< Ayyukan Manzanni 8 >

1 Bulus ya amince da mutuwarsa. A wannan rana tsanani mai zafi ya fara tasowa akan Iklisiya da take a Urushalima, sai masu bangaskiya duka suka bazu ko ina a cikin garuruwan Yahudiya da Samariya, sai manzannin kadai aka bari.
Or, en ce jour-là, il y eut une grande persécution contre l'Église de Jérusalem; et tous, excepté les apôtres, furent dispersés dans les contrées de la Judée et de la Samarie.
2 Amintattun mutane suka bizne Istifanus suka yi babban makoki game da shi.
Et des hommes pieux ensevelirent Étienne, et firent de grandes lamentations sur lui.
3 Amma Shawulu ya yi wa Iklisiya mugunta kwarai, ya dinga shiga gida gida yana jawo mutane maza da mata, kuma yana kulle su cikin kurkuku.
Et Saul ravageait l'Église, entrant dans les maisons; et traînant de force les hommes et les femmes, il les jetait en prison.
4 Duk da haka masu bangaskiyar nan da suka warwatsu suka tafi suka dinga yada wa'azin maganar.
Ceux donc qui avaient été dispersés, allaient de lieu en lieu, annonçant la bonne nouvelle de la Parole.
5 Filibus ya tafi can Samariya ya yi shelar Almasihu.
Or, Philippe étant descendu dans une ville de la Samarie, y prêcha Christ.
6 Da taron mutane suka ji kuma suka ga alamun da Filibus yake yi, sai suka mai da hankali dukansu domin su ji abinda yake fadi.
Et le peuple était attentif, d'un commun accord, à ce que Philippe disait, en apprenant, et en voyant les miracles qu'il faisait.
7 Domin kazaman ruhohi sun fito daga cikin mutane da yawa da suka saurare shi suna kuka da kururuwa; nakasassun mutane dayawa da guragu suka warke.
Car les esprits immondes sortaient, en jetant de grands cris, de beaucoup de gens qui en étaient possédés; et beaucoup de paralytiques et d'impotents furent guéris.
8 Kuma aka yi farin ciki mai girma a birnin.
Ce qui causa une grande joie dans cette ville.
9 Amma akwai wani mutum a cikin birnin da ake kira Siman, wanda tun farko shi masafi ne da kuma dan dabo, yana yi wa mutanen Samariya abubuwan ban mamaki, yayin da yake kiran kansa wani mai muhimmanci.
Or, il y avait auparavant, dans la ville, un homme nommé Simon, qui exerçait la magie et étonnait le peuple de la Samarie, se faisant passer pour un grand personnage.
10 Dukan Samariyawa, manya da yara, suna sauraronsa, su kan ce, ''Wannan mutum shine ikon Allahn nan wanda ake kira mai girma.''
Tous lui étaient attachés, depuis le plus petit jusqu'au plus grand; et ils disaient: Celui-ci est la grande puissance de Dieu.
11 Suna sauraron sa, domin ya dade yana yi masu abubuwan mamaki da tsafe-tsafensa.
Et ils étaient attachés à lui, parce que depuis longtemps il les étonnait par ses opérations magiques.
12 Amma da suka yi bangaskiya da wa'azin bisharar da Filibus yake yi game da mulkin Allah da sunan Yesu Almasihu, sai aka yi masu Baftisma dukansu maza da mata.
Mais, quand ils eurent cru à Philippe, qui leur annonçait la bonne nouvelle de ce qui concerne le royaume de Dieu et le nom de Jésus-Christ, ils furent baptisés, tant les hommes que les femmes.
13 Har shima Siman da kansa ya ba da gaskiya. Bayan an yi masa Baftisma ya cigaba da bin Filibus, da ya ga ana nuna alamu da manyan ayyuka, sai ya yi mamaki.
Et Simon lui-même crut aussi, et ayant été baptisé, il ne quittait point Philippe; et voyant les prodiges et les grands miracles qui se faisaient, il était étonné.
