< Yohanna 1 >
1 A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
In the beginning was the Word, and the Word was with God, and the Word was God.
2 Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
The same was in the beginning with God.
3 Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
By Him were all things made, and without Him was not any one thing made that was made.
4 A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
In Him was life, and the life was the light of men.
5 Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
And the light shineth in darkness, and the darkness attained it not.
6 Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
There was a man sent from God, whose name was John:
7 Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
this man came for witness, that he might testify concerning the light, that through him all might believe.
8 Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
He was not that light, but was sent to bear witness of the light.
9 Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
The true light was that which enlightneth every man that cometh into the world.
10 Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
He was in the world, and the world was made by Him, and yet the world knew Him not:
11 Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
yea, He came to his own peculiar right, and even his own people received Him not.
12 Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
But as many as received Him, to them granted He the privilege to become the children of God, even to them that believe on his name;
13 Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
who were born not of blood, nor of the will of the flesh, nor of the will of man, but of God.
14 Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
And the Word was made flesh, and dwelt among us, being full of grace and truth: and we beheld his glory, the glory as of the only-begotten of the Father.
15 Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
Of Him did John bare witness, and publicly declared, saying, This was He of whom I spake, He that cometh after me is preferred before me; for He was before me.
16 Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
And of his fulness have we all received, even grace for grace.
17 Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
For the law was given by Moses, but grace and truth came by Jesus Christ:
18 Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
and though no one hath ever seen God, or can see Him: yet the only-begotten Son, who is in the bosom of the Father, hath made Him known.
19 Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
And this is the testimony of John, when the Jews sent from Jerusalem priests and Levites to ask him, Who art thou?
20 Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
he confessed, and denied not; but declared openly, I am not the Christ.
21 Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
And they asked him, What then? art thou Elias? And he said, I am not. Art thou a prophet? and he answered, No.
22 Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
Therefore said they unto him, Who art thou? that we may give an answer to them that sent us: What dost thou say of thy self?
23 Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
and he said, I am the voice of one crying in the wilderness, "Make straight the way of the Lord," according to Esaias the prophet.
24 Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
Now they that were sent, were of the pharisees:
25 “To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
and they asked him, and said to him, Why then dost thou baptize, if thou art not the Christ, nor Elias, nor a prophet?
26 Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
John answered them, saying, I baptize with water: but there standeth one among you, whom ye know not;
27 shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
that cometh after me, but is preferred before me, the latchet of whose shoe I am not worthy to unloose.
28 Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
These things passed at Bethabara beyond Jordan, where John was baptizing.
29 Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
The next day John seeth Jesus coming towards him, and saith, Behold the Lamb of God that taketh away the sin of the world.
30 Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
This is He of whom I said, After me cometh a man, who is preferred before me: for He was before me.
31 Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
And I knew Him not: but therefore came I baptizing with water, that He might be made known to Israel.
32 Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
And John testified saying, I saw the Spirit descending like a dove from heaven, and it abode upon Him.
33 Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
And I knew Him not: but He that sent me to baptize with water, said unto me, Upon whom thou shalt see the Spirit descending and abiding on Him, the same is he that baptizeth with the Holy Spirit.
34 Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
And I saw it, and therefore testified that this is the Son of God.
35 Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
The day following John was standing, (and two of his disciples, )
36 suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
and looking upon Jesus as He was walking, he saith, "Behold the lamb of God."
37 Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
And when the two disciples heard what he said, they followed Jesus.
38 Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
And Jesus turning, and seeing them following Him, saith unto them, What do ye seek? They said unto Him, Rabbi (that is to say, Master, ) where is thine abode?
39 Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
He saith unto them, Come and see. And they came and saw where He dwelt, and abode with Him that day: and it was about the tenth hour.
40 Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
Now Andrew the brother of Simon Peter, was one of the two that heard what John said, and thereupon followed Jesus.
41 Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
He first meeteth with his own brother Simon, and telleth him, "We have found the Messiah, which is to say, the Christ."
42 Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
And Andrew brought him to Jesus: and Jesus looking at him said, Thou art Simon the son of Jonas, thou shalt be called Cephas; which is interpreted a stone.
43 Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
The day following Jesus had a mind to go out into Galilee, and meeting with Philip, saith unto him, Follow me.
44 Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
Now Philip was of Bethsaida the city of Andrew and Peter.
45 Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
Philip meeting Nathaniel, saith unto him, We have found Him, of whom Moses in the law, and of whom the prophets also wrote, Jesus of Nazareth, the son of Jeseph.
46 Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
And Nathaniel said unto him, Can any thing good come out of Nazareth? Philip replied, Come and see.
47 Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
And when Jesus saw Nathaniel coming towards Him, He saith concerning him, "Behold an Israelite indeed, in whom is no guile."
48 Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
Nathaniel saith unto Him, Whence knowest thou me? Jesus answered him, Before Philip called thee, I saw thee, when under the fig-tree.
49 Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
Nathaniel replied, Rabbi, thou art the Son of God; thou art the king of Israel.
50 Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
Jesus answered and said unto him, Because I told thee that I saw thee under the fig-tree, thou believest: thou shalt see greater things than these.
51 Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”
And He saith unto him, Verily verily I say unto you, Ye shall hereafter see heaven opened, and the angels of God ascending and descending upon the Son of man.