< Kolossiyawa 3 >

1 Idan dai Allah ya tashe ku tare da Almasihu, ku nemi abubuwan da ke sama, inda Almasihu ke zaune a hannun dama na Allah.
Når I altså, ere blevne oprejste med Kristus, da søger det, som er oventil, hvor Kristus sidder ved Guds højre Hånd.
2 Yi tunanin a kan abubuwan da ke sama, ba a kan abubuwan da ke kasa ba.
Tragter efter det, som er oventil, ikke efter det, som er på Jorden.
3 Gama ku kun mutu, ranku kuma yana boye tare da Almasihu cikin Allah.
Thi I ere døde, og eders Liv er skjult med Kristus i Gud.
4 Sa'anda Almasihu ya bayyana, wanda shine ranku, sa'anan ku kuma zaku bayyana tare da shi cikin daukakarsa.
Når Kristus, vort Liv, åbenbares, da skulle også I åbenbares med ham i Herlighed.
5 Ku kashe sha'awacce-sha'awaccen da suke a duniya - zina da fasikanci, rashin tsarki, muguwar sha'awa, mummunar buri, da kuma kwadayi, wadda shine bautar gumaka.
Så døder da de jordiske Lemmer, Utugt Urenhed, Brynde, ondt Begær og Havesygen, som jo er Afgudsdyrkelse;
6 Saboda wandannan abubuwa ne fushin Allah ke zuwa a kan marasa biyayya.
for disse Tings Skyld kommer Guds Vrede.
7 A cikin wadannan abubuwa ne kuka yi rayuwa a da da kuke zauna a cikinsu.
I dem vandrede også I fordum, da I levede deri.
8 Amma yanzu dole ku kawar da wadannan - zafin rai, fushi, mugayen manufofi, zage-zage, da kazamar magana daga bakinku.
Men nu skulle også I aflægge det alt sammen, Vrede, Hidsighed, Ondskab, Forhånelse, slem Snak af eders Mund.
9 Kada ku yi wa juna karya, domin kun tube tsohon mutumin da ayyukansa,
Lyver ikke for hverandre, da I have afført eder det gamle Menneske med dets Gerninger
10 kun kuma yafa sabon mutum, wanda ake sabontawa cikin sani bisa ga surar wannan da ya hallice shi.
og iført eder det nye, som fornyes til Erkendelse efter hans Billede, der skabte det;
11 A nan ne inda babu Baheline da Bayahude, mai kaciya da marar kaciya, bare, baubawa, ko Basikitiye, bawa ko yantacce, amma Almasihu shine duka, yana kuma cikin duka.
hvor der ikke er Græker og Jøde, Omskærelse og Forhud, Barbar, Skyther, Træl, fri, men Kristus er alt og i alle.
12 A matsayin ku na zababbun Allah, masu tsarki da kaunatattu sai ku yafa jinkai, ayyukan kirki, saukin kai, kamewa da hakuri.
Så ifører eder da som Guds udvalgte, hellige og elskede inderlig Barmhjertighed, Godhed, Ydmyghed, Sagtmodighed, Langmodighed,
13 Yi hakuri da juna. Ku yi wa juna alheri. Idan wani na da damuwa da wani, ku gafarta kamar yadda Ubangiji ya gafarta maku.
så I bære over med hverandre og tilgive hverandre, dersom nogen har Klagemål imod nogen; ligesom Kristus tilgav eder, således også I!
14 Fiye da wadanan abubuwa duka, ku kasance da kauna, wanda itace cikakkiyar kammalla.
Men over alt dette skulle I iføre eder Kærligheden, hvilket er Fuldkommenhedens Bånd.
15 Bari salamar Almasihu ta mallaki zukatanku. Sabili da wannan salama ce aka kiraye ku cikin jiki daya. Ku yi godiya.
Og Kristi Fred råde i eders Hjerter, til hvilken I også bleve kaldede i eet Legeme; og vorder taknemmelige!
16 Ku bar maganar Almasihu ta zauna a cikinku a yalwace. Da dukan hikima, ku koyar, ku kuma gargadi juna da zabura, wakoki, da wakokin yabo na ruhaniya. Kuna rairawa tare da godiya cikin zukatanku ga Allah.
Lad Kristi Ord bo rigeligt iblandt eder, så I med al Visdom lære og påminde hverandre med Salmer, Lovsange og åndelige Viser, idet I synge med Ynde i eders Hjerter for Gud.
17 Kuma duk abin da zaku yi cikin magana ko aiki ku yi duka cikin sunan Ubangiji Yesu. Kuna yin godiya ga Allah Uba ta wurinsa.
Og alt, hvad I gøre i Ord eller i Handling, det gører alt i den Herres Jesu Navn, takkende Gud Fader ved ham.
18 Mata, ku yi biyayya ga mazajenku, yadda yakamata a cikin Ubangiji.
I Hustruer! underordner eder under eders Mænd, som det sømmer sig i Herren.
19 Mazaje, ku kaunaci matayenku, kada ku muzguna masu.
I Mænd! elsker eders Hustruer, og værer ikke bitre imod dem!
20 Yaya, ku yi wa iyayen ku biyayya cikin dukan komai, domin wannan yana faranta wa Ubangiji rai.
I Børn! adlyder i alle Ting eders Forældre, thi dette er velbehageligt i Herren.
21 Ku Ubanni, kada ku cakuni 'ya'yanku domin kada su karaya.
I Fædre! opirrer ikke eders Børn, for at de ikke skulle tabe Modet.
22 Bayi, ku yi wa iyayengijinku na jiki biyayya cikin kowane abu, ba tare da bautan ganin ido ba don faranta wa mutane rai, amma da sahihiyar zuciya. Ji tsoron Ubangiji.
I Trælle! adlyder i alle Ting eders Herrer efter Kødet, ikke med Øjentjeneste som de, der ville tækkes Mennesker, men i Hjertets Enfold, frygtende Herren.
23 Duk abin da kuke yi, ku yi aiki daga zuci domin Ubangiji ba domin mutane ba.
Hvad I end foretage eder, så gører det af Hjertet, som for Herren og ikke for Mennesker,
24 Kun san cewa, zaku karbi sakamako na gado daga wurin Ubangiji. Domin Ubangiji Almasihu kuke bauta wa.
da I vide, at I af Herren skulle få Arven til Vederlag; det er den Herre Kristus, I tjene.
25 Domin kowa ya yi rashin adalci zai karbi sakamakon rashin adalcin da ya yi, kuma babu son kai.
Thi den, som gør Uret, skal få igen, hvad Uret han gjorde, og der er ikke Persons Anseelse.

< Kolossiyawa 3 >