< Ibraniyawa 1 >

1 A zamanin da, Allah ya yi wa kakanin kakanninmu magana ta hanyoyi ma su yawa iri iri, ta bakin annabawa.
Efterat Gud fordum hadde talt mange ganger og på mange måter til fedrene ved profetene,
2 Amma a zamanin nan na karshe, ya yi mana magana ta wurin Dansa, wanda ya sa magajin kome, wanda ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn g165)
så har han i disse siste dager talt til oss ved Sønnen, som han har satt til arving over alle ting, ved hvem han og har gjort verden, (aiōn g165)
3 Shi ne hasken daukakar Allah, ainihin kamanin zatinsa. Ya na rike da dukkan abubuwa ta ikon kalmarsa. Bayan da ya tsarkake zunubanmu, sai ya zauna a hannun dama na madaukaki a can sama.
han som er avglansen av hans herlighet og avbilledet av hans vesen og bærer alle ting ved sin krafts ord, og som derfor, da han hadde gjort renselse for våre synder, satte sig ved Majestetens høire hånd i det høie,
4 Ta haka ya ke da fifiko a kan mala'iku, kamar yadda sunansa da ya gada yake da fifiko nesa a kan nasu.
og er blitt så meget større enn englene som han har arvet et herligere navn fremfor dem.
5 Domin kuwa wanene a cikin mala'iku Allah ya taba cewa, “Kai Da na ne, yau na zama Uba a gare ka?'' kuma, “Zan kasance Uba a gareshi, shi kuma, zai kasance Da a gare ni?''
For til hvem av englene har han nogen tid sagt: Du er min sønn, jeg har født dig idag, og atter: Jeg vil være ham en far, og han skal være mig en sønn?
6 Kuma, da Allah ya kawo magaji a duniya, sai ya ce, “Dukan mala'ikun Allah su yi masa sujada.”
Men når han atter fører den førstefødte inn i verden, sier han: Og alle Guds engler skal tilbede ham.
7 A game da mala'iku kuma sai ya ce, “yakan mai da mala'ikunsa ruhohi, masu hidimarsa kuma harsunan wuta.
Og om englene sier han: Han som gjør sine engler til vinder og sine tjenere til ildslue,
8 A game da Dan, ya ce “kursiyinka, ya Allah, na har abada abadin ne. Sandar sarautarka sanda ce ta tsantsar gaskiya. (aiōn g165)
men om Sønnen: Din trone, Gud, står i all evighet, og rettvishets kongestav er ditt rikes kongestav; (aiōn g165)
9 Ka kaunaci aikin adalci, ka ki aikin sabo. Saboda haka Allah, wato Allahnka, ya shafe ka da man farin ciki fiye da tsararrakinka.”
du elsket rettferd og hatet urett; derfor har, Gud, din Gud salvet dig med gledens olje fremfor dine medbrødre.
10 “Tun farko, Ubangiji, kai ne ka hallici duniya. Sammai kuma aikin hannayenka ne.
Og: Du, Herre, grunnfestet i begynnelsen jorden, og himlene er dine henders verk;
11 Za su hallaka, amma kai madawwami ne. Duk za su tsufa kamar tufafi.
de skal forgå, men du blir, og de skal alle eldes som et klædebon,
12 Za ka nade su kamar mayafi, za su kuma sauya, amma kai kana nan ba sakewa, Har abada shekarunka ba za su kare ba.”
og som en kåpe skal du rulle dem sammen, og de skal omskiftes; men du er den samme, og dine år skal ikke få ende.
13 Amma wanene a cikin mala'ikun Allah ya taba cewa, “Zauna a hannun dama na, sai na sa makiyanka a karkashin kafafunka?''
Men til hvem av englene har han nogen tid sagt: Sett dig ved min høire hånd, til jeg får lagt dine fiender til skammel for dine føtter?
14 Ashe, ba dukkan mala'iku bane ruhohi, wadanda Allah yakan aika, don su yi wa wadanda za su gaji ceto hidima?
Er de ikke alle tjenende ånder, som sendes ut til tjeneste for deres skyld som skal arve frelse?

< Ibraniyawa 1 >