< Afisawa 1 >
1 Bulus, manzon Yesu Almasihu ta wurin nufin Allah, zuwa ga kebabbu na Allah da ke a Afisa wanda suke aminci cikin Yesu.
Me bulus udura u vana Asere a hira katuma ka Asere, uhana ahira anu uzatu madinisa wa ra u Afisus, nan an de sa wa hem in vana Asere.
2 Bari alheri ya kasance da ku, da salama daga wurin Allah Ubanmu da Ubangijinmu Yesu Almasihu.
Imum iriri a hira a shi me, nan kadura ka riri u suru ahira Asere aco aru nan vana Asere.
3 Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Shine ya albarkace mu da kowanne albarku na ruhaniya da ke cikin sammai cikin Almasihu.
Nan imum iriri ya Asere nan aco nan vana Asere, de sa ma nya duru imum iriri na ko de ya imum iriri a nymo a vana Asere.
4 Kafin halitar duniya, Allah ya zabe mu da muka ba da gaskiya cikin Yesu. Ya zabe mu domin mu yi zaman tsarki da rayuwar da babu aibu a gabansa.
Kasi sa ma zaukan be duru a nyimo ameme, uganiya sa da ma mu tuba unee ba, barki ti cukuno anu a lau, anu zatu madini a nyimo a meme nan a nyio u su.
5 Cikin kauna Allah ya kaddara ya dauke mu mu zama yayansa ta wurin Yesu almasihu. Ya yi wannan domin ya gamshe shi ya yi abin da ya ke so.
Uganiya sa mamu, kurzon duru ti cukuno ahana a meme, usuru u Yesu vana Asere, kasi u ira u meme.
6 Sakamakon shine Allah ya karbi yabo domin daukakan alherinsa. Wannan shine abinda ya ba mu hannu sake ta wurin kaunataccensa.
A wuzi imumu i geme vat, barki a norziko niza na Asere, ige sa a nyanki duru, barki u hem u vana uru.
7 Gama cikin kaunataccensa aka fanshe mu ta wurin jininsa, da gafarar zunubai ta wurin wadataccen alherinsa.
A hira ame ani ta kem ubura a hira a maye ma me, u ceki u ti mum ti zenzen turu, ahira u kem ti mumu ti riri ta Asere.
8 Ya ba da wannan alherin a yalwace cikin dukan hikima da fahimta.
ge sa ma nya duru, unu rusa u meme.
9 Allah ya bayyana mana gaskiyar al'amarin da aka boye na shirinsa, ta wurin abin da yake so ya nuna cikin Almasihu.
Ma bezin duru imum be sa ya ra iriba imeme, ti mumu ti riri tu meme sa ma nya ma nyinca ahira a vana umeme.
10 Idan lokaci ya yi na kammala shirinsa, Allah zai kawo dukan abubuwan da ke sama da kasa cikin Yesu.
Vat imum ige me ubarka, uni barki u myinca uganiya sa mu sa ti mum ahira a vana umemu ti mum a hira be a vana Asere.
11 An zabe mu cikin Almasihu mu zama abin gado na Allah. Ya yi mana wannan shirin tun da cikin shirin sa, shi mai yin dukan abu ta dalilin nufinsa.
A hira a me ani a kurzo duru a hana a kura Asere, a kurzon duru ani me barki de sa ma boo ti mumu tige sa ma nyari uwuza me.
12 Allah ya yi haka saboda mu rayu domin yabon daukakarsa. Mune na farko da muka sami bege cikin Almasihu.
Barki haru sa ta tubi nya iriba ahira a meme ti wuzi ti cukun ti ni nonzo nu meme.
13 A cikin Almasihu ne kuma kuka samu jin maganar gaskiya, bisharan cetonku ta wurin Yesu. A cikinsa ne kuka bada gaskiya aka hatimce ku da Ruhu Mai Tsarki wanda aka alkawarta.
A yimo ame ani ta kuri ti kunna tize ti huma, tize tu kaba uru, anyimo a meme sa ta nya mu riba muru.
14 Ruhun shine tabbacin gadonmu kafin mu kai ga samunsa. Wannan don yabon daukakarsa ne.
Me mani unu bezizi, uru ti mumu u hana uganiya sa ta kem me, barki ani me, ni nonzo nu me nini.
15 Sabo da haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kaunar ku zuwa dukan wadanda aka kebe dominsa.
Barki ani me ma kunna tize ti huma ti shi me ahira Yesu vana Asere, nan uhem uru me, ahana alau.
16 Ban fasa tunawa da ku ba ina addu'a saboda ku cikin addu'o'ina.
Daki ma diri unonzo Asere barki shi ba, vat uganiya sain zin nu wuza u shi biringara.
17 Ina addu'a da cewa Allah Ubangijinmu Yesu Almasihu, Uban daraja, ya ba ku ruhun basira da wahayin saninsa.
Unu guna Asere avana u Yesu, aco unu dang, ma nya shi bibe bu gamara nan bi boo urusa Asere.
18 Ina addu'a idanun zuciyarku su bude domin ku san tabacin kiranku. Ina addu'a dominku san arzikin mulkin gadonsa cikin wadanda aka kebe dominsa.
In kuru in wu shi irusi eje iriba, barki irusi nyanini tize ti gino me ta titan duru ni, nan nyanini gwardan sa i eze barki ana lau.
19 Ina addu'a ku san ikon nan nasa mai girma mara iyaka da ke cikin mu da muka ba da gaskiya. Wannan girman yana ta wurin aikin karfin ikonsa ne.
Nan ko di nyanini imumu i dandang i rusa anu zatu bata sa ma zinu boo me, ahira aru aru, haru anu nya iriba, i boo a nyimo ani kara nu meme.
20 Wannan shine ikon da ya yi aiki cikin Almasihu lokacin da Allah ya tashe shi daga matattu ya sa shi a hannun damansa cikin sammai.
De sa ma boo ahira Asere uganiya sa ma wu ahirza me a nya me a hira ucukuno a tari tina reh tu meme a. yimo Asesere.
21 Ya sanya shi bisa birbishin dukan sarauta, iko, mulki, karfi, da kowanne irin suna. Ya sanya Almasihu ba a wannan zamanin kadai ba, amma da zamani mai zuwa. (aiōn )
A nyimo a ni za ni ti Gomo nanu bari wan ni kara, vat tiza tu neh, a zo tiza sa adi nya nueh cas, uhana i wono. (aiōn )
22 Allah ya saka dukan abubuwa a karkashin kafafun Almasihu. Ya sa shi shugaban dukan abubuwa a cikin ikilisiya.
Aseri a nya ti mumu a tari tu bari uvana Asere, ma kuri ma nya a nyimo udenge Asere i cukuno unu inta u ti mumu vat.
23 Ikilisiya jikinsa ne, cikarsa wanda ya cika dukan abubuwa cikin kowacce hanya.
Udenge Asere une uni ni pum ni vana Asere, u nyinca unu nyinca u ti mumu.