< Yaƙub 4 >
1 Me ke kawo gaba da rashin jituwa a tsakanin ku? Ba yana tasowa ne daga muguwar sha'awa da ke yaki a cikin ku ba?
Where do the wars and disputes among you come from? Is it not precisely from your pleasures, the ones at war in your members?
2 Kuna sha'awa, kuma ba ku da shi. Kuna kisa da kyashi, kuma ba za ku iya samu ba. Kuna danbe da fada. Har wa yau baku samu ba domin baku tambaya ba.
You crave and do not have; you murder and covet and are not able to obtain; you fight and war. You do not have because you do not ask.
3 Kun roka kuma ba a baku ba saboda kuna roko ta hanya mara kyau, kuna so ku yi amfani da shi domin miyagun sha'awoyin ku.
You ask and do not receive because you ask wrongly, so that you may lavish it on your pleasures.
4 Ku mazinata! Baku sani ba, abokantaka da duniya, tawaye ne ga Allah? Don haka duk wanda ya shiga abokantaka da duniya ya zama magabcin Allah.
Adulterers and adulteresses! Do you not know that friendship with the world is enmity with God? So whoever may want to be a friend of the world makes himself an enemy of God.
5 Ko kuna zaton nassi ya fadi haka a banza ne, “Ruhun nan da ke a cikinmu yana da kishi matuka?”
Or do you suppose that the Scripture says in vain that the Spirit who dwells in us yearns jealously?
6 Amma Allah ya bayar da karin alheri, shi ya sa nassi ya ce, “Allah yana gaba da mai girman kai, Amma yana ba da alheri ga mai tawaliu.”
But He gives greater grace; therefore He says: “God resists proud ones, but gives grace to humble ones.”
7 Saboda haka ku mika kan ku ga Allah. Ku yi tsayayya da shaidan, zai kuma guje maku.
Therefore submit to God. Resist the devil and he will flee from you.
8 Ku matso kusa da Allah, shi kuma za ya matsa kusa da ku. Wanke hannayen ku, ku masu zunubi, ku tsabtace zukatan ku, ku masu zuciya biyu.
Draw near to God and He will draw near to you. Sinners, cleanse your hands! Double-minded, purify your hearts!
9 Ku yi bakin ciki, makoki, da kuka! Ku mayar da dariyar ku ta koma bakin ciki, farin cikinku kuma zuwa ga bakin ciki.
Lament and mourn and weep! Let your laughter be turned into mourning, and your joy into dejection.
10 Ku kaskantar da kanku a gaban Ubangiji, shi kuma za ya daukaka ku.
Humble yourself before the Lord and He will exalt you.
11 Kada ku rika zargin juna, 'yan'uwa. Wanda ya ke zargin dan'uwa ko shari'anta dan'uwansa, yana zargin shari'a kuma yana hukunta shari'a. Idan ka hukunta shari'a, ya nuna ba ka biyayya da shari'ar, amma mai hukunci.
Brothers, do not speak evil of one another. Because the one speaking against a brother and judging his brother speaks against a law and judges a law. So if you judge a law you are not a law-doer but a judge.
12 Mai ba da shari'a da yin hukunci daya ne. Shine mai iya ceto kuma ya hallakar. Kai wanene, da ke hukunta makwafcin ka?
The Lawgiver and Judge is One, the one who is able to save and to destroy. So who are you (sg) to be judging someone who is different?
13 Saurara, ku da kuke cewa, “Yau ko gobe za mu tafi wancan birnin mu yi shekara guda a wurin, muna kasuwanci, mu kuma yi riba.”
Come now, you who say, “Today and tomorrow let us travel to that certain city, spend a year there, do business and make a profit;”
14 Wa ya san abin da zai faru gobe, kuma yaya rayuwan ka zai kasance? Kai kamar hazo ne mai bayyana bayan dan lokaci kadan ya bace.
whereas you do not know anything about the morrow. For what is our life? It is even a vapor that appears for a little time but then vanishes away.
15 Maimakon haka, sai ka ce, “Idan Ubangiji ya nufa, za mu rayu kuma mu yi wannan ko wancan.”
Instead you ought to say, “If the Lord wills, we will live and do this or that.”
16 Amma yanzu kana fahariya da shirye shiryen ka na takama. Irin wannan fahariya, mugunta ce.
But now you boast in your arrogant pretensions. All such boasting is malignant.
17 Saboda haka ga wanda ya san abin da ya kamata ya aikata amma bai yi ba, ya zama zunubi a gare shi.
Therefore, to the one knowing to do good and not doing it, to him it is sin.