< Ayyukan Manzanni 8 >
1 Bulus ya amince da mutuwarsa. A wannan rana tsanani mai zafi ya fara tasowa akan Iklisiya da take a Urushalima, sai masu bangaskiya duka suka bazu ko ina a cikin garuruwan Yahudiya da Samariya, sai manzannin kadai aka bari.
Men Saulus fandt Behag i hans Mord. Og paa den Dag udbrød der en stor Forfølgelse imod Menigheden i Jerusalem, og de adspredtes alle over Judæas og Samarias Egne, undtagen Apostlene.
2 Amintattun mutane suka bizne Istifanus suka yi babban makoki game da shi.
Men gudfrygtige Mænd begravede Stefanus og holdt en stor Veklage over ham.
3 Amma Shawulu ya yi wa Iklisiya mugunta kwarai, ya dinga shiga gida gida yana jawo mutane maza da mata, kuma yana kulle su cikin kurkuku.
Men Saulus plagede Menigheden og gik ind i Husene og trak baade Mænd og Kvinder frem og lod dem sætte i Fængsel.
4 Duk da haka masu bangaskiyar nan da suka warwatsu suka tafi suka dinga yada wa'azin maganar.
Imidlertid gik de, som bleve adspredte, omkring og forkyndte Evangeliets Ord.
5 Filibus ya tafi can Samariya ya yi shelar Almasihu.
Da kom Filip til Byen Samaria og prædikede Kristus for dem.
6 Da taron mutane suka ji kuma suka ga alamun da Filibus yake yi, sai suka mai da hankali dukansu domin su ji abinda yake fadi.
Og Skarerne gave endrægtigt Agt paa det, som blev sagt af Filip, idet de hørte og saa de Tegn, som han gjorde.
7 Domin kazaman ruhohi sun fito daga cikin mutane da yawa da suka saurare shi suna kuka da kururuwa; nakasassun mutane dayawa da guragu suka warke.
Thi der var mange, som havde urene Aander, og af hvem disse fore ud, raabende med høj Røst; og mange værkbrudne og lamme bleve helbredede.
8 Kuma aka yi farin ciki mai girma a birnin.
Og der blev en stor Glæde i denne By.
9 Amma akwai wani mutum a cikin birnin da ake kira Siman, wanda tun farko shi masafi ne da kuma dan dabo, yana yi wa mutanen Samariya abubuwan ban mamaki, yayin da yake kiran kansa wani mai muhimmanci.
Men en Mand, ved Navn Simon, var i Forvejen i Byen og drev Trolddom og satte Samarias Folk i Forbavselse, idet han udgav sig selv for at være noget stort.
10 Dukan Samariyawa, manya da yara, suna sauraronsa, su kan ce, ''Wannan mutum shine ikon Allahn nan wanda ake kira mai girma.''
Paa ham gave alle Agt, smaa og store, og sagde: „Det er ham, som man kalder Guds store Kraft.”
11 Suna sauraron sa, domin ya dade yana yi masu abubuwan mamaki da tsafe-tsafensa.
Men de gave Agt paa ham, fordi han i lang Tid havde sat dem i Forbavselse ved sine Trolddomskunster.
12 Amma da suka yi bangaskiya da wa'azin bisharar da Filibus yake yi game da mulkin Allah da sunan Yesu Almasihu, sai aka yi masu Baftisma dukansu maza da mata.
Men da de troede Filip, som forkyndte Evangeliet om Guds Rige og Jesu Kristi Navn, lode de sig døbe, baade Mænd og Kvinder.
13 Har shima Siman da kansa ya ba da gaskiya. Bayan an yi masa Baftisma ya cigaba da bin Filibus, da ya ga ana nuna alamu da manyan ayyuka, sai ya yi mamaki.
Men Simon troede ogsaa selv, og efter at være døbt holdt han sig nær til Filip; og da han saa Tegn og store kraftige Gerninger ske, forbavsedes han højligt.
