< Ibraniyawa 2 >
1 Saboda haka, lalle ne mu kara mai da hankali musamman da abubuwan da mu ka ji, don kada mu yi sakaci, su sullube mana.
For this reason we must pay the more earnest heed to the things which we have heard, for fear we should drift away.
2 Idan kuwa maganar nan da aka fada ta bakin mala'iku ta zama tabbatacciya, har kowanne keta umarni da rashin biyayya, suka gamu da sakamakonsu wanda ya kamace su,
For if the word uttered through angels stood firm, so that every transgression and act of disobedience met with its just retribution, how shall we escape if we neglect so great a salvation?
3 ta kaka za mu tsira, in mun ki kula da ceto mai girma haka? Domin Ubangiji da kansa, shi ne ya fara sanar da shi, wadanda suka saurare shi kuma suka tabbatar mana da shi.
Which having begun to be spoken by the Lord, was confirmed to us by those who heard him;
4 San'nan kuma Allah da kansa ya shaida ta wasu alamu, da abubuwan al'ajabai, da mu'ajizai iri iri, da kuma baiwar Ruhu Mai Tsarki dabam dabam da ya rarraba kamar yadda ya nufa.
God himself corroborating their testimony by signs and wonders and a variety of miraculous powers, and by gifts of the Holy Spirit imparted in accordance with his own will.
5 Ai ba ga mala'iku ba ne Allah ya sa mulkin duniyar nan da za a yi, wanda muke zance.
It is not to angels that God subjected the age to be, of which we are speaking.
6 Amma wani ya shaida a wani wuri cewa, 'Mutum ma menene, har da za ka tuna da shi? Ko dan mutum ma, har da za ka kula da shi?'
But some one, somewhere, testified, saying. What is Man, that thou art mindful of him? Or any man, that thou carest for him?
7 Ka sa mutum ya gaza mala'iku; Ka nada shi da daukaka da girma. Bisa dukkan hallitta.
Thou hast made him only a little lower that the angels; With glory and honor hast thou crowned him; And hast set him to govern the works of thy hands;
8 Ka dora shi a kan dukkan halittarka, ka kuma mallakar da kome a karkashin sawayensa. Domin Allah ya mallakar da dukkan abubuwa a karkashinsa. Bai bar kome a kebe ba. Amma kuwa har a yanzu ba mu ga yana sarrafa dukkan abubuwa ba tukuna.
Thou hast put all things under his feet. For this putting all things under man means leaving nothing not subject to him. But we do not yet see all things subject to him.
9 Amma mun ga wani wanda dan lokaci aka sa shi ya gaza mala'iku, shine Yesu, an nada shi da daukaka da girma, saboda shan wuyarsa ta mutuwa, wanan kuwa duk ta wurin alherin Allah ne Yesu ya mutu saboda kowa.
What we do see is Jesus, who was made for a time a little lower than the angels, now crowned with glory and honor, because of the suffering of death, in order that through God’s grace he might taste death for every man.
10 Saboda haka, ya dace ga Allah, shi da dukkan abubuwa suka kasance domin sa, ta gare shi, domin ya kawo 'ya'ya masu yawa ga samun daukaka. Domin a kammala cetonsu ta wurin shan wuyarsa.
For it befitted him, for whom and through whom all things exist, in bringing many sons to glory, to make the Pioneer of their salvation perfect through sufferings.
11 Domin da shi mai tsarkakewar da kuma wadanda aka tsarkaken, duk tushensu daya ne. Saboda wanan dalili ne shi ya sa ba ya jin kunyar kiran su 'ya'uwansa.
For both he who sanctifies and those whom he is sanctifying are all from One; for which reason he is not ashamed to call them brothers, saying.
12 Da yace, ''zan sanar da sunanka ga ya'uwana, a tsakiyar taronsu zan yabe ka da waka.''
I will proclaim thy name to my brothers; In the midst of the Church I will hymn thy praises.
13 Har wa yau, yace, ''Zan dogara a gare shi.'' Da kuma ''Ga ni nan, ni da 'ya'yan da Allah ya ba ni.''
And again, I myself will put my trust in God. And again, Lo, I and the children God has given me.
14 Wato tun da yake 'ya'yan Allah duk suna da nama da jini, Yesu ma ya dauki kamannin haka, ta wurin mutuwa ya hallakar da mai ikon mutuwa, wato Iblis.
Therefore, since the children are sharers in flesh and blood, he also similarly partook of the same, in order that through death he might render powerless him that had the power of death, that is, the devil;
15 Ya kuma 'yanta duk wadanda tun haihuwarsu suke zaman bauta sabo da tsoron mutuwa.
And might deliver those who through fear of death had been subject to life-long bondage.
16 Don hakika ba mala'iku yake taimako ba, a'a, zuriyar Ibrahim ne yake taimako.
For assuredly it is not angels, nay, it is the offspring of Abraham, whom he is ever taking by the hand.
17 Saboda haka, lalle ne ya zama kamar yan'uwansa ta kowacce hanya, domin ya zama babban Firist, mai jinkai, mai aminci kuma na al'amarin Allah, ya kuma mika hadayar sulhu ta gafarta zunuban jama'a.
And so it was necessary that he should in all points be made like his brothers, so that he might become a compassionate and faithful high priest, in all that relates to God, to make reconciliation for the sins of the people.
18 Tun da yake Yesu ma da kansa ya sha wahala, sa'adda aka gwada shi, don haka, zai taimaki wadanda ake yi wa gwaji.
For inasmuch as he himself has suffered, being tempted, he is also able instantly to succor those who are tempted, he is also able instantly to succor those who are tempted.