< Ayyukan Manzanni 1 >

1 Littafin da na rubuta da farko, Tiyofilos, ya fadi abubuwan da Yesu ya fara yi ya kuma koyar,
My former narrative, Theophilus, dealt with all that Jesus did and taught as a beginning, down to the day on which,
2 har zuwa ranar da aka karbe shi zuwa sama. Wannan kuwa bayan da ya ba da umarni ga zababbun manzanninsa ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
after giving instruction through the Holy Spirit to the Apostles whom He had chosen, He was taken up to Heaven.
3 Bayan ya sha wahala, ya bayyana kan sa da rai a garesu, da alamu da dama masu gamsarwa. Kwana arba'in ya baiyana kansa a garesu yana yi masu magana game da mulkin Allah.
He had also, after He suffered, shown Himself alive to them with many sure proofs, appearing to them at intervals during forty days, and speaking of the Kingdom of God.
4 Yayin da yana zaune tare da su ya basu umarni cewa kada su bar Urushalima, amma su jira alkawarin Uban, wanda ya ce, ''Kun ji daga gare ni,
And while in their company He charged them not to leave Jerusalem, but to wait for the Father's promised gift. "This you have heard of," He said, "from me.
5 cewa Yahaya babu shakka ya yi baftisma da ruwa, amma ku za a yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki nan da kwanaki kadan.''
For John indeed baptized with water, but before many days have passed you shall be baptized with the Holy Spirit."
6 Sa'adda suna tare suka tambaye shi, ''Ubangiji, a wannan lokaci ne za ka maido da mulki ga Isra'ila?”
Once when they were with Him, they asked Him, "Master, is this the time at which you are about to restore the kingdom of Israel?"
7 Ya ce masu, ''Ba naku bane ku san lokaci ko sa'a wanda Uba ya shirya ta wurin ikonsa.
"It is not for you," He replied, "to know times or epochs which the Father has reserved within His own authority;
8 Amma za ku karbi iko, idan Ruhu Mai Tsarki ya zo bisanku, sa'annan za ku zama shaidu na cikin Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, har ya zuwa karshen duniya.”
and yet you will receive power when the Holy Spirit has come upon you, and you will be my witnesses in Jerusalem and in all Judaea and Samaria and to the remotest parts of the earth."
9 Lokacin da Ubangiji Yesu ya fadi wadannan abubuwa, yayin da suna kallon sama, sai aka dauke shi zuwa sama, kuma girgije ya boye shi daga idanunsu.
When He had said this, and while they were looking at Him, He was carried up, and a cloud closing beneath Him hid Him from their sight.
10 Da suka dinga kallon sama yayin da ya tafi, nan da nan, mazaje biyu suka tsaya a gabansu cikin fararen tufafi.
But, while they stood intently gazing into the sky as He went, suddenly there were two men in white garments standing by them,
11 Suka ce, ''Ku mazajen Galili me yasa ku ke tsaye a nan kuna kallon sama? Wannan Yesu wanda ya hau zuwa sama zai dawo kamar yadda kuka gan shi yana tafiya zuwa sama.''
who said, "Galilaeans, why stand looking into the sky? This same Jesus who has been taken up from you into Heaven will come in just the same way as you have seen Him going into Heaven."
12 Da suka dawo Urushalima daga dutsen Zaitun, wanda ke kusa da Urushalima, tafiyar Asabaci daya ne.
Then they returned to Jerusalem from the mountain called the Oliveyard, which is near Jerusalem, about a mile off.
13 Da suka iso, sai suka haye zuwa cikin bene inda suke da zama. Sune su Bitrus, Yahaya, Yakubu, Andarawus, Filibus, Toma, Bartalamawus, Matiyu, Yakubu dan Alfa, Siman mai tsattsauran ra'ayi, kuma da Yahuza dan Yakubu.
