< Ayyukan Manzanni 8 >

1 Bulus ya amince da mutuwarsa. A wannan rana tsanani mai zafi ya fara tasowa akan Iklisiya da take a Urushalima, sai masu bangaskiya duka suka bazu ko ina a cikin garuruwan Yahudiya da Samariya, sai manzannin kadai aka bari.
Bet Saulam viņa nāve bija ļoti pa prātam; un tanī dienā liela vajāšana cēlās pret to draudzi, kas bija Jeruzālemē. Un visi izklīda pa Jūdu zemes un Samarijas tiesām, tik ne tie apustuļi.
2 Amintattun mutane suka bizne Istifanus suka yi babban makoki game da shi.
Un dievbijīgi vīri Stefanu paglabāja un viņu gauži nožēloja.
3 Amma Shawulu ya yi wa Iklisiya mugunta kwarai, ya dinga shiga gida gida yana jawo mutane maza da mata, kuma yana kulle su cikin kurkuku.
Bet Sauls to draudzi postīja un gāja pa namiem, satverdams gan vīrus, gan sievas, un tos nodeva cietumā.
4 Duk da haka masu bangaskiyar nan da suka warwatsu suka tafi suka dinga yada wa'azin maganar.
Tad nu tie izklīdinātie apkārt staigāja, to vārdu pasludinādami.
5 Filibus ya tafi can Samariya ya yi shelar Almasihu.
Un Filips uz vienu Samarijas pilsētu nogājis, tiem Kristu pasludināja.
6 Da taron mutane suka ji kuma suka ga alamun da Filibus yake yi, sai suka mai da hankali dukansu domin su ji abinda yake fadi.
Un tie ļaudis vienprātīgi klausījās uz to, ko Filips runāja, dzirdēdami un redzēdami tās zīmes, ko viņš darīja;
7 Domin kazaman ruhohi sun fito daga cikin mutane da yawa da suka saurare shi suna kuka da kururuwa; nakasassun mutane dayawa da guragu suka warke.
Jo no daudziem, kam bija nešķīsti gari, tie izgāja, ar stipru balsi brēkdami, un daudzi melmeņu sērdzīgi(paralizēti) un tizli tapa dziedināti.
8 Kuma aka yi farin ciki mai girma a birnin.
Un liela līksmība cēlās tai pilsētā.
9 Amma akwai wani mutum a cikin birnin da ake kira Siman, wanda tun farko shi masafi ne da kuma dan dabo, yana yi wa mutanen Samariya abubuwan ban mamaki, yayin da yake kiran kansa wani mai muhimmanci.
Un kāds vīrs, ar vārdu Sīmanis, tai pilsētā līdz tam bija darbojies ar buršanu un Samarijas ļaudis iztrūcinājis sacīdams, ka esot liels vīrs;
10 Dukan Samariyawa, manya da yara, suna sauraronsa, su kan ce, ''Wannan mutum shine ikon Allahn nan wanda ake kira mai girma.''
Tam visi klausīja, tā mazi kā lieli sacīdami: “Šis ir tas lielais Dieva spēks.”
11 Suna sauraron sa, domin ya dade yana yi masu abubuwan mamaki da tsafe-tsafensa.
Bet tie tāpēc tam klausīja, ka tas jau sen ar burvību tos bija apstulbojis.
12 Amma da suka yi bangaskiya da wa'azin bisharar da Filibus yake yi game da mulkin Allah da sunan Yesu Almasihu, sai aka yi masu Baftisma dukansu maza da mata.
Kad tie nu Filipam ticēja, kas tiem pasludināja to evaņģēliju par Dieva valstību un Jēzus Kristus vārdu, tad tie tapa kristīti, tā vīri kā sievas.
13 Har shima Siman da kansa ya ba da gaskiya. Bayan an yi masa Baftisma ya cigaba da bin Filibus, da ya ga ana nuna alamu da manyan ayyuka, sai ya yi mamaki.
Un Sīmanis pats arīdzan ticēja, un kristīts pastāvīgi turējās pie Filipa, un redzēdams zīmes un lielus brīnumus notiekam, viņš iztrūkās.
14 Da manzannin da ke Urushalima suka ji labarin Samariya ta karbi maganar Allah, sai suka aika masu Bitrus da Yahaya.
Bet tie apustuļi Jeruzālemē dzirdēdami, ka Samarija Dieva vārdu bija pieņēmusi, sūtīja pie tiem Pēteri un Jāni.
