< Ayyukan Manzanni 6 >
1 A wadannan kwanaki, yawan almajiran ya ci gaba da ribanbanya, sai Yahudawan da suke zama a kasar Helanawa suka fara gunaguni game da Yahudawan Isra'ila, domin basu damu da gwamrayensu, wajen raba abinci da ake yi kullum.
Men da i de Dage Disciplenes Antal forøgedes, begyndte Hellenisterne at knurre imod Hebræerne", fordi deres Enker bleve tilsidesatte ved den daglige Uddeling.
2 Manzannin nan sha biyu suka kira taron almajiran suka ce masu, ''Bai kamata mu bar maganar Allah mu shiga hidimar rabon abinci ba.
Da sammenkaldte de tolv Disciplenes Skare og sagde: "Det huer os ikke at forlade Guds Ord for at tjene ved Bordene.
3 Don haka ku zabi 'yan'uwa maza daga cikinku, mutane bakwai wadanda a ke ganin su da daraja, cike da Ruhu da kuma hikima, wadanda za mu zaba suyi wannan hidima.
Udser derfor, Brødre! iblandt eder syv Mænd, som have godt Vidnesbyrd og ere fulde af Ånd og Visdom; dem ville vi så indsætte til denne Gerning.
4 Mu kuwa mu ci gaba da da addu'a da kuma hidimar kalmar.''
Men vi ville holde trolig ved i Bønnen og Ordets Tjeneste."
5 Maganar su kuwa ta farantawa dukan jama'a rai sosai. Sai suka zabi Istifanus, shi kuwa mutum ne cike da bangaskiya kuma da Ruhu Mai Tsarki da Filibus, da Birokoros, da Nikanar, da Timan, da Barminas, da kuma Nikolas, mutmin Antakiya wanda ya yi tuban Yahudanci.
Og denne Tale behagede hele Mængden; og de udvalgte Stefanus. en Mand fuld af Tro og den Helligånd, og Filip og Prokorus og Nikaiior og Timon og Parmenas og Nikolaus, en Proselyt fra Antiokia;
6 Masu bin kuwa suka gabatar da wadannan mutanen a gaban manzannin, su kuwa suka yi masu addu'a suka kuma dora hannuwansu a kansu.
dem stillede de frem for Apostlene; og disse bade og lagde Hænderne på dem.
7 Sai maganar Allah ta yawaita; yawan almajiran kuwa ya rubanbanya matuka a Urushalima; firistoci da yawa na Yahudawa suka bada gaskiya.
Og Guds Ord havde Fremgang og Disciplenes Tal forøgedes meget i Jerusalem; og en stor Mængde af Præsterne adløde Troen.
8 Sai Istifanus, cike da alheri da iko, ya rika yin ayyukan ban mamaki da alamu a cikin jama'a.
Men Stefanus, fuld af Nåde og Kraft, gjorde Undere og store Tegn iblandt Folket,
9 Amma sai ga wadansu mutane daga wata majami'a da ake kira majami'ar Yantattu, wato su Kuramiyawa da Iskandariyawa, da kuma wasu daga kasar Kilikiya da Asiya. Wadannan mutanen kuwa suna muhawara da Istifanus.
Da stod der nogle frem af den Synagoge, som kaldes de frigivnes og Kyrenæernes og Aleksandrinernes, og nogle af dem fra Kilikien og Asien, og de tvistedes med Stefanus.
10 Amma suka kasa yin tsayayya da Istifanus, saboda irin hikima da Ruhun da Istifanus ya ke magana da shi.
Og de kunde ikke modstå den Visdom og den Ånd, som han talte af.
11 Sai a asirce suka zuga wasu mutane su je su ce, ''Ai munji Istifanus yana maganganun sabo game da Musa da kuma Allah.''
Da fik de hemmeligt nogle Mænd til at sige: "Vi have hørt ham tale bespottelige Ord imod Moses og imod Gud."
12 Sai suka zuga mutanen, har da dattawa da marubuta suka tunkari Istifanus, suka kama shi, suka kawo shi gaban majalisa.
Og de ophidsede Folket og de Ældste og de skriftkloge, og de overfaldt ham og slæbte ham med sig og førte ham for Rådet;
13 Suka kawo masu shaidar karya suka ce, ''Wannan mutumin har yanzu bai dena maganganun gaba akan wannan wuri mai tsarki da kuma shari'a ba.
og de fremstillede falske Vidner, som sagde: "Dette Menneske holder ikke op med at tale Ord imod dette hellige Sted og imod Loven.
14 Domin kuwa mun ji shi, yana cewa wannan Yesu Banazarat zai rushe wannan wuri zai kuma canza al'adun da muka gada daga wurin Musa.''
Thi vi have hørt ham sige, at denne Jesus af Nazareth skal nedbryde dette Sted og forandre de Skikke, som Moses har overgivet os."
15 Dukan wadanda suke zaune a majalisar suka zuba masa ido, sai suka ga fuskarsa kamar ta mala'ika.
Og alle de, som sade i Rådet, stirrede på ham, og de så hans Ansigt som en Engels Ansigt.