< Galatiyawa 2 >
1 Daga nan, bayan shekara goma sha hudu na koma Urushalima tare da Barnaba. Na kuma dauki Titus tare da ni.
Senere, efter fjorten Aars Forløb, drog jeg atter op til Jerusalem med Barnabas og tog ogsaa Titus med.
2 Na koma ne domin Allah ya nuna mani in koma. Sai na gabatar masu shelar bisharan da nake yi a cikin al'ummai. (Amma a kebe na yi magana da wadanda aka dauka muhimman shugabanni). Na yi haka ne domin in tabbatar da cewa ba gudun banza nake yi ba, ko kuma na yi gudun banza.
Men jeg drog op ifølge en Aabenbaring og forelagde dem, men særskilt de ansete, det Evangelium, som jeg prædiker iblandt Hedningerne, — om jeg vel løber eller har løbet forgæves.
3 Amma ko Titus wanda yake tare da ni, Baheline, ba wanda ya tilasta masa ya yi kaciya.
Men end ikke min Ledsager, Titus, som var en Græker, blev tvungen til at omskæres,
4 Wannan maganar ta taso ne daga 'yan'uwan karya da suka zo cikinmu a boye su ga 'yancin mu a cikin Yesu Almsihu. Sun yi marmarin su maishe mu bayi ga doka.
nemlig for de indsnegne falske Brødres Skyld, som jo havde listet sig ind for at lure paa vor Frihed, som vi have i Kristus Jesus, for at de kunde gøre os til Trælle.
5 Ba mu mika kanmu biyayya gare su ba ko da na sa'a daya, domin gaskiyar bishara ta kasance babu canzawa domin ku.
For dem vege vi end ikke et Øjeblik i Eftergivenhed, for at Evangeliets Sandhed maatte blive varig hos eder.
6 Amma su wadanda a ke ganin su da muhimmanci ba su taimaka mani da komai ba. Ko su wanene su bai dame ni ba. Allah ba ya karbar wanda mutane suka fi so.
Men fra deres Side, som ansaas for at være noget, (hvordanne de fordum vare, er mig uden Forskel; Gud ser ikke paa et Menneskes Person; ) — over for mig nemlig havde de ansete intet at tilføje.
7 Maimakon haka, suka ga an danka mani shelar bishara ga wadanda ba su da kaciya. Kamar yadda aka ba Bitrus shelar bishara ga masu kaciya.
Men tværtimod, da de saa, at jeg har faaet Evangeliet til de uomskaarne betroet, ligesom Peter til de omskaarne,
8 Gama Allah wanda yake yin aiki a cikin Bitrus domin manzanci zuwa ga masu kaciya, haka kuma yake aiki ciki na zuwa ga al'ummai.
(thi han, som gav Peter Kraft til Apostelgerning for de omskaarne, gav ogsaa mig Kraft dertil for Hedningerne; )
9 Da Yakubu, Kefas, da Yahaya, wadanda a ke gani masu gina ikilisiya, suka fahimci alherin da aka ba ni, suka bamu hannun dama na zumunci ni da Barnaba, Sun yi haka ne kawai domin mu mu tafi zuwa wurin al'ummai, su kuma su je wurin masu kaciya.
og da de lærte den mig givne Naade at kende, gave Jakob og Kefas og Johannes, som ansaas for at være Søjler, mig og Barnabas Samfundshaand for at vi skulde gaa til Hedningerne og de til de omskaarne;
10 Suna kuma so mu tuna da matalauta. Ni ma ina da aniyar yin haka.
kun at vi skulde komme de fattige i Hu, hvad jeg ogsaa just har bestræbt mig for at gøre.
11 Da Kefas ya kai Antakiya, na yi tsayayya da shi a gabansa domin shine ke da kuskure.
Men da Kefas kom til Antiokia, traadte jeg op imod ham for hans aabne Øjne, thi domfældt var han.
