< Galatiyawa 2 >
1 Daga nan, bayan shekara goma sha hudu na koma Urushalima tare da Barnaba. Na kuma dauki Titus tare da ni.
Next, after fourteen years, I went up again to Jerusalem, taking with me Barnabas and Titus.
2 Na koma ne domin Allah ya nuna mani in koma. Sai na gabatar masu shelar bisharan da nake yi a cikin al'ummai. (Amma a kebe na yi magana da wadanda aka dauka muhimman shugabanni). Na yi haka ne domin in tabbatar da cewa ba gudun banza nake yi ba, ko kuma na yi gudun banza.
And I went up according to revelation, and I debated with them about the Gospel that I am preaching among the Gentiles, but away from those who were pretending to be something, lest perhaps I might run, or have run, in vain.
3 Amma ko Titus wanda yake tare da ni, Baheline, ba wanda ya tilasta masa ya yi kaciya.
But even Titus, who was with me, though he was a Gentile, was not compelled to be circumcised,
4 Wannan maganar ta taso ne daga 'yan'uwan karya da suka zo cikinmu a boye su ga 'yancin mu a cikin Yesu Almsihu. Sun yi marmarin su maishe mu bayi ga doka.
but only because of false brothers, who were brought in unknowingly. They entered secretly to spy on our liberty, which we have in Christ Jesus, so that they might reduce us to servitude.
5 Ba mu mika kanmu biyayya gare su ba ko da na sa'a daya, domin gaskiyar bishara ta kasance babu canzawa domin ku.
We did not yield to them in subjection, even for an hour, in order that the truth of the Gospel would remain with you,
6 Amma su wadanda a ke ganin su da muhimmanci ba su taimaka mani da komai ba. Ko su wanene su bai dame ni ba. Allah ba ya karbar wanda mutane suka fi so.
and away from those who were pretending to be something. (Whatever they might have been once, it means nothing to me. God does not accept the reputation of a man.) And those who were claiming to be something had nothing to offer me.
7 Maimakon haka, suka ga an danka mani shelar bishara ga wadanda ba su da kaciya. Kamar yadda aka ba Bitrus shelar bishara ga masu kaciya.
But it was to the contrary, since they had seen that the Gospel to the uncircumcised was entrusted to me, just as the Gospel to the circumcised was entrusted to Peter.
8 Gama Allah wanda yake yin aiki a cikin Bitrus domin manzanci zuwa ga masu kaciya, haka kuma yake aiki ciki na zuwa ga al'ummai.
For he who was working the Apostleship to the circumcised in Peter, was also working in me among the Gentiles.
9 Da Yakubu, Kefas, da Yahaya, wadanda a ke gani masu gina ikilisiya, suka fahimci alherin da aka ba ni, suka bamu hannun dama na zumunci ni da Barnaba, Sun yi haka ne kawai domin mu mu tafi zuwa wurin al'ummai, su kuma su je wurin masu kaciya.
And so, when they had acknowledged the grace that was given to me, James and Cephas and John, who seemed like pillars, gave to me and to Barnabas the right hand of fellowship, so that we would go to the Gentiles, while they went to the circumcised,
10 Suna kuma so mu tuna da matalauta. Ni ma ina da aniyar yin haka.
asking only that we should be mindful of the poor, which was the very thing that I also was solicitous to do.
11 Da Kefas ya kai Antakiya, na yi tsayayya da shi a gabansa domin shine ke da kuskure.
But when Cephas had arrived at Antioch, I stood against him to his face, because he was blameworthy.
12 Da ma Kefas yana cin abinci tare da al'ummai kafin zuwan wasu mutane daga wurin Yakubu. Amma da wadannan mutane suka iso, sai ya dena kuma ya ware kansa daga al'umman. Yana jin tsoron wadannan mutanen da ke bukatar kaciya.
For before certain ones arrived from James, he ate with the Gentiles. But when they had arrived, he drew apart and separated himself, fearing those who were of the circumcision.
13 Hakannan ma sauran Yahudawa da suke tare da shi sun bi munafurcin sa. A sakamakon haka Barnaba ma ya bi munafurcin su.
And the other Jews consented to his pretense, so that even Barnabas was led by them into that falseness.
14 Da na ga basu bin gaskiyar da take cikin bisharar, na gaya wa Kefas a gaban su duka, “Idan kai Bayahude ne kana rayuwar ka ta al'ummai a maimakon rayuwar Yahudawa, to ta yaya za ka tilasta wa al'ummai su yi zaman Yahudawa? “
But when I had seen that they were not walking correctly, by the truth of the Gospel, I said to Cephas in front of everyone: “If you, while you are a Jew, are living like the Gentiles and not the Jews, how is it that you compel the Gentiles to keep the customs of the Jews?”
15 Mu da muke Yahudawa daga haihuwa, ba ''Al'ummai masu zunubi ba.''
By nature, we are Jews, and not of the Gentiles, sinners.
16 Ku sani fa, babu wanda za a baratar ta ayyukan shari'a. A maimakon haka an baratar da su ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu. Mun zo ga cikin Almasihu Yesu domin mu samu baratarwa ta bangaskiya cikin Almasihu, kuma ba ta ayyukan shari'a ba. Domin ta ayyukan shari'a babu wanda zai samu baratarwa.
And we know that man is not justified by the works of the law, but only by the faith of Jesus Christ. And so we believe in Christ Jesus, in order that we may be justified by the faith of Christ, and not by the works of the law. For no flesh will be justified by the works of the law.
17 Amma idan mun nemi Allah ya baratar da mu cikin Almasihu, mun samu kanmu masu zunubi kenan, Almasihu ya zama bawan zunubi ne? Ko kadan!
But if, while seeking to be justified in Christ, we ourselves are also found to be sinners, would then Christ be the minister of sin? Let it not be so!
18 Idan na sake gina dogara ta a kan shari'a, dogarar da na juya wa baya, na nuna kai na mai karya shari'a kenan.
For if I rebuild the things that I have destroyed, I establish myself as a prevaricator.
19 Ta wurin shari'a na mutu ga shari'a, domin in yi rayuwa irin ta Allah.
For through the law, I have become dead to the law, so that I may live for God. I have been nailed to the cross with Christ.
20 An giciye ni tare da Almasihu, ba nine ke rayuwa ba kuma, amma Almasihu ke rayuwa a cikina. Rayuwar da nake yi a yanzu a cikin jiki, ina yin ta ne, ta wurin bangaskiya ga dan Allah, wanda ya kaunace ni ya ba da kansa domina.
I live; yet now, it is not I, but truly Christ, who lives in me. And though I live now in the flesh, I live in the faith of the Son of God, who loved me and who delivered himself for me.
21 Ban yi watsi da alherin Allah ba, domin idan adalci ya wanzu ta wurin shari'a, ashe Almasihu ya mutu a banza kenan.
I do not reject the grace of God. For if justice is through the law, then Christ died in vain.