< Ayyukan Manzanni 6 >

1 A wadannan kwanaki, yawan almajiran ya ci gaba da ribanbanya, sai Yahudawan da suke zama a kasar Helanawa suka fara gunaguni game da Yahudawan Isra'ila, domin basu damu da gwamrayensu, wajen raba abinci da ake yi kullum.
In those days, as the disciples increased in number, a complaint arose against the Hebrews on the part of the Hellenists that their widows were being overlooked in the daily distribution of food.
2 Manzannin nan sha biyu suka kira taron almajiran suka ce masu, ''Bai kamata mu bar maganar Allah mu shiga hidimar rabon abinci ba.
So the twelve called the multitude of the disciples together and said, “It is not proper for us to neglect the word of God to wait on tables.
3 Don haka ku zabi 'yan'uwa maza daga cikinku, mutane bakwai wadanda a ke ganin su da daraja, cike da Ruhu da kuma hikima, wadanda za mu zaba suyi wannan hidima.
Therefore, brothers, look for seven men among you who have a good reputation and are full of the Holy Spirit and wisdom, whom we can appoint for this need.
4 Mu kuwa mu ci gaba da da addu'a da kuma hidimar kalmar.''
But we will devote ourselves to prayer and to the ministry of the word.”
5 Maganar su kuwa ta farantawa dukan jama'a rai sosai. Sai suka zabi Istifanus, shi kuwa mutum ne cike da bangaskiya kuma da Ruhu Mai Tsarki da Filibus, da Birokoros, da Nikanar, da Timan, da Barminas, da kuma Nikolas, mutmin Antakiya wanda ya yi tuban Yahudanci.
This proposal pleased the whole multitude, so they chose Stephen, a man full of faith and the Holy Spirit, together with Philip, Prochorus, Nicanor, Timon, Parmenas, and Nicolaus, an Antiochean convert to Judaism.
6 Masu bin kuwa suka gabatar da wadannan mutanen a gaban manzannin, su kuwa suka yi masu addu'a suka kuma dora hannuwansu a kansu.
They set these men before the apostles, who then prayed and laid their hands on them.
7 Sai maganar Allah ta yawaita; yawan almajiran kuwa ya rubanbanya matuka a Urushalima; firistoci da yawa na Yahudawa suka bada gaskiya.
So the word of God continued to increase, and the number of disciples continued to multiply greatly in Jerusalem, and a large number of priests became obedient to the faith.
8 Sai Istifanus, cike da alheri da iko, ya rika yin ayyukan ban mamaki da alamu a cikin jama'a.
Now Stephen, a man full of faith and power, was performing great wonders and signs among the people.
9 Amma sai ga wadansu mutane daga wata majami'a da ake kira majami'ar Yantattu, wato su Kuramiyawa da Iskandariyawa, da kuma wasu daga kasar Kilikiya da Asiya. Wadannan mutanen kuwa suna muhawara da Istifanus.
But some men from the synagogue of the Freedmen (as it was called), along with some of the Cyrenians and Alexandrians, and some men from Cilicia and Asia, rose up and began to argue with Stephen.
10 Amma suka kasa yin tsayayya da Istifanus, saboda irin hikima da Ruhun da Istifanus ya ke magana da shi.
But they were not able to resist the wisdom and the Spirit with which he was speaking.
11 Sai a asirce suka zuga wasu mutane su je su ce, ''Ai munji Istifanus yana maganganun sabo game da Musa da kuma Allah.''
Then they induced some men to say, “We heard Stephen speaking blasphemous words against Moses and against God.”
12 Sai suka zuga mutanen, har da dattawa da marubuta suka tunkari Istifanus, suka kama shi, suka kawo shi gaban majalisa.
They also stirred up the people, the elders, and the scribes. So they came up to Stephen, seized him, and brought him to the Sanhedrin.
13 Suka kawo masu shaidar karya suka ce, ''Wannan mutumin har yanzu bai dena maganganun gaba akan wannan wuri mai tsarki da kuma shari'a ba.
Then they put forward false witnesses who said, “This man does not stop speaking blasphemous words against the holy place and against the law.
14 Domin kuwa mun ji shi, yana cewa wannan Yesu Banazarat zai rushe wannan wuri zai kuma canza al'adun da muka gada daga wurin Musa.''
For we heard him saying that this Jesus of Nazareth will destroy this place and change the customs that Moses handed down to us.”
15 Dukan wadanda suke zaune a majalisar suka zuba masa ido, sai suka ga fuskarsa kamar ta mala'ika.
And all who were sitting in the Sanhedrin stared at Stephen intently and saw that his face was like the face of an angel.

< Ayyukan Manzanni 6 >