< Galatiyawa 6 >
1 'Yan'uwa, idan an kama mutum yana yin wani laifi, ku da kuke da ruhaniya sai ku dawo da mutumin a hanya cikin ruhun tawali'u, ka lura da kanka don kada kai ma ka fada a cikin gwaji.
Even if any one should be overtaken in a fault, brothers, you that are spiritual ought, in a gentle spirit, to restore such a one, each one of you looking to himself, lest you too be tempted.
2 Ku dauki damuwar juna, ta yin haka za ku cika shari'ar Almasihu.
Ever be bearing one another’s burdens, and so be fulfilling the law of Christ.
3 Domin idan kowa ya zacci shi wani abu ne alhali shi ba komai ba ne rudin kansa yake yi.
If a man fancies himself to be somebody when he is really nobody he is deceiving himself.
4 Sai kowa ya auna aikin sa. Sa'annan zai sami abin da zai yi takama, ba sai ya kwatanta kansa da wani ba.
Let each one test his own work, and he will then have something to be proud of by comparing himself with himself, and not with any one else;
5 Domin kowa zai dauki nauyin kayansa.
for every one must carry his own pack load.
6 Wanda aka koya masa maganar, wajibi ne ya ci amfanin abubuwansa masu kyau duka tare da malaminsa.
He, however, who is being taught in the message, should always share with his instructor in all the good things which he possesses.
7 Kada fa a yaudare ku ba a yi wa Allah ba'a. Dukan abin da mutum ya dasa, shine abin da zai girba.
Be not deceived. God is not mocked. Whatever a man sows, that will he also reap.
8 Domin shi wanda ya shuka wa kansa dabi'ar zunubi zai girbi hallaka, amma shi wanda ya shuka cikin Ruhu, zai girbi rai madawwami daga Ruhu. (aiōnios )
The man who is sowing to his flesh will of the flesh reap corruption; but he who is sowing to the Spirit will of the Spirit reap life eternal. (aiōnios )
9 Kada mu gaji da aikata nagarta, domin a lokacin da ya dace za mu yi girbi idan ba mu gaji ba.
And let us not be weary in well-doing, for in due season we shall reap if we faint not.
10 Saboda haka, lokacin da muke da zarafi, sai mu yi nagarta ga kowa. Mu yi nagarta mussamman ga wadanda suke na iyalin bangaskiya.
So then, as we have opportunity, let is do good to all men, but especially to those who are of the household of faith.
11 Dubi yawan wasikun da na rubuta maku da hannuna.
See with what large letters I have written to you in my own handwriting!
12 Wadanda suke so su nuna hali mai kyau cikin jiki suke tilasta ku yin kaciya. Suna yin haka ne kadai saboda kada a tsananta masu saboda gicciyen Almasihu.
Those who are trying to compel you to be circumcised are such as wish to make a fair show in the flesh, only that they may not suffer persecution for the cross of Christ.
13 Domin ko su wadanda suke masu kaciya ba su kiyaye shari'a. Maimakon haka suna so ne a yi maku kaciya don su yi fahariya game jikinku.
Even those who are being circumcised, are not themselves keeping the Law, but they want you to be circumcised so that they may glory in your flesh.
14 Bari kada ya zama ina fahariya sai dai ta gicciyen Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurinsa ne aka gicciye duniya a gare ni, ni kuma ga duniya.
God forbid that I should glory in anything except in the cross of our Lord Jesus Christ, upon which the world has been crucified to me and I have been crucified to the world.
15 Domin kaciya ko rashin kaciya ba komai ba ne. Maimakon haka, sabon halita ne ke da muhimmanci.
For in Jesus Christ neither is circumcision anything, nor uncircumcision, but a new creation.
16 Ga dukan wadanda za su zauna cikin wannan ka'ida, bari salama da jinkai su kasance tare da su da kuma bisa Isra'ila na Allah.
On all who will govern their lives by this rule and on the Israel of God may peace and mercy rest.
17 Daga yanzu zuwa nan gaba kada wani ya dame ni, domin ina dauke da tabbai na Yesu a jikina.
From this time forth let no one trouble me, for I bear branded in my body the marks of Jesus, my Master.
18 Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu ya kasance da ruhun ku, 'yan'uwa. Amin.
May the grace of our Lord Jesus Christ be with your spirit, brothers. Amen.