14 Da manzannin da ke Urushalima suka ji labarin Samariya ta karbi maganar Allah, sai suka aika masu Bitrus da Yahaya.
Men da Apostlene i Jerusalem hørte, at Samaria havde taget imod Guds Ord, sendte de Peter og Johannes til dem,
15 Da suka iso, suka yi masu addu'a, domin su karbi Ruhu Mai Tsarki.
og da disse vare komne derned, bade de for dem om, at de maatte faa den Helligaand;
16 Domin har wannan lokaci, Ruhu Mai Tsarki bai sauko kan kowannensu ba; an dai yi masu baftisma ne kadai cikin sunan Ubangiji Yesu.
thi den var endnu ikke falden paa nogen af dem, men de vare blot døbte til den Herres Jesu Navn.
17 Sai Bitrus da Yahaya suka dora masu hannuwansu, sai suka karbi Ruhu Mai Tsarki.
Da lagde de Hænderne paa dem, og de fik den Helligaand.
18 Sa'adda Siman yaga ana bayar da Ruhu Mai Tsarki ta wurin dorawar hannuwan manzanni, ya basu kudi.
Men da Simon saa, at den Helligaand blev given ved Apostlenes Haandspaalæggelse, bragte han dem Penge og sagde:
19 Ya ce, “Ku bani wannan iko, ni ma, don duk wanda na dora wa hannu ya karbi Ruhu Mai Tsarki.''
„Giver ogsaa mig denne Magt, at, hvem jeg lægger Hænderne paa, han maa faa den Helligaand.”
20 Amma Bitrus yace masa, ''Azurfarka ta lalace tare da kai, saboda kana tunanin za ka malaki baiwar Ubangiji da kudi.
Men Peter sagde til ham: „Gid dit Sølv maa gaa til Grunde tillige med dig, fordi du mente at kunne erhverve Guds Gave for Penge.
21 Baka da wani rabo a wannan al'amari, domin zuciyarka ba daidai take da Allah ba.
Du har ikke Del eller Lod i dette Ord; thi dit Hjerte er ikke ret for Gud.
22 Saboda haka ka tuba daga wannan muguntarka, ka kuma yi addu'a ga Ubangiji, domin mai yiwuwa ya gafarta maka game da manufar zuciyarka.
Omvend dig derfor fra denne din Ondskab og bed Herren, om dog dit Hjertes Paafund maatte forlades dig.
23 Domin na gane kana cikin bacin rai da kuma cikin daurin zunubi.''
Thi jeg ser, at du er stedt i Bitterheds Galde og Uretfærdigheds Lænke.”
24 Siman ya amsa ya ce, ''Kayi addu'a ga Ubangiji domina, kada wani daga cikin abubuwan nan da ka fada ya faru da ni.''
Men Simon svarede og sagde: „Beder I for mig til Herren, for at intet af det, som I have sagt, skal komme over mig.”
25 Sa'anda Bitrus da Yahaya suka bada shaida kuma suka fadi maganar Ubangiji, sun koma Urushalima; akan hanya, suka yi wa'azin bishara a kauyukan samariyawa da yawa.
Men da de havde vidnet og talt Herrens Ord, vendte de tilbage til Jerusalem, og de forkyndte Evangeliet i mange af Samaritanernes Landsbyer.
26 Yanzu kuwa Mala'ikan Ubangiji ya yi wa Filibus magana cewa, ''Tashi ka tafi ta kudu da hanyar da ta yi kasa daga Urushalima zuwa Gaza'' (wannan hanyar yana cikin hamada.)
Men en Herrens Engel talte til Filip og sagde: „Staa op og gaa mod Syd paa den Vej, som gaar ned fra Jerusalem til Gaza; den er øde.”
27 Ya kuwa tashi ya tafi. Sai ga wani mutum daga Habasha, baba ne mai babban matsayi a karkashin Kandakatu, sarauniyar Habasha. Shine yake mulkin dukan dukiyarta. Ya zo Urushalima domin ya yi ibada.
Og han stod op og gik. Og se, der var en Æthioper, en Hofmand, en mægtig Mand hos Kandake, Æthiopernes Dronning, som var sat over alle hendes Skatte; han var kommen til Jerusalem for at tilbede.
