< Ayyukan Manzanni 1 >

1 Littafin da na rubuta da farko, Tiyofilos, ya fadi abubuwan da Yesu ya fara yi ya kuma koyar,
Den første Bog skrev jeg, o Theofilus! om alt det, som Jesus begyndte baade at gøre og lære,
2 har zuwa ranar da aka karbe shi zuwa sama. Wannan kuwa bayan da ya ba da umarni ga zababbun manzanninsa ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
indtil den Dag, da han blev optagen, efter at han havde givet Apostlene, som han havde udvalgt, Befaling ved den Helligaand;
3 Bayan ya sha wahala, ya bayyana kan sa da rai a garesu, da alamu da dama masu gamsarwa. Kwana arba'in ya baiyana kansa a garesu yana yi masu magana game da mulkin Allah.
for hvem han ogsaa, efter at han havde lidt, fremstillede sig levende ved mange Beviser, idet han viste sig for dem i fyrretyve Dage og talte om de Ting, der høre til Guds Rige.
4 Yayin da yana zaune tare da su ya basu umarni cewa kada su bar Urushalima, amma su jira alkawarin Uban, wanda ya ce, ''Kun ji daga gare ni,
Og medens han var sammen med dem, bød han dem, at de ikke maatte vige fra Jerusalem, men skulde oppebie Faderens Forjættelse, „hvorom,” sagde han, „I have hørt af mig.
5 cewa Yahaya babu shakka ya yi baftisma da ruwa, amma ku za a yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki nan da kwanaki kadan.''
Thi Johannes døbte med Vand; men I skulle døbes med den Helligaand om ikke mange Dage.”
6 Sa'adda suna tare suka tambaye shi, ''Ubangiji, a wannan lokaci ne za ka maido da mulki ga Isra'ila?”
Som de nu vare forsamlede, spurgte de ham og sagde: „Herre! opretter du paa denne Tid Riget igen for Israel?”
7 Ya ce masu, ''Ba naku bane ku san lokaci ko sa'a wanda Uba ya shirya ta wurin ikonsa.
Men han sagde til dem: „Det tilkommer ikke eder at kende Tider eller Timer, hvilke Faderen har fastsat i sin egen Magt.
8 Amma za ku karbi iko, idan Ruhu Mai Tsarki ya zo bisanku, sa'annan za ku zama shaidu na cikin Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, har ya zuwa karshen duniya.”
Men I skulle faa Kraft, naar den Helligaand kommer over eder; og I skulle være mine Vidner baade i Jerusalem og i hele Judæa og Samaria og indtil Jordens Ende.”
9 Lokacin da Ubangiji Yesu ya fadi wadannan abubuwa, yayin da suna kallon sama, sai aka dauke shi zuwa sama, kuma girgije ya boye shi daga idanunsu.
Og da han havde sagt dette, blev han optagen, medens de saa derpaa, og en Sky tog ham bort fra deres Øjne.
10 Da suka dinga kallon sama yayin da ya tafi, nan da nan, mazaje biyu suka tsaya a gabansu cikin fararen tufafi.
Og som de stirrede op imod Himmelen, medens han for bort, se, da stode to Mænd hos dem i hvide Klæder,
11 Suka ce, ''Ku mazajen Galili me yasa ku ke tsaye a nan kuna kallon sama? Wannan Yesu wanda ya hau zuwa sama zai dawo kamar yadda kuka gan shi yana tafiya zuwa sama.''
og de sagde: „I galilæiske Mænd, hvorfor staa I og se op imod Himmelen? Denne Jesus, som er optagen fra eder til Himmelen, skal komme igen paa samme Maade, som I have set ham fare til Himmelen.”
12 Da suka dawo Urushalima daga dutsen Zaitun, wanda ke kusa da Urushalima, tafiyar Asabaci daya ne.
Da vendte de tilbage til Jerusalem fra det Bjerg, som kaldes Oliebjerget og er nær ved Jerusalem, en Sabbatsvej derfra.
13 Da suka iso, sai suka haye zuwa cikin bene inda suke da zama. Sune su Bitrus, Yahaya, Yakubu, Andarawus, Filibus, Toma, Bartalamawus, Matiyu, Yakubu dan Alfa, Siman mai tsattsauran ra'ayi, kuma da Yahuza dan Yakubu.
