< Yohanna 1 >

1 A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
In the beginning was the Word, and the Word was with God, and the Word was God.
2 Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
He was in the beginning with God.
3 Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
All things were made through him, and apart from him nothing was made that has been made.
4 A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
In him was life, and the life was the light of humanity.
5 Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
And the light shines in the darkness, and the darkness hasn't overcome it.
6 Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
There came a man, sent from God, whose name was John.
7 Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
He came as a witness to testify about the light, that all might believe through him.
8 Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
He was not the light, but was sent that he might testify about the light.
9 Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
The true light that enlightens everyone was coming into the world.
10 Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
He was in the world, and the world was made through him, but the world did not recognize him.
11 Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
He came to his own, and those who were his own did not receive him.
12 Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
But as many as received him, to them he gave the right to become God's children, to those who believe in his name,
13 Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
who were born not of blood, nor of the will of the flesh, nor of the will of man, but of God.
14 Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
And the Word became flesh and lived among us, and we saw his glory, such glory as of the one and only of the Father, full of grace and truth.
15 Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
John testified about him and shouted out, saying, "This was the one of whom I said, 'He who comes after me has surpassed me, for he was before me.'"
16 Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
For of his fullness we all received, and grace upon grace.
17 Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
For the Law was given through Moses, grace and truth came through Jesus (the) Messiah.
18 Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
No one has seen God at any time. The only Son, who is at the Father's side, has made him known.
19 Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
And this is John's testimony, when the Jewish leaders sent priests and Levites from Jerusalem to ask him, "Who are you?"
20 Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
And he confessed, and did not deny, but he confessed, "I am not the Messiah."
21 Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
And they asked him, "What then? Are you Elijah?" And he said, "I am not." "Are you the Prophet?" And he answered, "No."
22 Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
They said therefore to him, "Who are you? Give us an answer to take back to those who sent us. What do you say about yourself?"
23 Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
He said, "I am the voice of one crying in the wilderness, 'Make straight the way of the Lord,' as Isaiah the prophet said."
24 Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
(Now they had been sent from the Pharisees.)
25 “To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
And they asked him, "Why then do you baptize, if you are not the Messiah, nor Elijah, nor the Prophet?"
26 Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
John answered them, saying, "I baptize in water, but among you stands one whom you do not know.
27 shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
He is the one who comes after me, whose sandal strap I'm not worthy to loosen."
28 Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
These things were done in Bethany across the Jordan, where John was baptizing.
29 Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
The next day, he saw Jesus coming to him, and said, "Look, the Lamb of God, who takes away the sin of the world.
30 Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
This is he of whom I said, 'After me comes a man who ranks ahead of me, because he existed before me.'
31 Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
I did not know him, but for this reason I came baptizing in water: that he would be revealed to Israel."
32 Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
And John testified, saying, "I saw the Spirit descending like a dove out of heaven, and it remained on him.
33 Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
And I did not recognize him, but he who sent me to baptize in water, he said to me, 'On whomever you will see the Spirit descending, and remaining on him, this is he who baptizes in the Holy Spirit.'
34 Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
And I have seen and have testified that this is the Chosen One of God."
35 Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
Again, the next day, John was standing with two of his disciples,
36 suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
and he looked at Jesus as he walked, and said, "Look, the Lamb of God."
37 Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
And the two disciples heard him say this, and they followed Jesus.
38 Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
And Jesus turned and saw them following, and said to them, "What are you looking for?" They said to him, "Rabbi" (which translated means Teacher), "where are you staying?"
39 Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
He said to them, "Come, and you will see." They came and saw where he was staying, and they stayed with him that day. It was about four in the afternoon.
40 Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
One of the two who heard John, and followed him, was Andrew, Simon Peter's brother.
41 Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
He first found his own brother, Simon, and said to him, "We have found the Messiah." (which is translated, Anointed One).
42 Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
He brought him to Jesus. Jesus looked at him, and said, "You are Simon the son of John. You will be called Cephas" (which is translated, Peter).
43 Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
On the next day, he was determined to go out into Galilee, and he found Philip. And Jesus said to him, "Follow me."
44 Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
Now Philip was from Bethsaida, of the city of Andrew and Peter.
45 Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
Philip found Nathanael, and said to him, "We have found him of whom Moses in the Law and the Prophets wrote: Jesus of Nazareth, the son of Joseph."
46 Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
And Nathanael said to him, "Can any good thing come out of Nazareth?" Philip said to him, "Come and see."
47 Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
Jesus saw Nathanael coming to him, and said about him, "Look, a true Israelite in whom there is no deceit."
48 Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
Nathanael said to him, "How do you know me?" Jesus answered him, "Before Philip called you, when you were under the fig tree, I saw you."
49 Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
Nathanael answered him, "Rabbi, you are the Son of God. You are King of Israel."
50 Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
Jesus answered him, "Because I told you, 'I saw you underneath the fig tree,' do you believe? You will see greater things than these."
51 Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”
And he said to him, "Truly, truly, I tell you, you will see heaven opened, and the angels of God ascending and descending on the Son of Man."

< Yohanna 1 >