< Yohanna 1 >
1 A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
In the beginning was the Word, and the Word was with God, and the Word was God.
2 Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
The same was in the beginning with God.
3 Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
All things were made by him; and without him was not any thing made that was made.
4 A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
In him was life; and the life was the light of men.
5 Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
And the light shines in darkness; and the darkness comprehended it not.
6 Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
There was a man sent from God, whose name was John.
7 Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
The same came for a witness, to bear witness of the Light, that all men through him might believe.
8 Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
He was not that Light, but was sent to bear witness of that Light.
9 Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
That was the true Light, which lights every man that comes into the world.
10 Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
He was in the world, and the world was made by him, and the world knew him not.
11 Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
He came to his own, and his own received him not.
12 Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
But as many as received him, to them gave he power to become the sons of God, even to them that believe on his name:
13 Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
Which were born, not of blood, nor of the will of the flesh, nor of the will of man, but of God.
14 Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
And the Word was made flesh, and dwelled among us, (and we beheld his glory, the glory as of the only begotten of the Father, ) full of grace and truth.
15 Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
John bore witness of him, and cried, saying, This was he of whom I spoke, He that comes after me is preferred before me: for he was before me.
16 Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
And of his fullness have all we received, and grace for grace.
17 Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
For the law was given by Moses, but grace and truth came by Jesus Christ.
18 Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
No man has seen God at any time, the only begotten Son, which is in the bosom of the Father, he has declared him.
19 Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
And this is the record of John, when the Jews sent priests and Levites from Jerusalem to ask him, Who are you?
20 Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
And he confessed, and denied not; but confessed, I am not the Christ.
21 Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
And they asked him, What then? Are you Elias? And he says, I am not. Are you that prophet? And he answered, No.
22 Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
Then said they to him, Who are you? that we may give an answer to them that sent us. What say you of yourself?
23 Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
He said, I am the voice of one crying in the wilderness, Make straight the way of the Lord, as said the prophet Isaiah.
24 Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
And they which were sent were of the Pharisees.
25 “To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
And they asked him, and said to him, Why baptize you then, if you be not that Christ, nor Elias, neither that prophet?
26 Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
John answered them, saying, I baptize with water: but there stands one among you, whom you know not;
27 shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
He it is, who coming after me is preferred before me, whose shoe’s lace I am not worthy to unloose.
28 Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
These things were done in Bethabara beyond Jordan, where John was baptizing.
29 Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
The next day John sees Jesus coming to him, and says, Behold the Lamb of God, which takes away the sin of the world.
30 Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
This is he of whom I said, After me comes a man which is preferred before me: for he was before me.
31 Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
And I knew him not: but that he should be made manifest to Israel, therefore am I come baptizing with water.
32 Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
And John bore record, saying, I saw the Spirit descending from heaven like a dove, and it stayed on him.
33 Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
And I knew him not: but he that sent me to baptize with water, the same said to me, On whom you shall see the Spirit descending, and remaining on him, the same is he which baptizes with the Holy Ghost.
34 Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
And I saw, and bore record that this is the Son of God.
35 Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
Again the next day after John stood, and two of his disciples;
36 suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
And looking on Jesus as he walked, he says, Behold the Lamb of God!
37 Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
And the two disciples heard him speak, and they followed Jesus.
38 Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
Then Jesus turned, and saw them following, and says to them, What seek you? They said to him, Rabbi, (which is to say, being interpreted, Master, ) where dwell you?
39 Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
He says to them, Come and see. They came and saw where he dwelled, and stayed with him that day: for it was about the tenth hour.
40 Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
One of the two which heard John speak, and followed him, was Andrew, Simon Peter’s brother.
41 Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
He first finds his own brother Simon, and says to him, We have found the Messias, which is, being interpreted, the Christ.
42 Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
And he brought him to Jesus. And when Jesus beheld him, he said, You are Simon the son of Jona: you shall be called Cephas, which is by interpretation, A stone.
43 Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
The day following Jesus would go forth into Galilee, and finds Philip, and says to him, Follow me.
44 Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
Now Philip was of Bethsaida, the city of Andrew and Peter.
45 Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
Philip finds Nathanael, and says to him, We have found him, of whom Moses in the law, and the prophets, did write, Jesus of Nazareth, the son of Joseph.
46 Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
And Nathanael says to him, Can there any good thing come out of Nazareth? Philip said to him, Come and see.
47 Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
Jesus saw Nathanael coming to him, and says of him, Behold an Israelite indeed, in whom is no guile!
48 Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
Nathanael says to him, From where know you me? Jesus answered and said to him, Before that Philip called you, when you were under the fig tree, I saw you.
49 Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
Nathanael answered and says to him, Rabbi, you are the Son of God; you are the King of Israel.
50 Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
Jesus answered and said to him, Because I said to you, I saw you under the fig tree, believe you? you shall see greater things than these.
51 Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”
And he says to him, Truly, truly, I say to you, Hereafter you shall see heaven open, and the angels of God ascending and descending on the Son of man.