< Ayyukan Manzanni 9 >
1 Amma Shawulu, ya cigaba da maganganun tsoratarwa har ma da na kisa ga almajiran Ubangiji, ya tafi wurin babban firist
Men Saulus, som endnu fnøs med Trusel og Mord imod Herrens Disciple, gik til Ypperstepræsten
2 kuma ya roke shi wasiku zuwaga majami'un da ke Dimashku, domin idan ya sami wani da ke na wannan hanya, maza ko mata, ya kawo su Urushalima a daure.
og bad ham om Breve til Damaskus til Synagogerne, for at han, om han fandt nogle, Mænd eller Kvinder, som holdt sig til Vejen, kunde føre dem bundne til Jerusalem.
3 Yayin da yana tafiya, ya kasance da ya iso kusa da Dimashku, nan da nan sai ga wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi;
Men da han var undervejs og nærmede sig til Damaskus, omstrålede et Lys fra Himmelen ham pludseligt.
4 Sai ya fadi a kasa kuma yaji wata murya na ce da shi, ''Shawulu, Shawulu, me yasa kake tsananta mani?''
Og han faldt til Jorden og hørte en Røst, som sagde til ham: "Saul! Saul! hvorfor forfølger du mig?"
5 Shawulu ya amsa, ''Wanene kai, Ubangiji?'' Ubangiji ya ce, ''Nine Yesu wanda kake tsanantawa;
Og han sagde: "Hvem er du, Herre?" Men han svarede: "Jeg er Jesus, som du forfølger.
6 amma ka tashi, ka shiga cikin birnin, kuma za a gaya maka abinda lallai ne kayi.
Men stå op og gå ind i Byen, og det skal siges dig, hvad du bør gøre."
7 Mutanen da ke tafiya tare da Shawulu suka tsaya shiru sun rasa abin fada, suna sauraron muryar, amma ba su ga kowa ba.
Men de Mænd, som rejste med ham, stode målløse, da de vel hørte Røsten, men ikke så nogen.
8 Shawulu ya tashi daga kasa, kuma daga ya bude idanunsa, baya ganin komai; sai suka kama hannuwansa suka yi masa jagora suka kawo shi cikin birnin Dimashku.
Og Saulus rejste sig op fra Jorden; men da han oplod sine Øjne, så han intet. Men de ledte ham ved Hånden og førte ham ind i Damaskus.
9 Har kwana uku ba ya kallo, kuma ba ya ci balle sha.
Og han kunde i tre Dage ikke se, og han hverken spiste eller drak.
10 Akwai wani almajiri a Dimashku mai suna Hananiya; sai Ubangiji ya yi magana da shi cikin wahayi, ya ce, ''Hananiya.'' Sai ya ce, ''Duba, gani nan Ubangiji.''
Men der var en Discipel i Damaskus, ved Navn Ananias, og Herren sagde til ham i et Syn: "Ananias!" Og han sagde: "Se, her er jeg, Herre!"
11 Ubangiji ya ce masa, ''Tashi, ka tafi titin da ake kira Mikakke, kuma a gidan wani mai suna Yahuza ka tambaya mutum daga Tarsus mai suna Shawulu; gama yana addu'a;
Og Herren sagde til ham: "Stå op, gå hen i den Gade, som kaldes den lige, og spørg i Judas's Hus efter en ved Navn Saulus fra Tarsus; thi se, han beder.
12 kuma ya gani cikin wahayi mutum mai suna Hananiya na shigowa kuma ya daura masa hannu, domin idanunsa su bude.''
Og han har i et Syn set en Mand, ved Navn Ananias, komme ind og lægge Hænderne på ham, for at han skulde blive seende."
13 Amma Hananiya ya amsa, ''Ubangiji, na ji labari daga wurin mutane da yawa game da mutumin nan, da irin muguntar da ya aikata ga tsarkakan mutanenka da ke Urushalima.
Men Ananias svarede: "Herre! jeg har hørt af mange om denne Mand, hvor meget ondt han har gjort dine hellige i Jerusalem.
14 An bashi izini daga babban firist domin ya kama dukan wanda ke kira bisa sunanka.''
Og her har han Fuldmagt fra Ypperstepræsterne til at binde alle dem, som påkalde dit Navn."
15 Amma Ubangiji ya ce masa, ''Jeka, gama shi zababben kayan aiki na ne, wanda zai yada sunana ga al'ummai da sarakuna da 'ya'yan Isra'ila;
Men Herren sagde til ham: "Gå; thi denne er mig et udvalgt Redskab til at bære mit Navn frem både for Hedninger og Konger og Israels Børn;
16 Domin zan nuna masa irin wahalar da zai sha sabo da sunana.''
thi jeg vil, vise ham hvor meget han bør lide for mit Navns Skyld."