12 Da ma Kefas yana cin abinci tare da al'ummai kafin zuwan wasu mutane daga wurin Yakubu. Amma da wadannan mutane suka iso, sai ya dena kuma ya ware kansa daga al'umman. Yana jin tsoron wadannan mutanen da ke bukatar kaciya.
Thi førend der kom nogle fra Jakob, spiste han sammen med Hedningerne; men da de kom, trak han sig tilbage og skilte sig fra dem af Frygt for dem af Omskærelsen.
13 Hakannan ma sauran Yahudawa da suke tare da shi sun bi munafurcin sa. A sakamakon haka Barnaba ma ya bi munafurcin su.
Og med ham hyklede ogsaa de øvrige Jøder, saa at endog Barnabas blev dragen med af deres Hykleri.
14 Da na ga basu bin gaskiyar da take cikin bisharar, na gaya wa Kefas a gaban su duka, “Idan kai Bayahude ne kana rayuwar ka ta al'ummai a maimakon rayuwar Yahudawa, to ta yaya za ka tilasta wa al'ummai su yi zaman Yahudawa? “
Men da jeg saa, at de ikke vandrede rettelig efter Evangeliets Sandhed, sagde jeg til Kefas i alles Paahør: Naar du, som er en Jøde, lever paa hedensk og ikke paa jødisk Vis, hvor kan du da tvinge Hedningerne til at opføre sig som Jøder?
15 Mu da muke Yahudawa daga haihuwa, ba ''Al'ummai masu zunubi ba.''
Vi ere af Natur Jøder og ikke Syndere af hedensk Byrd;
16 Ku sani fa, babu wanda za a baratar ta ayyukan shari'a. A maimakon haka an baratar da su ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu. Mun zo ga cikin Almasihu Yesu domin mu samu baratarwa ta bangaskiya cikin Almasihu, kuma ba ta ayyukan shari'a ba. Domin ta ayyukan shari'a babu wanda zai samu baratarwa.
men da vi vide, at et Menneske ikke bliver retfærdiggjort af Lovens Gerninger, men kun ved Tro paa Jesus Kristus, saa have ogsaa vi troet paa Kristus Jesus, for at vi maatte blive retfærdiggjorte af Tro paa Kristus og ikke af Lovens Gerninger; thi af Lovens Gerninger skal intet Kød blive retfærdiggjort.
17 Amma idan mun nemi Allah ya baratar da mu cikin Almasihu, mun samu kanmu masu zunubi kenan, Almasihu ya zama bawan zunubi ne? Ko kadan!
Men naar vi, idet vi søgte at blive retfærdiggjorte i Kristus, ogsaa selv fandtes at være Syndere, saa er jo Kristus en Tjener for Synd? Det være langtfra!
18 Idan na sake gina dogara ta a kan shari'a, dogarar da na juya wa baya, na nuna kai na mai karya shari'a kenan.
naar jeg nemlig igen bygger det op, som jeg nedbrød, da viser jeg mig selv som Overtræder.
19 Ta wurin shari'a na mutu ga shari'a, domin in yi rayuwa irin ta Allah.
Thi jeg er ved Loven død fra Loven, for at jeg skal leve for Gud.
20 An giciye ni tare da Almasihu, ba nine ke rayuwa ba kuma, amma Almasihu ke rayuwa a cikina. Rayuwar da nake yi a yanzu a cikin jiki, ina yin ta ne, ta wurin bangaskiya ga dan Allah, wanda ya kaunace ni ya ba da kansa domina.
Med Kristus er jeg korsfæstet, og det er ikke mere mig, der lever, men Kristus lever i mig; men hvad jeg nu lever i Kødet, det lever jeg i Troen paa Guds Søn, som elskede mig og gav sig selv hen for mig.
21 Ban yi watsi da alherin Allah ba, domin idan adalci ya wanzu ta wurin shari'a, ashe Almasihu ya mutu a banza kenan.
Jeg ophæver ikke Guds Naade; thi er der Retfærdighed ved Loven, da er jo Kristus død forgæves.