They entered the city, and they went up to the upper room which was now their fixed place for meeting. Their names were Peter and John, James and Andrew, Philip and Thomas, Bartholomew and Matthew, James the son of Alphaeus, Simon the Zealot, and Judas the brother of James.
14 Dukansu kuwa suka hada kai gaba daya, yayin da suka ci gaba da naciya cikin addu'a. Tare da su kuma akwai mata, Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma 'yan'uwansa.
All of these with one mind continued earnest in prayer, together with some women, and Mary the mother of Jesus, and His brothers.
15 A cikin wadannan kwanaki Bitrus ya tashi tsaye a tsakiyar 'yan'uwa, kimanin mutane dari da ashirin, ya ce,
It was on one of these days that Peter stood up in the midst of the brethren--the entire number of persons present being about 120--and said,
16 '' 'Yan'uwa, akwai bukatar Nassi ya cika, wanda Ruhu Mai Tsarki ya fada a baya ta bakin Dauda game da Yahuza, wanda ya jagoranci wadanda suka kama Yesu
"Brethren, it was necessary that the Scripture should be fulfilled--the prediction, I mean, which the Holy Spirit uttered by the lips of David, about Judas, who acted as guide to those who arrested Jesus.
17 Domin yana daya daga cikinmu kuma ya karbi rabonsa na ladan wannan hidima,”
For Judas was reckoned as one of our number, and a share in this ministry was allotted to him."
18 (Wannan mutum fa ya sai wa kansa fili da cinikin da ya yi na muguntarsa, kuma a nan ya fado da ka, cikinsa ya fashe, hanjinsa suka zubo waje.
(Now having bought a piece of ground with the money paid for his wickedness he fell there with his face downwards, and, his body bursting open, he became disembowelled.
19 Duka mazaunan Urushalima suka ji wannan, saboda haka suka kira wannan fili da harshensu “Akeldama'' wato, “Filin Jini.”)
This fact became widely known to the people of Jerusalem, so that the place received the name, in their language, of Achel-damach, which means 'The Field of Blood.')
20 “Domin an rubuta a littafin Zabura, 'Bari filinsa ya zama kufai, kada a bar kowa ya zauna wurin,'kuma, 'Bari wani ya dauki matsayinsa na shugabanci.'
"For it is written in the Book of Psalms, "'Let his encampment be desolate: let there be no one to dwell there'; and "'His work let another take up.'
21 Saboda haka ya zama dole, daya daga cikin wadanda suke tare da mu tun lokacin da Ubangiji Yesu yana shiga da fita, a tsakaninmu,
"It is necessary, therefore, that of the men who have been with us all the time that the Lord Jesus went in and out among us--
22 farawa daga baftismar yahaya har zuwa ranar da aka dauke shi daga wurinmu zuwa sama, ya zama daya daga cikin mu wurin shaidar tashinsa.”
beginning from His baptism by John down to the day on which He was taken up again from us into Heaven--one should be appointed to become a witness with us as to His resurrection."
23 Suka gabatar da mutum biyu, Yusufu wanda ake kira Barsabbas, wanda kuma aka yiwa suna Justus, da kuma Matayas.
So two names were proposed, Joseph called Bar-sabbas--and surnamed Justus--and Matthias.
24 Su ka yi addu'a suka ce, ''Ubangiji, kai ka san zuciyar dukan mutane, ka bayyana mana wanda ka zaba cikin su biyun nan
And the brethren prayed, saying, "Thou, Lord, who knowest the hearts of all, show clearly which of these two Thou hast chosen
25 Domin ya dauki gurbin da kuma manzancin daga inda Yahuza ya kauce zuwa nashi waje''
to occupy the place in this ministry and Apostleship from which Judas through transgression fell, in order to go to his own place."
26 suka jefa kuri'a a kansu; zabe ya fada kan Matayas kuma suka lissafta shi tare da manzanni sha dayan.
Then they drew lots between them. The lot fell on Matthias, and a place among the eleven Apostles was voted to him.

< Ayyukan Manzanni 1 >