Og da de kom derind, gik de op paa den Sal, hvor de plejede at opholde sig, Peter og Johannes og Jakob og Andreas, Filip og Thomas, Bartholomæus og Matthæus, Jakob Alfæus's Søn og Simon Zelotes, og Judas, Jakobs Søn.
14 Dukansu kuwa suka hada kai gaba daya, yayin da suka ci gaba da naciya cikin addu'a. Tare da su kuma akwai mata, Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma 'yan'uwansa.
Alle disse vare endrægtigt vedholdende i Bønnen tillige med nogle Kvinder og Maria, Jesu Moder, og med hans Brødre.
15 A cikin wadannan kwanaki Bitrus ya tashi tsaye a tsakiyar 'yan'uwa, kimanin mutane dari da ashirin, ya ce,
Og i disse Dage stod Peter op midt iblandt Brødrene og sagde, (og der var en Skare samlet paa omtrent hundrede og tyve Personer):
16 '' 'Yan'uwa, akwai bukatar Nassi ya cika, wanda Ruhu Mai Tsarki ya fada a baya ta bakin Dauda game da Yahuza, wanda ya jagoranci wadanda suka kama Yesu
„I Mænd, Brødre! det Skriftens Ord burde opfyldes, som den Helligaand forud havde talt ved Davids Mund om Judas, der blev Vejleder for dem, som grebe Jesus;
17 Domin yana daya daga cikinmu kuma ya karbi rabonsa na ladan wannan hidima,”
thi han var regnet iblandt os og havde faaet denne Tjenestes Lod.
18 (Wannan mutum fa ya sai wa kansa fili da cinikin da ya yi na muguntarsa, kuma a nan ya fado da ka, cikinsa ya fashe, hanjinsa suka zubo waje.
Han erhvervede sig nu en Ager for sin Uretfærdigheds Løn, og han styrtede ned og brast itu, og alle hans Indvolde væltede ud,
19 Duka mazaunan Urushalima suka ji wannan, saboda haka suka kira wannan fili da harshensu “Akeldama'' wato, “Filin Jini.”)
hvilket ogsaa er blevet vitterligt for alle dem, som bo i Jerusalem, saa at den Ager kaldes paa deres eget Maal Hakeldama, det er Blodager.
20 “Domin an rubuta a littafin Zabura, 'Bari filinsa ya zama kufai, kada a bar kowa ya zauna wurin,'kuma, 'Bari wani ya dauki matsayinsa na shugabanci.'
Thi der er skrevet i Psalmernes Bog: „Hans Bolig blive øde, og der være ingen, som bor i den,” og: „Lad en anden faa hans Tilsynsgerning.”
21 Saboda haka ya zama dole, daya daga cikin wadanda suke tare da mu tun lokacin da Ubangiji Yesu yana shiga da fita, a tsakaninmu,
Derfor bør en af de Mænd, som vare sammen med os i hele den Tid, da den Herre Jesus gik ind og gik ud hos os,
22 farawa daga baftismar yahaya har zuwa ranar da aka dauke shi daga wurinmu zuwa sama, ya zama daya daga cikin mu wurin shaidar tashinsa.”
lige fra Johannes's Daab indtil den Dag, da han blev optagen fra os, blive Vidne sammen med os om hans Opstandelse.”
23 Suka gabatar da mutum biyu, Yusufu wanda ake kira Barsabbas, wanda kuma aka yiwa suna Justus, da kuma Matayas.
Og de fremstillede to, Josef, som kaldtes Barsabbas med Tilnavn Justus, og Matthias.
24 Su ka yi addu'a suka ce, ''Ubangiji, kai ka san zuciyar dukan mutane, ka bayyana mana wanda ka zaba cikin su biyun nan
Og de bade og sagde: „Du Herre! som kender alles Hjerter, vis os den ene, som du har udvalgt af disse to
25 Domin ya dauki gurbin da kuma manzancin daga inda Yahuza ya kauce zuwa nashi waje''
til at faa denne Tjenestes og Apostelgernings Plads, som Judas forlod for at gaa hen til sit eget Sted.”
26 suka jefa kuri'a a kansu; zabe ya fada kan Matayas kuma suka lissafta shi tare da manzanni sha dayan.
Og de kastede Lod imellem dem, og Loddet faldt paa Matthias, og han blev regnet sammen med de elleve Apostle.

< Ayyukan Manzanni 1 >