< Yohanna 1 >

1 A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
In the beginning was the Word, and the Word was with God, and the Word was God.
2 Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
The same was in the beginning with God.
3 Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
All things were made by him: and without him was made nothing that was made.
4 A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
In him was life, and the life was the light of men.
5 Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
And the light shineth in darkness, and the darkness did not comprehend it.
6 Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
There was a man sent from God, whose name was John.
7 Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
This man came for a witness, to give testimony of the light, that all men might believe through him.
8 Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
He was not the light, but was to give testimony of the light.
9 Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
That was the true light, which enlighteneth every man that cometh into this world.
10 Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
He was in the world, and the world was made by him, and the world knew him not.
11 Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
He came unto his own, and his own received him not.
12 Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
But as many as received him, he gave them power to be made the sons of God, to them that believe in his name.
13 Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
Who are born, not of blood, nor of the will of the flesh, nor of the will of man, but of God.
14 Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
And the Word was made flesh, and dwelt among us, (and we saw his glory, the glory as it were of the only begotten of the Father, ) full of grace and truth.
15 Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
John beareth witness of him, and crieth out, saying: This was he of whom I spoke: He that shall come after me, is preferred before me: because he was before me.
16 Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
And of his fulness we all have received, and grace for grace.
17 Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
For the law was given by Moses; grace and truth came by Jesus Christ.
18 Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
No man hath seen God at any time: the only begotten Son who is in the bosom of the Father, he hath declared him.
19 Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
And this is the testimony of John, when the Jews sent from Jerusalem priests and Levites to him, to ask him: Who art thou?
20 Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
And he confessed, and did not deny: and he confessed: I am not the Christ.
21 Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
And they asked him: What then? Art thou Elias? And he said: I am not. Art thou the prophet? And he answered: No.
22 Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
They said therefore unto him: Who art thou, that we may give an answer to them that sent us? What sayest thou of thyself?
23 Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
He said: I am the voice of one crying out in the wilderness, make straight the way of the Lord, as said the prophet Isaias.
24 Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
And they that were sent, were of the Pharisees.
25 “To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
And they asked him, and said to him: Why then dost thou baptize, if thou be not Christ, nor Elias, nor the prophet?
26 Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
John answered them, saying: I baptize with water; but there hath stood one in the midst of you, whom you know not.
27 shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
The same is he that shall come after me, who is preferred before me: the latchet of whose shoe I am not worthy to loose.
28 Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
These things were done in Bethania, beyond the Jordan, where John was baptizing.
29 Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
The next day, John saw Jesus coming to him, and he saith: Behold the Lamb of God, behold him who taketh away the sin of the world.
30 Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
This is he, of whom I said: After me there cometh a man, who is preferred before me: because he was before me.
31 Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
And I knew him not, but that he may be made manifest in Israel, therefore am I come baptizing with water.
32 Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
And John gave testimony, saying: I saw the Spirit coming down, as a dove from heaven, and he remained upon him.
33 Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
And I knew him not; but he who sent me to baptize with water, said to me: He upon whom thou shalt see the Spirit descending, and remaining upon him, he it is that baptizeth with the Holy Ghost.
34 Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
And I saw, and I gave testimony, that this is the Son of God.
35 Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
The next day again John stood, and two of his disciples.
36 suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
And beholding Jesus walking, he saith: Behold the Lamb of God.
37 Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
And the two disciples heard him speak, and they followed Jesus.
38 Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
And Jesus turning, and seeing them following him, saith to them: What seek you? Who said to him, Rabbi, (which is to say, being interpreted, Master, ) where dwellest thou?
39 Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
He saith to them: Come and see. They came, and saw where he abode, and they stayed with him that day: now it was about the tenth hour.
40 Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
And Andrew, the brother of Simon Peter, was one of the two who had heard of John, and followed him.
41 Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
He findeth first his brother Simon, and saith to him: We have found the Messias, which is, being interpreted, the Christ.
42 Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
And he brought him to Jesus. And Jesus looking upon him, said: Thou art Simon the son of Jona: thou shalt be called Cephas, which is interpreted Peter.
43 Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
On the following day, he would go forth into Galilee, and he findeth Philip. And Jesus saith to him: Follow me.
44 Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
Now Philip was of Bethsaida, the city of Andrew and Peter.
45 Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
Philip findeth Nathanael, and saith to him: We have found him of whom Moses in the law, and the prophets did write, Jesus the son of Joseph of Nazareth.
46 Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
And Nathanael said to him: Can any thing of good come from Nazareth? Philip saith to him: Come and see.
47 Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
Jesus saw Nathanael coming to him: and he saith of him: Behold an Israelite indeed, in whom there is no guile.
48 Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
Nathanael saith to him: Whence knowest thou me? Jesus answered, and said to him: Before that Philip called thee, when thou wast under the fig tree, I saw thee.
49 Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
Nathanael answered him, and said: Rabbi, thou art the Son of God, thou art the King of Israel.
50 Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
Jesus answered, and said to him: Because I said unto thee, I saw thee under the fig tree, thou believest: greater things than these shalt thou see.
51 Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”
And he saith to him: Amen, amen I say to you, you shall see the heaven opened, and the angels of God ascending and descending upon the Son of man.

< Yohanna 1 >