< Galatiyawa 3 >

1 Ku Galatiyawa marasa wayo! Wanne mugun ido ya cuce ku? Ashe, ba Yesu Almasihu gicciyayye aka nuna a gaban idon ku ba?
You foolish Galatians! Whose sophistry has bewitched you--you to whom Jesus Christ has been vividly portrayed as on the Cross?
2 Ina so in gane wannan daga wurin ku ne kawai. Kun karbi Ruhun ta wurin ayyukan doka ne ko ta wurin ba da gaskiya ga abin da kuka ji?
Answer me this one question, "Is it on the ground of your obedience to the Law that you received the Spirit, or is it because, when you heard, you believed?"
3 Rashin wayonku ya yi yawa haka ne? Kun fara da Ruhu, sai kuma yanzu ku karasa a cikin jiki?
Are you so foolish? Having begun by the Spirit, are you now going to reach perfection through what is external?
4 Kun fuskanci abubuwa da yawa a banza ne - har idan a banza ne?
Have you endured such sufferings to no purpose--if indeed it has been to no purpose?
5 To, shi wanda ya ba ku Ruhun, da ayyuka masu iko a tsakanin ku, ya yi ne ta wurin ayyukan shari'a ko ta wurin ji tare da bangaskiya?
He who gives you His Spirit and works miracles among you--does He do so on the ground of your obedience to the Law, or is it the result of your having heard and believed:
6 Ibrahim ''ya ba da gaskiya ga Allah, kuma an lisafta mashi wannan a matsayin adalci.''
even as Abraham believed God, and his faith was placed to his account as righteousness?
7 Ta wannan hanya ku fahimta su wadanda suka ba da gaskiya, 'ya'yan Ibrahim ne.
Notice therefore that those who possess faith are true sons of Abraham.
8 Nassi ya riga ya hangi gaba cewa, ta wurin bangaskiya Allah zai baratar da Al'ummai. An yi wa Ibrahim shelar bishara tuntuni: ''A cikinka ne dukan al'ummai za su yi albarka.''
And the Scripture, foreseeing that in consequence of faith God would declare the nations to be free from guilt, sent beforehand the Good News to Abraham, saying, "In you all the nations shall be blessed."
9 Saboda haka, wadanda suka ba da gaskiya, masu albarka ne tare da Ibrahim wanda ke da bangaskiya.
So we see that it is those who possess faith that are blessed with believing Abraham.
10 La'ana na kan wadanda sun dangana ga ayyukan shari'a. Gama a rubuce yake, ''La'ananne ne kowanne mutum da bai tsaya ga duk abin da ke a rubuce cikin littafin shari'a ba, ya kuma aikata shi duka.”'
All who are depending upon their own obedience to the Law are under a curse, for it is written, "Cursed is every one who does not remain faithful to all the precepts of the Law, and practise them."
11 Yanzu a sarari yake, Allah ba ya baratar da kowa ta wurin shari'a, domin ''Mai adalci zai rayu ta bangaskiya.''
It is evident, too, that no one can find acceptance with God simply by obeying the Law, because "the righteous shall live by faith,"
12 Doka ba daga bangaskiya take ba, 'Amma a maimakon haka, “Shi wanda ke yin wadannan abubuwa cikin shari'a, zai yi rayuwa ta wurin shari'a.''
and the Law has nothing to do with faith. It teaches that "he who does these things shall live by doing them."
13 Almasihu ya fanshe mu daga la'anar shari'a da ya zama la'ananne saboda mu. Kamar yadda yake a rubuce, ''La'ananne ne duk wanda aka sargafe a bisa itace.''
Christ has purchased our freedom from the curse of the Law by becoming accursed for us--because "Cursed is every one who is hanged upon a tree."
14 Dalilin shine, albarkan da ke bisan Ibrahim ta zo ga al'ummai cikin Almasihu Yesu, domin mu samu karban alkawarin Ruhu ta wurin bangaskiya.
Our freedom has been thus purchased in order that in Christ Jesus the blessing belonging to Abraham may come upon the nations, so that through faith we may receive the promised Spirit.
15 'Yan'uwa, ina magana bisa ga ka'idojin mutane. Idan mutane sun yi yarjejeniya, babu mai kawar da shi ko a kara shi.