14 Da manzannin da ke Urushalima suka ji labarin Samariya ta karbi maganar Allah, sai suka aika masu Bitrus da Yahaya.
Cependant, les apôtres qui étaient à Jérusalem, ayant appris que la Samarie avait reçu la parole de Dieu, y envoyèrent Pierre et Jean,
15 Da suka iso, suka yi masu addu'a, domin su karbi Ruhu Mai Tsarki.
Qui étant descendus, prièrent pour eux, afin qu'ils reçussent le Saint-Esprit.
16 Domin har wannan lokaci, Ruhu Mai Tsarki bai sauko kan kowannensu ba; an dai yi masu baftisma ne kadai cikin sunan Ubangiji Yesu.
Car il n'était encore descendu sur aucun d'eux; mais ils avaient été seulement baptisés au nom du Seigneur Jésus.
17 Sai Bitrus da Yahaya suka dora masu hannuwansu, sai suka karbi Ruhu Mai Tsarki.
Alors les apôtres leur imposèrent les mains, et ils reçurent le Saint-Esprit.
18 Sa'adda Siman yaga ana bayar da Ruhu Mai Tsarki ta wurin dorawar hannuwan manzanni, ya basu kudi.
Mais Simon voyant que le Saint-Esprit était donné par l'imposition des mains des apôtres, leur offrit de l'argent, en disant:
19 Ya ce, “Ku bani wannan iko, ni ma, don duk wanda na dora wa hannu ya karbi Ruhu Mai Tsarki.''
Donnez-moi aussi ce pouvoir, afin que tous ceux à qui j'imposerai les mains reçoivent le Saint-Esprit.
20 Amma Bitrus yace masa, ''Azurfarka ta lalace tare da kai, saboda kana tunanin za ka malaki baiwar Ubangiji da kudi.
Mais Pierre lui dit: Que ton argent périsse avec toi, puisque tu as cru que le don de Dieu s'acquérait avec de l'argent.
21 Baka da wani rabo a wannan al'amari, domin zuciyarka ba daidai take da Allah ba.
Il n'y a pour toi ni part, ni lot en cette affaire; car ton cœur n'est pas droit devant Dieu.
22 Saboda haka ka tuba daga wannan muguntarka, ka kuma yi addu'a ga Ubangiji, domin mai yiwuwa ya gafarta maka game da manufar zuciyarka.
Repens-toi donc de ta méchanceté, et prie Dieu, que, s'il est possible, la pensée de ton cour te soit pardonnée.
23 Domin na gane kana cikin bacin rai da kuma cikin daurin zunubi.''
Car je vois que tu es dans un fiel amer et dans les liens de l'iniquité.
24 Siman ya amsa ya ce, ''Kayi addu'a ga Ubangiji domina, kada wani daga cikin abubuwan nan da ka fada ya faru da ni.''
Mais Simon répondit et dit: Priez vous-mêmes le Seigneur pour moi, afin qu'il ne m'arrive rien de ce que vous avez dit.
25 Sa'anda Bitrus da Yahaya suka bada shaida kuma suka fadi maganar Ubangiji, sun koma Urushalima; akan hanya, suka yi wa'azin bishara a kauyukan samariyawa da yawa.
Ayant donc rendu témoignage à la parole du Seigneur, et l'ayant annoncée, ils retournèrent à Jérusalem, et prêchèrent l'Évangile en plusieurs villages des Samaritains.
26 Yanzu kuwa Mala'ikan Ubangiji ya yi wa Filibus magana cewa, ''Tashi ka tafi ta kudu da hanyar da ta yi kasa daga Urushalima zuwa Gaza'' (wannan hanyar yana cikin hamada.)
Or un ange du Seigneur parla à Philippe, et lui dit: Lève-toi, et va vers le midi, sur le chemin désert qui descend de Jérusalem à Gaza.
27 Ya kuwa tashi ya tafi. Sai ga wani mutum daga Habasha, baba ne mai babban matsayi a karkashin Kandakatu, sarauniyar Habasha. Shine yake mulkin dukan dukiyarta. Ya zo Urushalima domin ya yi ibada.
S'étant levé, il partit. Or voici, un Éthiopien, eunuque, grand ministre de Candace, reine d'Éthiopie, surintendant de tous ses trésors, venu à Jérusalem pour adorer,
28 Yana komawa zaune cikin karussarsa, kuma yana karanta Littafin annabi Ishaya.
S'en retournait, et assis sur son chariot, lisait le prophète Ésaïe.