17 Sai Hananiya ya tafi, ya shiga gidan. Ya dora masa hannu a kai, ya ce, ''Dan'uwa Shawulu, Ubangiji Yesu, wanda ya bayyana a gareka a hanya sa'adda kake zuwa, ya aiko ni domin ka sami ganin gari ka kuma cika da Ruhu Mai Tsarki.''
Men Ananias gik hen og kom ind i Huset og lagde Hænderne på ham og sagde: "Saul, Broder! Herren har sendt mig, den Jesus, der viste sig for dig på Vejen, ad hvilken du kom, for at du skal blive seende igen og fyldes med den Helligånd."
18 Nan take wani abu kamar bawo ya fado daga idanun Shawulu, kuma ya sami ganin gari; ya tashi aka yi masa baftisma;
Og straks faldt der ligesom Skæl fra hans Øjne, og han blev seende, og han stod op og blev døbt.
19 kuma ya ci abinci sai aka karfafa shi. Ya zauna tare da almajirai a Dimashku kwanaki da yawa.
Og han fik Mad og kom til Kræfter. Men han blev nogle Dage hos Disciplene i Damaskus.
20 Nan take ya fara shellar Yesu cikin haikali, yana cewa shine dan Allah.
Og straks prædikede han i Synagogerne om Jesus, at han er Guds Søn.
21 Dukan wadanda suka saurare shi suka yi mamaki suka ce ''Ba wannan mutumin ne yake hallaka mutanen Urushalima da ke kira bisa ga wannan suna ba? Ya kuma zo nan domin ya ba da su a daure ga manyan firistoci.''
Men alle, som hørte det, forbavsedes og sagde: "Er det ikke ham, som i Jerusalem forfulgte dem, der påkaldte dette Navn, og var kommen hertil for at føre dem bundne til Ypperstepræsterne?"
22 Amma Shawulu kuwa ya sami iko sosai, kuma yana haddasa damuwa tare da rinjaya tsakanin Yahudawan dake zama a Dimashku ta wurin tabbatar da Yesu shine Almasihu.
Men Saulus voksede i Kraft og gendrev Jøderne, som boede i Damaskus, idet han beviste, at denne er Kristus.
23 Bayan kwanaki da yawa, sai Yahudawan suka yi shiri domin su kashe shi.
Men da nogle Dage vare forløbne, holdt Jøderne Råd om at slå ham ihjel.
24 Amma shirin su ya zama sananne ga Shawulu. Suna fakkon sa ta wurin tsaron kofar birnin dare da rana domin su kashe shi.
Men Saulus fik deres Efterstræbelser at vide. Og de bevogtede endog Portene både Dag og Nat, for at de kunde slå ham ihjel.
25 Amma da tsakar dare almajiransa suka daukeshi a kwando, suka zurara shi ta katanga.
Men hans Disciple toge ham ved Nattetid og bragte ham ud igennem Muren, idet de firede ham ned i en Kurv.
26 Sa'adda ya zo Urushalima, Shawulu ya yi niyyar hada kai da almajirai, amma dukansu suna tsoronsa, domin ba su yarda cewa shima ya zama almajiri ba.
Men da han kom til Jerusalem, forsøgte han at holde sig til Disciplene; men de frygtede alle for ham, da de ikke troede, at han var en Discipel.
27 Amma Barnaba ya dauke shi ya kawo shi wurin manzannin. Ya kuwa gaya musu yadda Shawulu ya sadu da Ubangiji a hanya, har Ubangiji ya yi magana da shi, kuma yadda Shawulu ya yi wa'azi cikin sunan Yesu gabagadi a Dimashku.
Men Barnabas tog sig af ham og førte ham til Apostlene; og han fortalte dem, hvorledes han havde set Herren på Vejen, og at han havde talt til ham, og hvorledes han i Damaskus havde vidnet frimodigt i Jesu Navn.
28 Ya sadu da su lokacin shigar su da fitar su a Urushalima. Ya yi wa'azi gabagadi cikin sunan Ubangiji Yesu
Og han gik ind og gik ud med dem i Jerusalem
29 kuma yana muhawara da Yahudawan Helenanci; amma sun ci gaba da kokarin kashe shi.
og vidnede frimodigt i Herrens Navn. Og han talte og tvistedes med Hellenisterne; men de toge sig for at slå ham ihjel.
