< Afisawa 5 >

1 Saboda haka ku zama masu koyi da Allah, kamar kaunatattun 'ya'yansa.
Vorder derfor Guds Efterlignere som elskede Børn,
2 Ku yi zama cikin kauna kamar yadda Almasihu ya kaunace mu, ya kuma mika kansa sadaka da hadaya ga Allah dominmu, hadaya mai kanshi abin karba ga Allah.
og vandrer i Kærlighed, ligesom også Kristus elskede os og gav sig selv hen for os som en Gave og et Slagtoffer, Gud til en velbehagelig Lugt.
3 Fasikanci ko kowacce irin kazamta, ko kazamar lalata kada a ambace su a tsakaninku, don haka ya dace ga masu bi.
Men Utugt og al Urenhed eller Havesyge bør end ikke nævnes iblandt eder, som det sømmer sig for hellige,
4 Kada a ambaci batsa, maganar wauta ko alfasha wadanda ba su dace ba. Maimakon haka, mu zama masu godiya.
ej heller ublu Væsen eller dårlig Snak eller letfærdig Skæmt, hvilket er utilbørligt, men hellere Taksigelse.
5 Domin wannan kun sani cewa ba fasiki, ko mara tsarki, ko mai hadama wato mai bautar gumaka zai sami gado cikin mulkin Almasihu da Allah.
Thi dette vide og erkende I, at ingen utugtig eller uren eller havesyg, hvilket er en Afgudsdyrker, har Arv i Kristi og Guds Rige.
6 Kada kowa ya rude ku da maganganun wofi. Saboda wadannan abubuwa ne fushin Allah ke zuwa kan kangararrun 'ya'ya.
Ingen bedrage eder med tomme Ord; thi for disse Ting kommer Guds Vrede over Genstridighedens Børn.
7 Kada ku yi tarayya tare da su.
Derfor, bliver ikke meddelagtige med dem!
8 Domin da ku duhu ne, amma yanzu ku haske ne cikin Ubangiji. Sai ku yi tafiya kamar 'ya'yan haske.
Thi I vare forhen Mørke, men nu ere I Lys i Herren; vandrer som Lysets Børn;
9 Saboda amfanin haske shine dukan alheri, adalci da gaskiya.
(Lysets Frugt viser sig jo i al Godhed og Retfærdighed og Sandhed, )
10 Kuna bidar abin da Ubangiji ke murna da shi.
så I prøve, hvad der er velbehageligt for Herren.
11 Kada ku sa hannu ga ayyuka marasa amfani da ayyukan duhu amma gara a tone su.
Og haver ikke Samfund med Mørkets ufrugtbare Gerninger. Men revser dem hellere;
12 Don abubuwan da suke yi a boye abin kunya ne a bayyana su.
thi hvad der lønligt bedrives af dem, er skammeligt endog at sige;
13 Dukan abu, idan haske ya bayyana su, za a gan su.
men alt dette bliver åbenbaret, når det revses af Lyset. Thi alt det, som bliver åbenbaret, er Lys.
14 Domin duk abin da aka bayyana ya zama haske. Saboda haka aka ce, “Ka farka, kai mai barci, ka tashi daga cikin matattu; Almasihu kuwa zai haskaka bisanka”.
Derfor hedder det: "Vågn op, du, som sover, og stå op fra de døde, og Kristus skal lyse for dig!"
15 Saboda haka, ku maida hankali yadda kuke rayuwar ku, ba kamar mutane marasa hikima ba amma kamar masu hikima.
Ser derfor nøje til, hvorledes I vandre, ikke som uvise, men som vise,
16 Ku yi lura yadda kuke amfani da lokaci don kwanakin miyagu ne.
så I købe den belejlige Tid, efterdi Dagene ere onde.
17 Kada ku zama wawaye. Maimakon haka, ku fahimci ko menene nufin Ubangiji.
Derfor bliver ikke uforstandige, men skønner, hvad Herrens Villie er.
