< Afisawa 5 >
1 Saboda haka ku zama masu koyi da Allah, kamar kaunatattun 'ya'yansa.
Therefore, be imitators of God, as beloved children,
2 Ku yi zama cikin kauna kamar yadda Almasihu ya kaunace mu, ya kuma mika kansa sadaka da hadaya ga Allah dominmu, hadaya mai kanshi abin karba ga Allah.
and walk in love, just as Christ loved us and gave himself up for us as a fragrant offering and sacrifice to God.
3 Fasikanci ko kowacce irin kazamta, ko kazamar lalata kada a ambace su a tsakaninku, don haka ya dace ga masu bi.
But fornication, impurity of any kind, and covetousness must not even be mentioned among you, because such things are improper for saints.
4 Kada a ambaci batsa, maganar wauta ko alfasha wadanda ba su dace ba. Maimakon haka, mu zama masu godiya.
Nor should there be any obscenity, foolish talk, or coarse joking, which are not fitting, but there should be thanksgiving instead.
5 Domin wannan kun sani cewa ba fasiki, ko mara tsarki, ko mai hadama wato mai bautar gumaka zai sami gado cikin mulkin Almasihu da Allah.
For you know that no one who is a fornicator, impure, or covetous (that is, an idolater) has any inheritance in the kingdom of Christ and of God.
6 Kada kowa ya rude ku da maganganun wofi. Saboda wadannan abubuwa ne fushin Allah ke zuwa kan kangararrun 'ya'ya.
Let no one deceive you with empty words, for because of these things the wrath of God is coming upon the sons of disobedience.
7 Kada ku yi tarayya tare da su.
Therefore do not be partners with them.
8 Domin da ku duhu ne, amma yanzu ku haske ne cikin Ubangiji. Sai ku yi tafiya kamar 'ya'yan haske.
For you were once darkness, but now you are light in the Lord. Walk as children of light
9 Saboda amfanin haske shine dukan alheri, adalci da gaskiya.
(for the fruit of the Spirit is found in all goodness, righteousness, and truth).
10 Kuna bidar abin da Ubangiji ke murna da shi.
Carefully determine what is pleasing to the Lord.
11 Kada ku sa hannu ga ayyuka marasa amfani da ayyukan duhu amma gara a tone su.
Do not participate in the unfruitful works of darkness, but expose them instead.
12 Don abubuwan da suke yi a boye abin kunya ne a bayyana su.
For it is shameful even to mention what such people do in secret.
13 Dukan abu, idan haske ya bayyana su, za a gan su.
But everything exposed by the light becomes illuminated, and everything that is illuminated becomes a light.
14 Domin duk abin da aka bayyana ya zama haske. Saboda haka aka ce, “Ka farka, kai mai barci, ka tashi daga cikin matattu; Almasihu kuwa zai haskaka bisanka”.
Therefore it says, “Awake, O sleeper, and arise from the dead, and Christ will shine upon yoʋ.”
15 Saboda haka, ku maida hankali yadda kuke rayuwar ku, ba kamar mutane marasa hikima ba amma kamar masu hikima.
See then that you walk carefully, not as unwise people but as wise,
16 Ku yi lura yadda kuke amfani da lokaci don kwanakin miyagu ne.
making the best use of the time, because the days are evil.
17 Kada ku zama wawaye. Maimakon haka, ku fahimci ko menene nufin Ubangiji.
Therefore do not be foolish, but understand what the will of the Lord is.
18 Kuma Kada ku bugu da ruwan inabi, don yana iya lalata rayuwa. Maimakon haka, ku cika da Ruhu Mai Tsarki.
Do not be drunk with wine, which leads to debauchery, but be filled with the Spirit,
19 Kuna magana da junanku cikin zabura da wakoki da wakokin ruhaniya, kuna rairawa da yabo da zuciyarku ga Ubangiji.
speaking to one another in psalms, hymns, and spiritual songs, singing and making melody with your hearts to the Lord,
20 Kullum kuna ba da gaskiya domin dukan abubuwa cikin sunan Ubangiji Yesu ga Allah Uba.
always giving thanks for everything to our God and Father in the name of our Lord Jesus Christ,
21 Kuna sarayadda kanku ga juna cikin girmama Almasihu.
and submitting to one another in the fear of Christ.
22 Mata, ku yi biyayya ga mazan ku kamar ga Ubangiji.
Wives, submit to your husbands, as to the Lord.
23 Domin miji shine shugaban matarsa kamar yadda Almasihu yake shugaban ikilisiya. Shine kuma mai ceton jiki.
For the husband is the head of the wife, just as Christ is the head and Savior of the church, which is his body.
24 Amma kamar yadda ikilisiya take biyayya ga Almasihu, haka kuma dole mata suyi ga mazajen su cikin kowanne abu.
Just as the church submits to Christ, so wives should submit to their husbands in everything.
25 Mazaje, ku kaunaci matanku kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya har ya ba da kansa dominta,
Husbands, love your wives, just as Christ loved the church and gave himself up for her
26 Ya yi wannan domin ya tsarkake ta. Ya wanke mu da ruwan wanki ta wurin kalma.
to sanctify her by cleansing her with the washing of water by the word,
27 Ya yi wannan domin ya mika ma kansa ikilisiya mai daraja, ba tare da tabo ko cikas ko wani abu kamar wadannan, amma ta zama da tsarki da kuma mara aibi.
so that he might present her to himself as a glorious church, without spot or wrinkle or any such thing, but holy and unblemished.
28 Hakannan kuma, mazaje su kaunaci matansu kamar jikunnansu. Wanda yake kaunar matarsa yana kaunar kansa.
In the same way husbands ought to love their wives as their own bodies. He who loves his wife loves himself.
29 Ba wanda ya taba kin jikinsa. Amma, yakan ciyadda shi yana kaunarsa, kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya.
For no one has ever hated his own flesh, but he nourishes and cares for it, just as the Lord does for the church,
30 Domin mu gabobin jikinsa ne.
because we are members of his body, of his flesh and of his bones.
31 “Domin wannan mutum zai rabu da ubansa da uwarsa ya manne wa matarsa, su biyu su zama nama daya”.
“For this reason a man will leave his father and mother and be joined to his wife, and the two will become one flesh.”
32 Wannan asirin gaskiyar, da girma yake, amma ina magana ne game da Almasihu da ikilisiyarsa.
This is a profound mystery, but I am talking about Christ and the church.
33 Duk da haka, kowannenku dole ya kaunaci matarsa kamar kansa, matar kuma dole ta girmama mijinta.
Nevertheless, each man among you must love his own wife as he loves himself, and the wife must respect her husband.