< Galatiyawa 2 >

1 Daga nan, bayan shekara goma sha hudu na koma Urushalima tare da Barnaba. Na kuma dauki Titus tare da ni.
Then, fourteen years after, I went up again to Jerusalem with Barnabas, and I took Titus also with me.
2 Na koma ne domin Allah ya nuna mani in koma. Sai na gabatar masu shelar bisharan da nake yi a cikin al'ummai. (Amma a kebe na yi magana da wadanda aka dauka muhimman shugabanni). Na yi haka ne domin in tabbatar da cewa ba gudun banza nake yi ba, ko kuma na yi gudun banza.
And I went up because of a revelation, and communicated to them the gospel that I preach among the Gentiles, but privately to those who are of reputation, lest, by any means, I should run or had run in vain.
3 Amma ko Titus wanda yake tare da ni, Baheline, ba wanda ya tilasta masa ya yi kaciya.
But not even Titus, who was with me, though he was a Greek, was compelled to be circumcised.
4 Wannan maganar ta taso ne daga 'yan'uwan karya da suka zo cikinmu a boye su ga 'yancin mu a cikin Yesu Almsihu. Sun yi marmarin su maishe mu bayi ga doka.
I acted thus indeed on account of false brethren, stealthily brought in, who stole in to spy out our freedom, which we have in Christ Jesus, that they might bring us into bondage,
5 Ba mu mika kanmu biyayya gare su ba ko da na sa'a daya, domin gaskiyar bishara ta kasance babu canzawa domin ku.
to whom we yielded in submission, not even for an hour, in order that the truth of the gospel might remain with you.
6 Amma su wadanda a ke ganin su da muhimmanci ba su taimaka mani da komai ba. Ko su wanene su bai dame ni ba. Allah ba ya karbar wanda mutane suka fi so.
But from those who were supposed to be something; (what they were is a matter of no importance to me: God does not accept the person of man; ) they, indeed, who were supposed to be something, communicated no additional truth to me;
7 Maimakon haka, suka ga an danka mani shelar bishara ga wadanda ba su da kaciya. Kamar yadda aka ba Bitrus shelar bishara ga masu kaciya.
but; on the other hand, seeing that I was intrusted with the gospel of the uncircumcision, as Peter was with that of the circumcision,
8 Gama Allah wanda yake yin aiki a cikin Bitrus domin manzanci zuwa ga masu kaciya, haka kuma yake aiki ciki na zuwa ga al'ummai.
(for he who gave efficiency to Peter, for the apostleship of the circumcision, gave efficiency to me also, as an apostle for the Gentiles, )
9 Da Yakubu, Kefas, da Yahaya, wadanda a ke gani masu gina ikilisiya, suka fahimci alherin da aka ba ni, suka bamu hannun dama na zumunci ni da Barnaba, Sun yi haka ne kawai domin mu mu tafi zuwa wurin al'ummai, su kuma su je wurin masu kaciya.
and knowing the grace that was given to me, James and Cephas and John, who seemed to be pillars, gave to me and Barnabas the right hand of fellowship, that we should go to the Gentiles, but they to the circumcision,
10 Suna kuma so mu tuna da matalauta. Ni ma ina da aniyar yin haka.
requesting only that we would remember the poor, which same thing I have been diligent in doing.
11 Da Kefas ya kai Antakiya, na yi tsayayya da shi a gabansa domin shine ke da kuskure.
But when Peter came to Antioch, I openly opposed him, because he had incurred blame.
12 Da ma Kefas yana cin abinci tare da al'ummai kafin zuwan wasu mutane daga wurin Yakubu. Amma da wadannan mutane suka iso, sai ya dena kuma ya ware kansa daga al'umman. Yana jin tsoron wadannan mutanen da ke bukatar kaciya.
For, before certain persons came from James, he ate with the Gentiles: but, when they had come, he withdrew, and separated himself, because he feared those who were of the circumcision.
13 Hakannan ma sauran Yahudawa da suke tare da shi sun bi munafurcin sa. A sakamakon haka Barnaba ma ya bi munafurcin su.
And the other Jews, also, acted hypocritically with him, so that even Barnabas was led away by their hypocrisy.
14 Da na ga basu bin gaskiyar da take cikin bisharar, na gaya wa Kefas a gaban su duka, “Idan kai Bayahude ne kana rayuwar ka ta al'ummai a maimakon rayuwar Yahudawa, to ta yaya za ka tilasta wa al'ummai su yi zaman Yahudawa? “
But when I saw that they did not walk uprightly according to the truth of the gospel, I said to Peter, before them all: If you, being a Jew, live after the manner of the Gentiles, and not after the manner of the Jews, why do you compel the Gen tiles to observe Jewish customs?
15 Mu da muke Yahudawa daga haihuwa, ba ''Al'ummai masu zunubi ba.''
We, who are Jews by birth, and not Gentile sinners,
16 Ku sani fa, babu wanda za a baratar ta ayyukan shari'a. A maimakon haka an baratar da su ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu. Mun zo ga cikin Almasihu Yesu domin mu samu baratarwa ta bangaskiya cikin Almasihu, kuma ba ta ayyukan shari'a ba. Domin ta ayyukan shari'a babu wanda zai samu baratarwa.
knowing that a man is not justified by works of law, but by faith in Jesus Christ, even we have believed on Christ Jesus, that we may be justified by faith in Christ, and not by works of law: because, by works of law no flesh shall be justified.
17 Amma idan mun nemi Allah ya baratar da mu cikin Almasihu, mun samu kanmu masu zunubi kenan, Almasihu ya zama bawan zunubi ne? Ko kadan!
But if, while we seek to be justified in Christ, we ourselves are also found sinners, is Christ, therefore, the minister of sin? It can not be.
18 Idan na sake gina dogara ta a kan shari'a, dogarar da na juya wa baya, na nuna kai na mai karya shari'a kenan.
For if I build again those things which I have destroyed, I make myself a transgressor.
19 Ta wurin shari'a na mutu ga shari'a, domin in yi rayuwa irin ta Allah.
For, through law, I have died to law, that I might live to God.
20 An giciye ni tare da Almasihu, ba nine ke rayuwa ba kuma, amma Almasihu ke rayuwa a cikina. Rayuwar da nake yi a yanzu a cikin jiki, ina yin ta ne, ta wurin bangaskiya ga dan Allah, wanda ya kaunace ni ya ba da kansa domina.
I have been crucified with Christ, yet I live; no longer I, but Christ lives in me. And the life which I now live in the flesh, I live by the faith of the Son of God, who loved me, and gave himself for me.
21 Ban yi watsi da alherin Allah ba, domin idan adalci ya wanzu ta wurin shari'a, ashe Almasihu ya mutu a banza kenan.
I do not set aside the grace of God: for if righteousness be through law, then Christ has died in vain.

< Galatiyawa 2 >