15 Da suka iso, suka yi masu addu'a, domin su karbi Ruhu Mai Tsarki.
Šie nonākuši par tiem lūdza Dievu, ka tie dabūtu Svēto Garu.
16 Domin har wannan lokaci, Ruhu Mai Tsarki bai sauko kan kowannensu ba; an dai yi masu baftisma ne kadai cikin sunan Ubangiji Yesu.
Jo tas vēl uz nevienu no tiem nebija nācis, bet tie bija tikai kristīti uz Tā Kunga Jēzus vārdu.
17 Sai Bitrus da Yahaya suka dora masu hannuwansu, sai suka karbi Ruhu Mai Tsarki.
Tad viņi rokas tiem uzlika, un tie dabūja Svēto Garu.
18 Sa'adda Siman yaga ana bayar da Ruhu Mai Tsarki ta wurin dorawar hannuwan manzanni, ya basu kudi.
Bet Sīmanis redzēdams, ka caur apustuļu roku uzlikšanu Svētais Gars top dots, tiem dāvāja naudu,
19 Ya ce, “Ku bani wannan iko, ni ma, don duk wanda na dora wa hannu ya karbi Ruhu Mai Tsarki.''
Sacīdams: “Dodiet man arīdzan to spēku, ka tas, kam es rokas uzlieku, dabū Svēto Garu.”
20 Amma Bitrus yace masa, ''Azurfarka ta lalace tare da kai, saboda kana tunanin za ka malaki baiwar Ubangiji da kudi.
Bet Pēteris uz to sacīja: “Ka tu pazustu ar savu sudrabu, tāpēc ka tu domā Dieva dāvanu par naudu pirkt.
21 Baka da wani rabo a wannan al'amari, domin zuciyarka ba daidai take da Allah ba.
Tev nav daļas nedz mantošanas pie šā vārda, jo tava sirds nav taisna Dieva priekšā.
22 Saboda haka ka tuba daga wannan muguntarka, ka kuma yi addu'a ga Ubangiji, domin mai yiwuwa ya gafarta maka game da manufar zuciyarka.
Tāpēc atgriezies no šā sava ļaunuma un lūdz Dievu, vai šis tavas sirds nodoms tev varētu tapt piedots;
23 Domin na gane kana cikin bacin rai da kuma cikin daurin zunubi.''
Jo es tevi redzu rūgtas žults pilnu un netaisnībā saistītu.”
24 Siman ya amsa ya ce, ''Kayi addu'a ga Ubangiji domina, kada wani daga cikin abubuwan nan da ka fada ya faru da ni.''
Bet Sīmanis atbildēja un sacīja: “Lūdziet jūs par mani To Kungu, lai uz mani nenāk, ko jūs esat runājuši.”
25 Sa'anda Bitrus da Yahaya suka bada shaida kuma suka fadi maganar Ubangiji, sun koma Urushalima; akan hanya, suka yi wa'azin bishara a kauyukan samariyawa da yawa.
Tad nu Tā Kunga vārdu apliecinājuši un runājuši, tie griezās atpakaļ uz Jeruzālemi un pasludināja evanģēliju daudz Samarijas miestos.
26 Yanzu kuwa Mala'ikan Ubangiji ya yi wa Filibus magana cewa, ''Tashi ka tafi ta kudu da hanyar da ta yi kasa daga Urushalima zuwa Gaza'' (wannan hanyar yana cikin hamada.)
Un Tā Kunga eņģelis uz Filipu runāja sacīdams: “Celies un ej uz dienvidu pusi uz to ceļu, kas no Jeruzālemes iet uz Gazu, kur daudz nestaigā.”
27 Ya kuwa tashi ya tafi. Sai ga wani mutum daga Habasha, baba ne mai babban matsayi a karkashin Kandakatu, sarauniyar Habasha. Shine yake mulkin dukan dukiyarta. Ya zo Urushalima domin ya yi ibada.
Un cēlies viņš nogāja. Un redzi, viens Moru vīrs, Kandaces, Moru zemes ķēniņienes, kambarjunkurs un lielskungs, kas bija pār visām viņas mantām, tas bija nācis uz Jeruzālemi, Dievu pielūgt.