30 Da 'yan'uwa suka gane haka, sai suka kawo shi Kaisariya, suka kuwa tura shi zuwa Tarsus.
Men da Brødrene fik dette at vide, førte de ham ned til Kæsarea og sendte ham videre til Tarsus.
31 Sa'annan iklisiya dake dukan kasar Yahudiya, Galili da kuma Samariya suka sami salama da kuma ginuwa; suka kuwa ci gaba da tafiya cikin tsoron Ubangiji, da kuma ta'aziyar Ruhu Mai Tsarki, iklisiyar kuwa ta karu da yawan mutane.
Så havde da Menigheden Fred over hele Judæa og Galilæa og Samaria, og den opbyggedes og vandrede i Herrens Frygt, og ved den Helligånds Formaning voksede den.
32 Har ta kai, yayin da Bitrus ya zaga dukan yankin kasar, ya dawo wurin masu bi dake zama a garin Lidda.
Men det skete, medens Peter drog omkring alle Vegne, at han også kom ned til de hellige, som boede i Lydda.
33 A can kuwa ya sami wani mutum mai suna Iniyasu, wanda yake shanyayye ne, yana kwance har tsawon shekara takwas a kan gado.
Der fandt han en Mand ved Navn Æneas, som havde ligget otte År til Sengs og var værkbruden.
34 Bitrus ya ce masa, ''Iniyasu, Yesu Almasihu ya warkar da kai. Tashi ka nade shimfidarka.'' Nan take sai ya mike.
Og Peter sagde til ham: "Æneas! Jesus Kristus helbreder dig; stå op, og red selv din Seng!" Og han stod straks op.
35 Sai duk mazauna kasar Lidda da kasar Sarona suka ga mutumin, suka kuma juyo ga Ubangiji.
Og alle Beboere af Lydda og Saron så ham, og de omvendte sig til Herren.
36 Yanzu kuwa a Yafa akwai wata almajira, mai suna Tabita, ma'ana ''Dokas.'' Wannan matar kuwa tana chike da ayyukan nagarta da halin tausayi da take yi ga mabukata.
Men i Joppe var der en Discipelinde ved Navn Tabitha, hvilket udlagt betyder Hind; hun var rig på gode Gerninger og gav mange Almisser.
37 Ya kai ga cewa a kwanakin can ta yi rashin lafiya har ta mutu; da suka wanke gawar ta suka kwantar da ita a bene.
Men det skete i de Dage, at hun blev syg og døde. Da toede de hende og lagde hende i Salen ovenpå.
38 Da shike Lidda na kusa da Yafa, almajiran kuma sun ji cewa Bitrus yana can, suka aika mutane biyu wurinsa. Suna rokansa, ''Ka zo garemu ba tare da jinkiri ba.''
Men efterdi Lydda var nær ved Joppe, udsendte Disciplene, da de hørte, at Peter var der, to Mænd til ham og bade ham: "Kom uden Tøven over til os!"
39 Bitrus ya tashi ya tafi da su, da isowar sa, suka kai shi benen. Sai dukan gwamrayen suka tsaya kusa da shi suna kuka, sai suka dauko riguna da sutura da Dokas ta dinka lokacin da take tare da su.
Men Peter stod op og gik med dem. Og da han kom derhen, førte de ham op i Salen ovenpå, og alle Enkerne stode hos ham, græd og viste ham alle de Kjortler og Kapper, som "Hinden" havde forarbejdet, medens hun var hos dem.
40 Bitrus ya fitar da su duka daga cikin dakin, ya durkusa, ya yi addu'a; sai, ya juya wurin gawar, ya ce, ''Tabita, tashi.'' Ta bude idanunta, da ta ga Bitrus ta zauna,
Men Peter bød dem alle at gå ud, og han faldt på Knæ og bad; og han vendte sig til det døde Legeme og sagde: "Tabitha, stå op!" Men hun oplod sine Øjne, og da hun så Peter, satte hun sig op.
41 Bitrus kuwa ya mika hannunsa ya tashe ta; sa'annan ya kira masu bi da gwamrayen, ya mika ta a raye garesu.
Men han gav hende Hånden og rejste hende op, og han kaldte på de hellige og Enkerne og fremstillede hende levende for dem.
42 Wannan al'amari ya zama sananne cikin dukan Yafa, kuma mutane da yawa suka bada gaskiya ga Ubangiji.
Men det blev vitterligt over hele Joppe, og mange troede på Herren.
43 Ya kasance, cewa, Bitrus ya zauna kwanaki da dama a Yafa tare da wani mutum mai suna Saminu, majemi.
Og det skete, at han blev mange Dage i Joppe hos en vis Simon, en Garver.