< Yaƙub 5 >

1 Ku zo yanzu, ku da kuke masu arziki, ku yi ta kuka da kururuwa domin bakin ciki iri-iri da ke zuwa gare ku.
Og nu, I rige! græder og jamrer over de Ulykker, som komme over eder.
2 Arzikin ku ya rube, tufafinku kuma duk cin asu ne.
Eders Rigdom er rådnet, og eders Klæder er mølædte;
3 Zinariya da azurfarku sun yi tsatsa. Tsatsar su kuwa zai zama shaida a kanku. Zai cinye naman ku kamar wuta. Kun yi ajiyar dukiyarku domin ranakun karshe.
eders Guld og Sølv er rustet op, og deres Rust skal være til Vidnesbyrd imod eder og æde eders Kød som en Ild; I have samlet Skatte i de sidste Dage.
4 Duba, hakin ma'aikata yana kuka - hakin da kuka hana wa wadanda suka girbe maku gonaki. Kuma kukan masu girbin ya tafi ya kai ga kunnuwan Ubangiji mai Runduna.
Se, den Løn skriger, som I have forholdt Arbejderne, der høstede eders Marker, og Høstfolkenes Råb ere komne ind for den Herre Zebaoths Øren.
5 Kun yi zama cikin annashuwa a duniya kuma kun tsunduma kanku. Kun sa zukatan ku sun yi kiba domin ranar yanka.
I levede i Vellevned på Jorden og efter eders Lyster; I gjorde eders Hjerter til gode som på en Slagtedag.
6 Kun hukunta kuma kun kashe adalin mutum. Bai kuwa yi tsayayya da ku ba.
I domfældte, I dræbte den retfærdige; han står eder ikke imod.
7 Saboda haka ku yi hakuri, 'yan'uwa, har sai zuwan Ubangiji. Duba, yadda manomi ya kan jira kaka mai amfani daga gona. Da hakuri yake jiran ta har sai ta karbi ruwa na fari da na karshe.
Derfor, værer tålmodige, Brødre! indtil Herrens Tilkommelse. Se, Bonden venter på Jordens dyrebare Frugt og bier tålmodigt efter den, indtil den får tidlig Regn og sildig Regn.
8 Ku, ma, ku yi hakuri. Ku karfafa zukatan ku, domin zuwan Ubangiji ya yi kusa.
Værer også I tålmodige, styrker eders Hjerter; thi Herrens Tilkommelse er nær.
9 Kada ku yi gunaguni, 'Yan'uwana, game da juna, don kada a hukunta ku. Duba, mai shari'a na tsaye a bakin kofa.
Sukker ikke imod hverandre, Brødre! for at I ikke skulle dømmes; se, Dommeren står for Døren.
10 Dauki misali, 'yan'uwa, daga shan wuya da hakurin annabawa, wadanda suka yi magana a cikin sunan Ubangiji.
Brødre! tager Profeterne, som have talt i Herrens Navn, til Forbillede på at lide ondt og være tålmodige.
11 Duba, mukan kira wadanda suka jimre masu albarka. Kun dai ji irin jimiri da Ayuba ya yi, kun kuma san nufin Ubangiji, yadda yake mai yawan tausayi da jinkai.
Se, vi prise dem salige, som have holdt ud. I have hørt om Jobs Udholdenhed og vide Udfaldet fra Herren; thi Herren er såre medlidende og barmhjertig.
12 Fiye da komai duka, 'yan'uwana, kada ku yi rantsuwa, ko da sama, ko da kasa, ko da kowace irin rantsuwa ma. A maimakon haka bari “I” ya zama “I”, in kuwa kun ce “A'a”, ya zama “A'a”, don kada ku fada a cikin hukunci.
Men for alting, mine Brødre! sværger ikke, hverken ved Himmelen eller ved Jorden eller nogen anden Ed; men eders Ja være Ja, og Nej være Nej, for at I ikke skulle falde under Dom.
13 Akwai wanda ke fama a tsakanin ku? Sai ya yi addu'a, akwai wanda yake murna? Sai ya raira wakar yabo.
Lider nogen iblandt eder ondt, han bede; er nogen vel til Mode, han synge Lovsang!
14 Akwai mara lafiya a tsakanin ku? Sai ya kira dattawan ikilisiya, sai su yi masa addu'a. Suna shafa masa mai a cikin sunan Ubangiji.
Er nogen iblandt eder syg, han kalde Menighedens Ældste til sig, og de skulle bede over ham og salve ham med Olie i Herrens Navn.
15 Addu'ar bangaskiya zai warkar da mara lafiyan, Ubangiji zai tashe shi. Idan ma ya yi zunubi, Allah zai gafarta masa.
Og Troens Bøn skal frelse den syge, og Herren skal oprejse ham, og har han gjort Synder, skulle de forlades ham.
16 Soboda haka, ku furta zunuban ku ga juna, kuna yi wa juna addu'a, don a warkar da ku. Addu'ar mai adalci tana da karfin aiki kwarai da gaske.
Bekender derfor Synderne for hverandre og beder for hverandre, for at I må blive helbredte; en retfærdigs Bøn formår meget, når den er alvorlig.
17 Iliya dan Adam ne kamar mu. Amma da ya nace da addu'a kada a yi ruwa, ba kuma yi ruwa a kasar ba har shekara uku da wata shida.
Elias var et Menneske, lige Vilkår undergivet med os, og han bad en Bøn, at det ikke måtte regne; og det regnede ikke på Jorden i tre År og seks Måneder.
18 Sai Iliya ya sake yin addu'a. Sammai suka ba da ruwa, kasa kuma ta ba da amfanin ta.
Og han bad atter, og Himmelen gav Regn, og Jorden bar sin Frugt.
19 Ya ku 'yan'uwana, idan wanin ku ya baude wa gaskiya, wani kuma ya dawo da shi,
Mine Brødre! dersom nogen iblandt eder farer vild fra Sandheden, og nogen omvender ham,
20 wannan mutum ya sani cewa, duk wanda ya dawo da mai zunubi a hanya daga baudewar sa, zai cece shi daga mutuwa, kuma zai rufe dunbin zunubai.
han vide, at den, som omvender en Synder fra hans Vejs Vildfarelse, han Frelser en Sjæl fra Døden og skjuler en Mangfoldighed af Synder.

< Yaƙub 5 >