18 Kuma Kada ku bugu da ruwan inabi, don yana iya lalata rayuwa. Maimakon haka, ku cika da Ruhu Mai Tsarki.
Og drikker eder ikke drukne i Vin, i hvilket der er Ryggesløshed, men lader eder fylde med Ånden,
19 Kuna magana da junanku cikin zabura da wakoki da wakokin ruhaniya, kuna rairawa da yabo da zuciyarku ga Ubangiji.
så I tale hverandre til med Salmer og Lovsange og åndelige Viser og synge og spille i eders Hjerte for Herren
20 Kullum kuna ba da gaskiya domin dukan abubuwa cikin sunan Ubangiji Yesu ga Allah Uba.
og altid sige Gud og Faderen Tak for alle Ting i vor Herres Jesu Kristi Navn
21 Kuna sarayadda kanku ga juna cikin girmama Almasihu.
og underordne eder under hverandre i Kristi Frygt;
22 Mata, ku yi biyayya ga mazan ku kamar ga Ubangiji.
Hustruerne skulle underordne sig under deres egne Mænd, som under Herren;
23 Domin miji shine shugaban matarsa kamar yadda Almasihu yake shugaban ikilisiya. Shine kuma mai ceton jiki.
thi en Mand er sin Hustrus Hoved, ligesom også Kristus er Menighedens Hoved. Han er sit Legemes Frelser.
24 Amma kamar yadda ikilisiya take biyayya ga Almasihu, haka kuma dole mata suyi ga mazajen su cikin kowanne abu.
Dog, ligesom Menigheden underordner sig under Kristus, således skulle også Hustruerne underordne sig under deres Mænd i alle Ting.
25 Mazaje, ku kaunaci matanku kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya har ya ba da kansa dominta,
I Mænd! elsker eders Hustruer, ligesom også Kristus elskede Menigheden og hengav sig selv for den,
26 Ya yi wannan domin ya tsarkake ta. Ya wanke mu da ruwan wanki ta wurin kalma.
for at han kunde hellige den, idet han rensede den ved Vandbadet med et Ord,
27 Ya yi wannan domin ya mika ma kansa ikilisiya mai daraja, ba tare da tabo ko cikas ko wani abu kamar wadannan, amma ta zama da tsarki da kuma mara aibi.
for at han selv kunde fremstille Menigheden for sig som herlig, uden Plet eller Rynke eller noget deslige, men for at den måtte være hellig og ulastelig.
28 Hakannan kuma, mazaje su kaunaci matansu kamar jikunnansu. Wanda yake kaunar matarsa yana kaunar kansa.
Således ere Mændene skyldige at elske deres egne Hustruer som deres egne Legemer; den, som elsker sin egen Hustru, elsker sig selv.
29 Ba wanda ya taba kin jikinsa. Amma, yakan ciyadda shi yana kaunarsa, kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya.
Ingen har jo nogen Sinde hadet sit eget Kød, men han nærer og plejer det, ligesom også Kristus Menigheden.
30 Domin mu gabobin jikinsa ne.
Thi vi ere Lemmer på hans Legeme.
31 “Domin wannan mutum zai rabu da ubansa da uwarsa ya manne wa matarsa, su biyu su zama nama daya”.
Derfor skal et Menneske forlade sin Fader og Moder og holde fast ved sin Hustru, og de to skulle være eet Kød.
32 Wannan asirin gaskiyar, da girma yake, amma ina magana ne game da Almasihu da ikilisiyarsa.
Denne Hemmelighed er stor - jeg sigter nemlig til Kristus og til Menigheden.
33 Duk da haka, kowannenku dole ya kaunaci matarsa kamar kansa, matar kuma dole ta girmama mijinta.
Dog, også I skulle elske hver især sin egen Hustru som sig selv; men Hustruen have Ærefrygt for Manden!

< Afisawa 5 >