29 Ruhun ya ce wa Filibus, ''Ka je kusa da karussar nan.''
Alors l'Esprit dit à Philippe: Approche-toi, et rejoins ce chariot.
30 Sai Filibus ya gudu ya same shi, kuma ya ji shi yana karanta littafin annabi Ishaya, sai ya ce, ''Ka fahimci abin da kake karantawa?''
Et Philippe, étant accouru, entendit qu'il lisait le prophète Ésaïe; et il lui dit: Comprends-tu bien ce que tu lis?
31 Bahabashen ya ce. ''Yaya zan iya, idan ba wani ya bishe ni ba?'' Ya roki Filibus ya shigo cikin karussar ya zauna tare da shi.
Il lui répondit: Comment le pourrais-je, si quelqu'un ne me guide? Et il pria Philippe de monter, et de s'asseoir auprès de lui.
32 Wannan kuwa shine nassin da Bahabashen yake karantawa, ''An kai shi kamar tunkiya zuwa mayanka; shiru kuma, kamar dan rago a hannun masu sosayarsa, bai bude baki ba.
Or, le passage de l'Écriture qu'il lisait, était celui-ci: Il a été mené à la tuerie comme une brebis; et comme un agneau, muet devant celui qui le tond, il n'a pas ouvert la bouche.
33 Cikin kaskancinsa aka yi masa shari'a da rashin adalci: Wa zai bada tarihin tsararsa? Domin an dauke ransa daga duniya.''
Sa condamnation a été levée dans son abaissement. Mais qui pourra compter sa durée? Car sa vie a été retranchée de la terre.
34 Sai baban ya tambayi Filibus, ya ce, ''Na roke ka, gaya mani, game da wa annabin yake magana? Da kansa, ko kuwa wani mutum dabam?''
Et l'eunuque prenant la parole dit à Philippe: Je te prie, de qui le prophète dit-il cela? Est-ce de lui-même ou de quelque autre?
35 Filibus ya fara magana; akan littafin Ishaya, ya kuwa yi masa wa'azi akan Yesu.
Philippe prenant la parole et commençant par cet endroit de l'Écriture, lui annonça l'Évangile de Jésus.
36 Yayin da suke tafiya akan hanya, sai suka iso bakin wani kogi; Baban ya ce, “Duba, ga ruwa anan; me zai hana ayi mani baftisma?”
Et comme ils continuaient leur chemin, ils rencontrèrent de l'eau; et l'eunuque dit: Voici de l'eau, qu'est-ce qui m'empêche d'être baptisé?
37 Filibus ya ce,” Idan ka gaskanta da zuciya daya, ana iya yi maka baftisma.” Sai Bahabashen ya ce, “Na gaskata Yesu Almasihu shine Dan Allah.”
Et Philippe lui dit: Si tu crois de tout ton cour, cela t'est permis. Et l'eunuque répondant, dit: Je crois que Jésus-Christ est le Fils de Dieu.
38 Sai Bahabashen ya umarta a tsai da karussar. Sai suka zo wurin ruwa dukan su biyu, Filibus da baban, Filibus kuwa yayi masa baftisma.
Et il commanda qu'on arrêtât le chariot; et ils descendirent tous deux dans l'eau, Philippe et l'eunuque; et Philippe le baptisa.
39 Yayin da suka fito daga cikin ruwan, Ruhun Ubangiji ya dauke Filibus; baban bai sake ganin shi ba, sai ya ci gaba da tafiyar sa yana murna.
Mais quand ils furent ressortis de l'eau, l'Esprit du Seigneur enleva Philippe, et l'eunuque ne le vit plus; car il continua son chemin plein de joie,
40 Amma Filibus ya bayyana a Azotus. Ya ratsa wannan yankin yana wa'azin bishara a dukan garuruwan, har sa'anda ya iso Kaisariya.
Et Philippe se trouva dans Azot; et il évangélisait par toutes les villes où il passait, jusqu'à ce qu'il vînt à Césarée.

< Ayyukan Manzanni 8 >