28 Yana komawa zaune cikin karussarsa, kuma yana karanta Littafin annabi Ishaya.
Un atpakaļ uz ceļu devies viņš sēdēja savos ratos un lasīja pravieti Jesaju.
29 Ruhun ya ce wa Filibus, ''Ka je kusa da karussar nan.''
Un Tas Gars uz Filipu sacīja: “Ej klāt un turies pie šiem ratiem.”
30 Sai Filibus ya gudu ya same shi, kuma ya ji shi yana karanta littafin annabi Ishaya, sai ya ce, ''Ka fahimci abin da kake karantawa?''
Un piesteidzies Filips dzirdēja viņu lasām pravieti Jesaju un sacīja: “Vai tu arī saproti, ko tu lasi?”
31 Bahabashen ya ce. ''Yaya zan iya, idan ba wani ya bishe ni ba?'' Ya roki Filibus ya shigo cikin karussar ya zauna tare da shi.
Bet tas sacīja: “Kā lai to varu, kad neviens mani nemāca?” Un viņš lūdza Filipu, lai tas uzkāptu un pie tā piesēstos.
32 Wannan kuwa shine nassin da Bahabashen yake karantawa, ''An kai shi kamar tunkiya zuwa mayanka; shiru kuma, kamar dan rago a hannun masu sosayarsa, bai bude baki ba.
Un tas rakstu gabals, ko tas lasīja, bija šis: “Viņš ir tā kā avs pie kaušanas vests un itin kā jērs apklusis sava cirpēja priekšā, tāpat Viņš savu muti neatdara.
33 Cikin kaskancinsa aka yi masa shari'a da rashin adalci: Wa zai bada tarihin tsararsa? Domin an dauke ransa daga duniya.''
Iekš Viņa pazemošanās Viņa sodība ir atņemta; kas izteiks Viņa dzimumu? Jo Viņa dzīvība top aizrauta no zemes.”
34 Sai baban ya tambayi Filibus, ya ce, ''Na roke ka, gaya mani, game da wa annabin yake magana? Da kansa, ko kuwa wani mutum dabam?''
Un tas kambarjunkurs atbildēja un uz Filipu sacīja: “Es tevi lūdzu, par ko tas pravietis to saka? Vai par sevi pašu, jeb vai par citu kādu?”
35 Filibus ya fara magana; akan littafin Ishaya, ya kuwa yi masa wa'azi akan Yesu.
Un Filips savu muti atdarīja un no šī raksta iesākdams viņam pasludināja to evaņģēliju no Jēzus.
36 Yayin da suke tafiya akan hanya, sai suka iso bakin wani kogi; Baban ya ce, “Duba, ga ruwa anan; me zai hana ayi mani baftisma?”
Un to ceļu braukdami tie nāca pie kāda ūdens, un tas kambarjunkurs sacīja: “Redz, še ūdens! Kas stāv pretī, ka topu kristīts?”
37 Filibus ya ce,” Idan ka gaskanta da zuciya daya, ana iya yi maka baftisma.” Sai Bahabashen ya ce, “Na gaskata Yesu Almasihu shine Dan Allah.”
Bet Filips sacīja: “Ja tu no visas sirds tici, tad to var.” Un viņš atbildēja un sacīja: “Es ticu, ka Jēzus Kristus ir Dieva Dēls.”
38 Sai Bahabashen ya umarta a tsai da karussar. Sai suka zo wurin ruwa dukan su biyu, Filibus da baban, Filibus kuwa yayi masa baftisma.
Un viņš pavēlēja, tos ratus pieturēt, un abi divi nokāpa ūdenī, tā Filips kā tas kambarjunkurs, un viņš to kristīja.
39 Yayin da suka fito daga cikin ruwan, Ruhun Ubangiji ya dauke Filibus; baban bai sake ganin shi ba, sai ya ci gaba da tafiyar sa yana murna.
Un kad tie no ūdens bija izkāpuši, Dieva Gars Filipu aizrāva, un tas kambarjunkurs viņu vairs neredzēja; bet viņš līksms brauca savu ceļu.
40 Amma Filibus ya bayyana a Azotus. Ya ratsa wannan yankin yana wa'azin bishara a dukan garuruwan, har sa'anda ya iso Kaisariya.
Bet Filips atradās Ašdodā; un visas pilsētas pārstaigādams, viņš evaņģēliju sludināja, kamēr nāca uz Cezareju.

< Ayyukan Manzanni 8 >