous crussent par lui;
8 Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
Il n’était pas la lumière, mais il devait rendre témoignage à la lumière.
9 Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
Celui-là était la vraie lumière, qui illumine tout homme venant en ce monde.
10 Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
Il était dans le monde, et le monde a été fait par lui, et le monde ne l’a pas connu.
11 Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
Il est venu chez lui, et les siens ne l’ont pas reçu.
12 Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
Mais à tous ceux qui l’ont reçu, il a donné le pouvoir d’être faits enfants de Dieu; à ceux qui croient en son nom;
13 Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
Qui ne sont point nés du sang, ni de la volonté de la chair, ni de la volonté de l’homme, mais de Dieu.
14 Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
Et le Verbe a été fait chair, et il a habité parmi nous et nous avons vu sa gloire comme la gloire qu’un fils unique reçoit de son père, plein de grâce et de vérité.
15 Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
Jean rend témoignage de lui, et il crie, disant: Voici celui-ci dont j’ai dit: Celui qui doit venir après moi a été fait avant moi, parce qu’il était avant moi.
16 Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
Et nous avons tous reçu de sa plénitude, et grâce pour grâce;
17 Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
Car la loi a été donnée par Moïse, la grâce et la vérité sont venues par Jésus-Christ.
18 Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
Personne n’a jamais vu Dieu: le Fils unique qui est dans le sein du Père est celui qui l’a fait connaître.
19 Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
Or voici le témoignage de Jean, lorsque les Juifs lui envoyèrent de Jérusalem des prêtres et des lévites pour lui demander: Qui es-tu?
20 Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
Car il confessa, et il ne le nia point; il confessa: Ce n’est pas moi qui suis le Christ.
21 Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
Et ils lui demandèrent: Quoi donc? Es-tu Elie? Et il dit: Non. Es-tu le prophète? Et il répondit: Non.
22 Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
Ils lui dirent donc: Qui es-tu, afin que nous donnions une réponse à ceux qui nous ont envoyés? Que dis-tu de toi-même?
23 Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
Je suis, répondit-il, la voix de celui qui crie dans le désert: Redressez la voie du Seigneur, comme l’a dit le prophète Isaïe.
24 Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
Or ceux qui avaient été envoyés étaient du nombre des pharisiens.
25 “To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
Ils l’interrogèrent encore et lui dirent: Pourquoi donc baptises-tu, si tu n’es ni le Christ, ni Élie, ni le prophète?
26 Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
Jean leur répondit, disant: Moi je baptise dans l’eau, mais il y a au milieu de vous quelqu’un que vous ne connaissez point.
27 shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
C’est lui qui doit venir après moi, qui a été fait avant moi; je ne suis même pas digne de délier la courroie de sa chaussure.
28 Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
Ceci se passa en Béthanie, au-delà du Jourdain où Jean baptisait.
29 Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
Le jour suivant Jean vit Jésus venant à lui, et il dit: Voici l’agneau de Dieu, voici celui qui ôte le péché du monde.
30 Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
C’est celui de qui j’ai dit: Après moi vient un homme qui a été fait avant moi, parce qu’il était avant moi;
31 Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
Et moi je ne le connaissais pas; mais c’est pour qu’il fût manifesté en Israël, que je suis venu baptisant dans l’eau.
32 Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
Jean rendit encore témoignage, disant: J’ai vu l’Esprit descendant sur lui en forme de colombe, et il s’est reposé sur lui.
33 Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
Et moi je ne le connaissais pas; mais celui qui m’a envoyé baptiser dans l’eau m’a dit: Celui sur qui tu verras l’Esprit descendre et se reposer, c’est celui-là qui baptisera dans l’Esprit-Saint.
34 Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
Et je l’ai vu, et j’ai rendu témoignage que c’est lui qui est le Fils de Dieu.
35 Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
Le jour suivant, Jean se trouvait de nouveau avec deux de ses disciples.
36 suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
Et regardant Jésus qui se promenait, il dit: Voilà l’agneau de Dieu.
37 Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
Les deux disciples l’entendirent parler ainsi, et ils suivirent Jésus.
38 Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
Or Jésus s’étant retourné et les voyant qui le suivaient, leur dit: Que cherchez-vous? Ils lui répondirent; Rabbi (ce qui veut dire, par interprétation, Maître), où demeurez-vous?
39 Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
Il leur dit: Venez et voyez. Ils vinrent, et virent où il demeurait, et ils restèrent avec lui ce jour-là: or, il était environ la dixième heure,
40 Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
Or André, frère de Simon-Pierre, était un des deux qui avaient entendu de Jean ce témoignage, et qui avaient suivi Jésus.
41 Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
Or il rencontra d’abord son frère Simon, et lui dit: Nous avons trouvé le Messie (ce qu’on interprète par le Christ).
42 Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
Et il l’amena à Jésus. Et Jésus l’ayant regardé, dit: Tu es Simon, fils de Jona; tu seras appelé Céphas, ce qu’on interprète par Pierre.
43 Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
Le lendemain, Jésus voulut aller en Galilée; il trouva Philippe et lui dit: Suis-moi.
44 Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
Or Philippe était de Bethsaïde, de la même ville qu’André et Pierre.
45 Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
Philippe trouva Nathanaël, et lui dit: Nous avons trouvé celui de qui Moïse a écrit dans la loi et ensuite les prophètes, Jésus, fils de Joseph de Nazareth.
46 Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
Et Nathanaël lui demanda: Peut-il venir de Nazareth quelque chose de bon? Philippe lui répondit: Viens et vois.
47 Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
Jésus vit venir à lui Nathanaël, et il dit de lui: Voici vraiment un Israélite en qui il n’y a point d’artifice.
48 Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
Nathanaël lui demanda: D’où me connaissez-vous? Jésus répondit et lui dit: Avant que Philippe t’appelât, lorsque tu étais sous le figuier, je t’ai vu.
49 Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
Nathanaël lui répondit et dit: Rabbi, vous êtes le Fils de Dieu, vous êtes le roi d’Israël.
50 Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
Jésus répliqua et lui dit: Parce que je t’ai dit: Je t’ai vu sous le figuier, tu crois; tu verras de plus grandes choses.
51 Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”
Et il ajouta: En vérité, en vérité, je vous le dis, vous verrez le ciel ouvert et les anges de Dieu montant et descendant sur le Fils de l’homme.

< Yohanna 1 >