Brethren, even a covenant made by a man--to borrow an illustration from daily life--when once formally sanctioned is not liable to be set aside or added to.
16 Yanzu fa, an fada alkawaran nan ne ga Ibrahim da zuriyarsa. Bai ce, ''ga zuriya ba'' da manufar masu yawa; amma a maimakon haka ga daya kadai, ''ga zuriyar ka,'' wanda shine Almasihu.
(Now the promises were given to Abraham and to his seed. God did not say "and to seeds," as if speaking of many, but "and to your seed," since He spoke of only one--and this is Christ.)
17 Yanzu na fadi wannan. Shari'a, wadda ta zo shekaru 430 daga baya, ba ta kawar da alkawarin da Allah ya tabbatar da shi ba tun a baya.
I mean that the Covenant which God had already formally made is not abrogated by the Law which was given four hundred and thirty years later--so as to annul the promise.
18 Domin idan da gadon ya zo ta dalilin shari'a ne, da ba za ya zo kuma ta dalilin alkawari ba. Amma Allah ya ba da shi ga Ibrahim kyauta ta wurin alkawari.
For if the inheritance comes through obedience to Law, it no longer comes because of a promise. But, as a matter of fact, God has granted it to Abraham in fulfilment of a promise.
19 Me ya sa kenan aka ba da shari'a? An kara ta ne saboda laifuffuka, har sai zuriyar Ibrahim din nan ta zo ga wadanda aka yi masu alkawarinta. An kaddamar da ikon shari'ar ta wurin mala'iku, ta hannun matsakaici.
Why then was the Law given? It was imposed later on for the sake of defining sin, until the seed should come to whom God had made the promise; and its details were laid down by a mediator with the help of angels.
20 Yanzu dai matsakanci yana nufin mutum fiye da daya, duk da haka Allah daya ne.
But there cannot be a mediator where only one individual is concerned.
21 Shari'a tana tsayayya da alkawaran Allah kenan? Ko kadan! Domin idan da an ba da shari'a da ke iya bayar da rai, babu shakka da adalci ya zo ta wurin wannan shari'a.
God, however, is only one. Is the Law then opposed to the promises of God? No, indeed; for if a Law had been given which could have conferred Life, righteousness would certainly have come by the Law.
22 A maimakon haka, nassi ya kulle abubuwa duka a karkashin zunubi. Allah ya yi wannan domin alkawarin sa na ceton mu ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu ya samu a ba da shi ga wadanda suka gaskanta.
But Scripture has shown that all mankind are the prisoners of sin, in order that the promised blessing, which depends on faith in Jesus Christ, may be given to those who believe.
23 Amma kafin bangaskiya cikin Almasihu ta zo, an kulle mu kuma aka tsare mu da shari'a har zuwa ga wahayin bangaskiya.
Before this faith came, we Jews were perpetual prisoners under the Law, living under restraints and limitations in preparation for the faith which was soon to be revealed.
24 Daga nan shari'a ta zama mana jagora har sai da Almasihu ya zo, domin mu samu baratarwa ta wurin bangaskiya.
So that the Law has acted the part of a tutor-slave to lead us to Christ, in order that through faith we may be declared to be free from guilt.
25 Yanzu da bangaskiya ta zo, ba mu kuma a karkashin jagora.
But now that this faith has come, we are no longer under a tutor-slave.
26 Domin dukanku 'ya'yan Allah ne ta wurin bangaskiya cikin Almasihu Yesu.
You are all sons of God through faith in Christ Jesus;
27 Dukanku da aka yi wa baftisma cikin Almasihu, kun suturce kanku da Almasihu.
for all of you who have been baptized into Christ, have clothed yourselves with Christ.
28 Babu Bayahude ko Baheline, bawa ko 'yantacce, babu na miji ko mace, domin dukanku daya ne cikin Almasihu Yesu.
In Him the distinctions between Jew and Gentile, slave and free man, male and female, disappear; you are all one in Christ Jesus.
29 Idan ku na Almasihu ne, ku zuriyar Ibrahim ne kenan, magada bisa ga alkawarin.
And if you belong to Christ, then you are indeed true descendants of Abraham, and are heirs in fulfilment of the promise.

< Galatiyawa 3 >