28 Yana komawa zaune cikin karussarsa, kuma yana karanta Littafin annabi Ishaya.
Og han var paa Hjemvejen og sad paa sin Vogn og læste Profeten Esajas.
29 Ruhun ya ce wa Filibus, ''Ka je kusa da karussar nan.''
Men Aanden sagde til Filip: „Gaa hen og hold dig til denne Vogn!”
30 Sai Filibus ya gudu ya same shi, kuma ya ji shi yana karanta littafin annabi Ishaya, sai ya ce, ''Ka fahimci abin da kake karantawa?''
Og Filip løb derhen og hørte ham læse Profeten Esajas; og han sagde: „Forstaar du ogsaa det, som du læser?”
31 Bahabashen ya ce. ''Yaya zan iya, idan ba wani ya bishe ni ba?'' Ya roki Filibus ya shigo cikin karussar ya zauna tare da shi.
Men han sagde: „Hvorledes skulde jeg kunne det, uden nogen vejleder mig?” Og han bad Filip stige op og sætte sig hos ham.
32 Wannan kuwa shine nassin da Bahabashen yake karantawa, ''An kai shi kamar tunkiya zuwa mayanka; shiru kuma, kamar dan rago a hannun masu sosayarsa, bai bude baki ba.
Men det Stykke af Skriften, som han læste, var dette: „Som et Faar blev han ført til Slagtning, og som et Lam er stumt imod den, der klipper det, saaledes oplader han ej sin Mund.
33 Cikin kaskancinsa aka yi masa shari'a da rashin adalci: Wa zai bada tarihin tsararsa? Domin an dauke ransa daga duniya.''
I Fornedrelsen blev hans Dom taget bort; hvem kan fortælle om hans Slægt, efterdi hans Liv borttages fra Jorden?”
34 Sai baban ya tambayi Filibus, ya ce, ''Na roke ka, gaya mani, game da wa annabin yake magana? Da kansa, ko kuwa wani mutum dabam?''
Men Hofmanden talte til Filip og sagde: „Jeg beder dig, om hvem siger Profeten dette? om sig selv eller om en anden?”
35 Filibus ya fara magana; akan littafin Ishaya, ya kuwa yi masa wa'azi akan Yesu.
Da oplod Filip sin Mund, og idet han begyndte fra dette Skriftsted, forkyndte han ham Evangeliet om Jesus.
36 Yayin da suke tafiya akan hanya, sai suka iso bakin wani kogi; Baban ya ce, “Duba, ga ruwa anan; me zai hana ayi mani baftisma?”
Men som de droge frem ad Vejen, kom de til noget Vand; og Hofmanden siger: „Se, her er Vand, hvad hindrer mig fra at blive døbt?”
37 Filibus ya ce,” Idan ka gaskanta da zuciya daya, ana iya yi maka baftisma.” Sai Bahabashen ya ce, “Na gaskata Yesu Almasihu shine Dan Allah.”
[Men Filip sagde: „Dersom du tror af hele dit Hjerte, kan det ske.” Men han svarede og sagde: „Jeg tror, at Jesus Kristus er Guds Søn.”]
38 Sai Bahabashen ya umarta a tsai da karussar. Sai suka zo wurin ruwa dukan su biyu, Filibus da baban, Filibus kuwa yayi masa baftisma.
Og han bød, at Vognen skulde holde, og de stege begge ned i Vandet, baade Filip og Hofmanden; og han døbte ham.
39 Yayin da suka fito daga cikin ruwan, Ruhun Ubangiji ya dauke Filibus; baban bai sake ganin shi ba, sai ya ci gaba da tafiyar sa yana murna.
Men da de stege op af Vandet, bortrykkede Herrens Aand Filip, og Hofmanden saa ham ikke mere; thi han drog sin Vej med Glæde.
40 Amma Filibus ya bayyana a Azotus. Ya ratsa wannan yankin yana wa'azin bishara a dukan garuruwan, har sa'anda ya iso Kaisariya.
Men Filip blev funden i Asdod, og han drog omkring og forkyndte Evangeliet i alle Byerne, indtil han kom til Kæsarea.